𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Mene ne
hukuncin namijin da bayasan haihuwa saboda tsoran dawainiyar 'ya'ya, mene ne
hukuncin zama dashi, shin matarsa zata iya bijiremar tadau ciki ba tare da
yasani ba?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
الحمد لله الذي أنعمنا
بلإسلام .
Shaik Usaimeen
Rahimahullah ya ce: Abin da ya kamata ga Musulmi shi ne suyawaita nasabarsu
gwar-gwadon yanda suka Samu iko, domin hakan shi ne Umarni da Annabi sallallahu
Alaihi Wasallam ya fuskantar dashi zuwa Al'ummarsa cikin fadinsa (Ku Auri mata
waɗanda kuke ƙauna
masu haihuwa, domin nayi alfahari da yawanku ranar alkiyama, Yawan dangi kuma shi
ne yawan Al'ummah, yawan al'umma kuma shi ne izzarta da kwarjininta, kamar
yanda Allah madaukakin Sarki ya ce: Yana gorantawa Banu Isra'ila:
وَجَعَلْنَاكُمْ أَكْثَرَ نَفِيرًا... {الإسراء،/ ٦ }
Muka sanyaku
Masu yawa cikin mutane.
Annabi Shu'Aibu
Alaihissalamu yacewa mutanensa.
وَاذْكُرُوا إِذْ كُنْتُمْ قَلِيلًا
فَكَثَّرَكُمْ ۖ ... {الأعراف /٨٦}
Kutuna sanda
baku dayawa Allah yayawaitaku
Babu wanda
yake inkarin yawan al'umma shi ne sababin izzarta da karfinta mai-makon yanda
masu mugun zato suke suranta waɗanda
suke ɗaukar cewa yawan
al'umma shi ne dalilin dake kawowa Al'umma talauci da yunwa.
Lallai
Al'Ummah intayi yawa tadogara ga Allah, tayi Imani da Alkawarinsa zai azurtata
komai yawanta kamar yanda yazo cikin fadinsa:
وَمَا مِنْ دَابَّةٍ فِي
الْأَرْضِ إِلَّا عَلَى اللَّهِ رِزْقُهَا... {هود /٦}
Babu wata
halitta face arzikinta yana wajan Allah
Face Allah ya
saukake mata Al'amuranta ya wadatata daka falalarsa.
Dan haka bai
kamata mace tayi amfani da kwayoyin hana ɗaukar
ciki dasunan tsarin iyali ba saida sharudda guda biyu.
1. Nafarko:
Yakasance tana cikin buƙatar hakan dole, kamar ba ta da lafiya bazata iya ɗaukar ciki kowacce shekara
ba, ko mai siririn jikice ko kwan-kwaso, ko tana da wasu ababe dazasu hanata ɗaukar ciki kowacce shekara.
2. Na biyu:
Mijinta yayi mata izinin tasha, domin miji yanada hakkin a kan 'ya'ya da ɗaukar ciki, sannan dolene
sai anshawarci likita a kan waɗannan
kwayoyin, shin shansu yana cutarwa kobaya cutarwa.
Idan sharudda
biyunnan suka cika, Babu laifi amfani da kwayoyin hana ɗaukar ciki, Saidai hana ɗaukar cikin naɗan wani lokaci, bawai na
din-din har abada ba, domin wannan akwai yanke yaduwar al'umma acikinsa.
fatawa
Mar'atul musulimah (2/ 657-658).
Illah da cutar dashan wadannan kwayoyin suke
haifarwa Shaik Usaimeen ya ce: Labari ya iskeni daka bangarori dayawa daka
likitoci damasu bada magani cewa kwayoyin hana ɗaukar
ciki suna cutarwa, tabangarenmu munsan illarsa, domin hana wani abu na dabi'ah
da Allah yahalicci mutum akansa yakuma rubutawa matan 'yan adam babu kokwanto
wannan cutarwane, Allah maɗaukakin
sarki mai hikimane, bahaka kawai yasa jini ke fita daka jijiyoyiba awani lokaci
sananne saida hikima, kasancewar Mukuma muna hana haka da wannan magun-guna
cutane babu shakka.
Labari
yariskeni abun yawuce yanda ake siffanta mana, yanasa lalacewar mahaifa, kuma
yanasa cutukan gabobi, Wannan wajibine anisanceshi.
Tsarin iyalin
da musulunci yayarda dashi shi ne wanda lalura tasa dole mace tadaina haihuwa,
kodai saboda siranta kwan-kwasonta ba ta iya haihuwa dakanta, ko saboda wata
cuta datasa dole tayi tsarin bisa sharudda biyun can da muka ambata.
Amma irin
wanda yahudawa da 'yan bokoko suke tallatawa mutane wai ka ƙayyade
iyalinka daka mace ɗaya
ko 'ya'a uku zuwa biyar wannan haramunne yahudancine wajibine musulmai sutashi
suyaƙi
wannan bala'in.
Babu inda
yahalatta haka kawai saboda yahudanci ma'aurata su dena haihuwa wannan ba
musulunci ba ne.
Insuna so
sudunga samun tazara daka haihuwa zuwa wata haihuwar Saisubi tsarin musulunci
wajan Yaye yaro kada suke yaye yaro sai ya cika shekara biyu kamar yanda alƙur'ani
yabasu shawara.
Sudunga yin
azalu ko mula masa inzasu biya buƙatar sha'awarsu dan kada ciki yashiga
wannan shi ne tsarin iyalin da musulmai zasu iya yi amatsayin tazarar haihuwa,
ba irin wanda makiya Allah yahudawa suke fesa gubarsa cikin al'ummar musulmai
ba, bisa da'awar hakan nakawo talauci da yunwa, Allah yayi mana tsari daka
makircin kafirai yahudawa.
mijinda
bayasan haihuwa saboda tsoran dawainiyar 'ya'ya kibi duk hanyar data kamata
kinuna masa addinin musulunci baiyarda da hakanba, kuma ke yana cutar dake dan
kinasan haihuwa, inkikayi iya ƙoƙarinki yaƙi, ki kabi duk hanyoyin daya kamata babu
wani canji toki nemi yasakeki kawai babu Alkhairi atare da shi wannan mijin.
Bakiyi laifi
ba idan kika nemi yasakeki anan, kinemi kodai yahakura kuci gaba da hayayyafa
koya sakeki danke bazaki iya zama dashi ba.
Kuma aibashi
ne zai azurtasu ba, Allah ne, kinuna masa shi sunawane agidansu ubansa shi kaɗai ko su biyu yahaifa amma
ya akayi yanzu kowa yana rayuwa iya wacce Allah yaƙaddara masa na
arzikinsa!!
Arzikinsu ba'a
hannunsa yakeba aikinsa yayi tarbiyyarsu yadorasu a kan hanya taƙwarai,
shiriyarsu da arzikinsu yana hannun Allah wanda shi ne ya'azurta kafiri da
zindiƙi
dajahilin dan bokon da turawa suka jirkita masa kwakwalwa.
WALLAHU
A'ALAM.
Zauren
Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah, ta fahimtar magabatan ƙwarai.
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.