𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Ina da 'yar'uwa sama da shekara goma tana soyayya da ɗan shi'a, anyi anyi ta rabu dashi taƙi, har ta shiga shi'ar, iyayenta sunƙi aura mata shi, yanzu an samu wasu adangi 'yan bidi'a zasu daura musu aure, shin ya halatta muje bikin?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
الحمد لله.
Idan Allah ya
datar da Mutum ya shiryar da shi da
bin hanyar Ahlussunnah wal-jama'a, to dole ya san abubuwan da zasu raba shi da abin da Ahulussunnah wal-jama'a
suke akai don nesantar su, ya kuma san Abin da 'yan shi'a suke akai na aƙidu
mugwaye da tafarki.
Asalai da 'yan
shi'a suka saɓawa
ahulussunnah akansu suna da yawa daka cikinsu akwai:-.
'yan shi'a
suna ƙudurce
jirkitar alƙur'ani
badai-dai yake ba, suna ƙudurce limamansu basa Saɓo,
sun kafirta sahabbai baki ɗaya
sai 'yan kaɗan da suka
bari ba su kafirta ba, suna girmama Ƙabur-bura, da raya su, suna neman agajin
mamacin dake cikin ƙabari da roƙonsa biyan wata buƙata, a mai-makon Allah,
duk Wannan ya samo asali saboda baƙar ƙiyayya da hassada da suke da ita a kan ahlusunnah
Wal-jama'a, da kafirta su da sukayi, ta yaya zaka Aurar da 'yarka ga wanda
wannan shi ne aƙidarsa, ta yaya kake tunani zai samu nasara arayuwa tare da
tattaruwar wannan tufka da War-wara da yake da ita acikin addini? ta yaya zai
tarbiyanci 'ya'ya?, a kan tauhudi zai rainesu ko a kan shirka da ba ta da
maguzanci? shin kanajin Zai koya musu son sahabbai, ko ƙinsu zai koya musu?, shin
zai koya musu Tsarkakuwar limamansu goma sha biyu, ko zai koyar dasu mantuwa da
kus-kure yana iya faruwa dasu?, da sauran Abubuwa masu yawa na tufka da
War-wara.
Indai Mutum ɗan shi'ane ko an daura masa
Aure da yarinya wannan auren bataccene, bai halatta Mace ta Aureshi ba, domin
waɗannan aƙidun
suna kishiyantar addinin musulunci ne, Allah madaukakin Sarki ya ce a suratul
Baƙara
aya ta 221:
وَلَا تَنْكِحُوا الْمُشْرِكَاتِ حَتَّىٰ يُؤْمِنَّ ۚ وَلَأَمَةٌ مُؤْمِنَةٌ
خَيْرٌ مِنْ مُشْرِكَةٍ وَلَوْ
أَعْجَبَتْكُمْ ۗ وَلَا تُنْكِحُوا
الْمُشْرِكِينَ حَتَّىٰ يُؤْمِنُوا ۚ وَلَعَبْدٌ مُؤْمِنٌ
خَيْرٌ مِنْ مُشْرِكٍ وَلَوْ
أَعْجَبَكُمْ ۗ أُولَٰئِكَ يَدْعُونَ
إِلَى النَّارِ ۖ وَاللَّهُ يَدْعُو
إِلَى الْجَنَّةِ وَالْمَغْفِرَةِ بِإِذْنِهِ ۖ وَيُبَيِّنُ آيَاتِهِ
لِلنَّاسِ لَعَلَّهُمْ يَتَذَكَّرُونَ
FASSARA:
Kuma kada ku auri
mãtã mushirikai sai sun yi ĩmãni: Kuma lalle ne baiwa mũmina ita ce mafi alheri
daga ɗiya kãfira, kuma
kõ da tã bã ku sha'awa. Kuma kada ku aurar wa maza mushirikai sai sun yi ĩmãni,
kuma lalle ne bãwa mũmini shi ne mafi alheri daga ɗa mushiriki, kuma kõ da yã bã ku sha'awa, waɗannan suna kira ne zuwa ga
wuta kuma Allah Yana kira zuwa ga Aljanna da gãfara da izninsa. Kuma Yana
bayyana ãyõyinsa ga mutãne; tsammãninsu suna tunãwa.
An tambayi
Shaikul Islam ibnu taimiyyah a kan shin ya halatta mace ta auri ɗan shi'a ko na miji ya Auri
'yar shi'a?.
Ya Amsa da:
'yan shi'a masoya son zuciyane da bidi'a da ɓata,
bai kamata musulmi ya Aurar da 'yarsa ko wacce yake da walicci akanta ga ɗan shi'a ba.
Idan ita ma
'yar shi'ace, aure yayi, idan ana fatan zata tuba, idan ita macen ce 'yar shi'a
namijin ba ɗan shi'a
ba ne, kuma ba'a tsammanin zata tuba, barin Aurenta shi ne yafi, don kada ta ɓata masa 'ya'yansa.
Maj-mu'u
fatawa (32/61).
Kaga A nan shaikul
islam ya hana auren 'yar shi'a, duk da Aure yana sanya miji yayi tasiri a kan matarsa,
ya halatta auren 'yar shi'a idan ana fatan tuban ta..
idan Mutum
yaga aurenta zaisa ya tsayar da ita a kan hanyar gaskiya.
Amma Idan
Macece Ɗan
shi'a ya nemi Aurenta kai tsaye haramunne a daura musu aure, idan An daura
auren baiyi ba.
Ta kowacce
hali babu wata hujja da uba zai ƙyale wasu tsoffi 'yan bidi'a yanaji yana
gani su aurar wa da ɗan
shi'a 'yarsa, wannan ya nuna shikansa bai san me yake yi ba, ranar ƙiyama
kai uba kai Allah zaiwa tambaya dangane da kiwon 'ya'yanka da Allah ya baka.
ba dai-dai ba
ne iyaye maza sudunga ƙyale Al'amarin auren 'ya'yansu a hannun kakanninsu ko iyayensu
koda kuwa su ba su aminta da aƙida ko halaye na wannan da yake neman
'ya'yansu ba.
Uba shike da
haƙƙin
Aurar da 'yarsa ga mutumin daya aminta da halayyarsa da Addininsa da Aƙidarsa.
Wajibine a kan
Uba ya tashi tsaye yayi bincke mai ƙarfi a kan duk wanda yazo neman Auren
'yarsa.
Idan ya
tabbatar bashi da aƙida ko halayya mai kyau, to shi ne yake da cikakken iko da
hurumin Auren da 'yarsa, in yaga mutum bashi da aƙida mai kyau, to karya sake wasu tsoffi
su yi masa dole, ya tsaya tsayin daka ko sama da Ƙasa zata haɗe
karya Aurar da 'yarsa ga mutumin banza mushiriki.
Yanzu ba
Maganar zuwa Daurin Aure ba, ko an daura ma Auren baiyi ba.
Dolene a kan uban
wannan yarinya ya tsaya yaga 'yarsa ba ta Auri wannan zindiƙin ba,
duk irin rikicin da za ayi saidai ayi 'yarkace kai Allah zai tambaya a kan Amanarta
daya damƙa
ahannunka.
Kada Ku sake
ayi wannan Auren iskanci da fasadi mai yawa dake cikinsa.
WALLAHU
A'ALAM.
Zauren
Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah, ta fahimtar magabatan ƙwarai.
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.