Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Kaciyar Mata

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum malam ina fata kana cikin koshin lafiya Allah yasa haka amin malam Allah ya azurtani da samun ya mace kasancewar abaya duk ya'yan da nake haifa maza ne kuma ba'a cire musu abun wuya to ita ma mace za ai iya barinta ba tare da ancire mata abun da ake cirewa a gaban su ba? Ina fatan malam zai amsa mini wannan tambaya tawa domin ina fuskanta matsin lamba daga wajan matata amma idan taga abun da kace to zata yarda.

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa'alaikumussalam wa rahmatullahi wa barakatuhu.

Shi yiwa mata kaciya, ya zo a wasu hadisai cewa Manzon Allah ya ce "Yiwa mata kaciya, girmamawa ce".

To amma wasu maluman sun ce kusan dukkan hadisan dake magana a kan kaciyar mata ɗin, dha'ifai ne (wato raunana) babu ingantacce daga cikinsu ko ɗaya. (Kamar yadda Shaikh Sayyid Sabiƙ ya fa'da acikin Fiƙhus Sunnah, babin dake magana a kan kaciya). Sai dai kuma ai ba'a hana yin aiki da rauna nan hadisai ba, musamman acikin abin da ya shafi riskar wata falala, ko wa'azantarwa.

Don haka ma Maluman fiƙhu suka daukeshi amatsayin mustahabbi. Shi kuma kaciyar maza wasu malaman Mazhabin Zahiriyyah sun ce wajibi ne. Amma Imamu Malik da mafiya yawan Malaman Shafi'iyyah sun ce sunnah ne.

A bangaren likitocin Musulunci kuma, wasu daga cikinsu sun ce lallai yiwa mata kaciya ɗin nan yakan sanya hasken fuska da ni'ima garesu kuma yakan rage musu Ƙarfin sha'awa alokacin budurci. Wanda kuma wannan ɗin abu ne mai kyawu saboda yakan taimaka wajen kiyaye mutuncinsu.

Haka nan Ibnu Ƙudamah Almaƙdisiy a cikin littafinsa "Al Mughnee" ya kawo hujjoji a kan sunnancin yin kaciya ga mata, kuma ya dogara da sahihiyar fatawar Imamu Ahmad bn Hanbal a kan haka.

Don haka abin da nake gani shi ne: ka bar su su yi mata kaciyar, amma ka sanya ido sosai a kan lamarin. Ka gaya musu su yi ta sama-sama (kamar yadda Annabi ya ba da shawara ga wata wanzamiya) sannan su yi amfani da sabuwar reza mai tsafta.

Allah ta'ala yasa mudace

Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah, ta fahimtar magabatan ƙwarai.

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/Fb6ƙgYPXfEeHb8CD1SWAkK

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Questions and Answers

Post a Comment

0 Comments