𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Salamun
alaikum, Malam zan iya bawa makocina kirista naman layya ?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikum
assalam. Ya halatta a ba wa kafiri
naman layya, mutukar babu yaki tsakaninsa da Musulmai, Allah Yana cewa a
suratul Mumtahanah aya ta (8): "Allah Ba Ya hanaku kyautatawa kafiran da
ba su yake ku ba, ba su Kuma fitar da ku daga gidajanku ba"
Ibnu Khudama
Yana cewa: "Layya sadaka ce, don haka ya halatta a bawa kafiri kamar
ragowar sadakoki na nafila" Almugni 9/450.
Annabi ﷺ Yana cewa: "Mala'ika
Jibrilu bai gushe yana min wasici da makoci ba, har sai da na zaci zai ce akwai
gado tsakanin makoci da makoci".
Allah ne mafi
sani
DR. JAMILU
YUSUF ZAREWA
Zauren
Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah, ta fahimtar magabatan ƙwarai.
SHIN YA HALATTA NA BAWA KIRISTA NAMAN LAYYA?
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Salamun alaikum, Malam zan iya bawa makocina kirista naman
layya? Ina son in sani cewa ya kamata inbada kyauta naman layya ga christa
watau kafiri wanda baya sallah ko bai kamata ba.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikum assalam. Ya halatta a bawa kafiri naman layya,
mutukar babu yaki tsakaninsa da Musulmai, Allah Yana cewa
لَّا
يَنْهَاكُمُ اللَّهُ عَنِ الَّذِينَ لَمْ يُقَاتِلُوكُمْ فِي الدِّينِ وَلَمْ يُخْرِجُوكُم
مِّن دِيَارِكُمْ أَن تَبَرُّوهُمْ وَتُقْسِطُوا إِلَيْهِمْ ۚ إِنَّ اللَّهَ يُحِبُّ
الْمُقْسِطِينَ إِنَّمَا يَنْهَاكُمُ اللَّهُ عَنِ الَّذِينَ قَاتَلُوكُمْ فِي الدِّينِ
وَأَخْرَجُوكُم مِّن دِيَارِكُمْ وَظَاهَرُوا عَلَىٰ إِخْرَاجِكُمْ أَن تَوَلَّوْهُمْ
ۚ وَمَن يَتَوَلَّهُمْ فَأُولَٰئِكَ هُمُ الظَّالِمُونَ
Allah bã Ya hana ku, daga waɗanda
ba su yãƙe
ku ba sabõda addini
kuma ba su fitar da ku ba daga gidãjenku,
ga ku kyautata musu kuma ku yi musu ãdalci.
Lalle Allah Yanã son mãsu ãdalci. Allah Yanã hana ku kawai daga waɗanda
suka yãke ku sabõda addini kuma suka fitar da ku daga gidãjenku, kuma suka
taimaki jũna ga fitar da ku, karku jiɓince
su, kuma wanda ya jiɓince
su, to waɗannan sũ ne
azzãlumai. (Suratul Mumtahanah aya ta 8-9)
Shaykh Ibn ‘Uthaymin yace: Ya halarta a bawa kafiri naman
hadayah (wato layya) a matsayin sadaqa matuqar ana zaman lafiya da kafirin,
baya ɗaya daga cikin
wanda suke kashe musulmai. Idan yana cikin masu kashe musulmai, to kada a bashi
komai.
Ibnu Khudama Yana cewa : "Layya sadaka ce, don haka ya
halatta a bawa kafiri kamar ragowar sadakoki na nafila" Almugni 9/450.
Annabi Sallallahu alaihi Wasallam Yana cewa: "Mala'ika
Jibrilu bai gushe yana min wasici da makoci ba, har sai da na zaci zai ce akwai
gado tsakanin makoci da makoci".
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.