Ticker

6/recent/ticker-posts

Ya Halatta Na Bawa Kirista Naman Layya?

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Salamun alaikum, Malam zan iya bawa makocina kirista naman layya ?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikum assalam. Ya halatta a ba wa kafiri naman layya, mutukar babu yaki tsakaninsa da Musulmai, Allah Yana cewa a suratul Mumtahanah aya ta (8): "Allah Ba Ya hanaku kyautatawa kafiran da ba su yake ku ba, ba su Kuma fitar da ku daga gidajanku ba"

Ibnu Khudama Yana cewa: "Layya sadaka ce, don haka ya halatta a bawa kafiri kamar ragowar sadakoki na nafila" Almugni 9/450.

Annabi Yana cewa: "Mala'ika Jibrilu bai gushe yana min wasici da makoci ba, har sai da na zaci zai ce akwai gado tsakanin makoci da makoci".

Allah ne mafi sani

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah, ta fahimtar magabatan ƙwarai.

SHIN YA HALATTA NA BAWA KIRISTA NAMAN LAYYA?

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Salamun alaikum, Malam zan iya bawa makocina kirista naman layya? Ina son in sani cewa ya kamata inbada kyauta naman layya ga christa watau kafiri wanda baya sallah ko bai kamata ba.

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikum assalam. Ya halatta a bawa kafiri naman layya, mutukar babu yaki tsakaninsa da Musulmai, Allah Yana cewa

لَّا يَنْهَاكُمُ اللَّهُ عَنِ الَّذِينَ لَمْ يُقَاتِلُوكُمْ فِي الدِّينِ وَلَمْ يُخْرِجُوكُم مِّن دِيَارِكُمْ أَن تَبَرُّوهُمْ وَتُقْسِطُوا إِلَيْهِمْ ۚ إِنَّ اللَّهَ يُحِبُّ الْمُقْسِطِينَ ۝ إِنَّمَا يَنْهَاكُمُ اللَّهُ عَنِ الَّذِينَ قَاتَلُوكُمْ فِي الدِّينِ وَأَخْرَجُوكُم مِّن دِيَارِكُمْ وَظَاهَرُوا عَلَىٰ إِخْرَاجِكُمْ أَن تَوَلَّوْهُمْ ۚ وَمَن يَتَوَلَّهُمْ فَأُولَٰئِكَ هُمُ الظَّالِمُونَ

Allah bã Ya hana ku, daga waɗanda ba su yãƙe ku ba sabõda addini kuma ba su fitar da ku ba daga gidãjenku, ga ku kyautata musu kuma ku yi musu ãdalci. Lalle Allah Yanã son mãsu ãdalci. ۝ Allah Yanã hana ku kawai daga waɗanda suka yãke ku sabõda addini kuma suka fitar da ku daga gidãjenku, kuma suka taimaki jũna ga fitar da ku, karku jiɓince su, kuma wanda ya jiɓince su, to waɗannan sũ ne azzãlumai. (Suratul Mumtahanah aya ta 8-9)

Shaykh Ibn ‘Uthaymin yace: Ya halarta a bawa kafiri naman hadayah (wato layya) a matsayin sadaqa matuqar ana zaman lafiya da kafirin, baya ɗaya daga cikin wanda suke kashe musulmai. Idan yana cikin masu kashe musulmai, to kada a bashi komai.

Ibnu Khudama Yana cewa : "Layya sadaka ce, don haka ya halatta a bawa kafiri kamar ragowar sadakoki na nafila" Almugni 9/450.

Annabi Sallallahu alaihi Wasallam Yana cewa: "Mala'ika Jibrilu bai gushe yana min wasici da makoci ba, har sai da na zaci zai ce akwai gado tsakanin makoci da makoci".

WALLAHU A'ALAM

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Questions and Answers

Post a Comment

0 Comments