1) Bisimillahi majidi,
Taimake ni karimi.
2) Nai nufin waƙe a kaina,
Rayuwata na ga ilmi.
3) Duniya ni ta yi ƙunci,
Wanda
nib ba muƙami.
5) Can cikin zuci da
fayi,
Wai ka ji shi shina balami.
6) Ya Ilahu ka ban
habibi
Wanda zai riƙan da ƙaimi.
7) Mu yi ɗa'a gun ka sarki,
Tsare mu da bin su mami.
8) Na dubi waɗansu nawa,
Ƙila sun sam muƙami.
9) Ko ko dai baƙosani ne,
Aka nuna haɗi da tagumi.
10) Wansu na riƙe fal aboki,
Aka
koma ko kalami.
11) Ƙila ko don ban da naira,
Dole
ko in ƙara ƙaimi-
12) Ga biɗa in kare yawa,
Kar
na zam tamkar ƙazami.
13) Kar ka yo cuta ga
kowa,
Nemi
son Allah a komi.
14) An yi watsi da old
aboki,
Ba tunawa bubu komi.
15) In Ilahu ya ce ka
zamto,
Babu mai iya ɓata komi.
16) Ya Ilahi ka ba ni
baiwa,
In yabon ɗan nan salimi-
17) Wanda shi ab ba
kamarshi,
Wajen bauta haɗa da komi.
18) Duka mai son ka
ka so shi,
Dubi Jalla ka miƙa komi.
19) Ni Samirun nan faƙirun
Gun Ilahu da ad da komi-
20) Nai tunani nar rubuta,
Da
isar yaddar karimi.
Name: Samir Aminu Musa
Email: samiraminumusa95@gmail.com
Phone Number: 08109474995
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.