𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum warahmatullah. Dan Allah malam ina
da tambayoyi ne guda uku duk da cewa ta farkon kusan a haɗe suke. Tambaya ta ita ce matar aure ce
akayi mata fyaɗe
sannan ta cigaba da kwanciyar aure da mijinta. Shin akwai aure a tsakanin su ko
babu? kuma zasu iya cigaba da zaman aurensu akan haka? Sannan zata iya faɗa masa ko Kuma a'a, saboda gudun zargi ?
Na biyu Kuma sai ciki ya bayyana a tare da ita
Kuma sannan ta cigaba da kwanciyar aure da mijinta shin akwai aure a tsakaninsu
ko babu? kuma meye matsayin auren ?
Na uku Kuma shi ne macece a kaima auren dole har
Allah yasa ahalin yanzu suna da yara kusan 8 amma tace har yanzu babu digon
sonsa a ranta wai zata iyayin karya da wata laluran dan ya saketa wai bazata
iya cigaba da rayuwarta dashi ba. Nagode sosai Allah biyaka da mafificin
Alkhairi duniya da lahira amiin ya hayyu ya qayyum.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikis salam wa rahmatullah.
Hukuncin matar da aka yiwa fyaɗe shi ne: dole ne ta sanar da mijinta
saboda hakkinsa na aure. Sannan kuma wajibi ne tayi zaman istibra'i wato domin
tabbatar da ko ciki ya shiga ko bai shiga ba.
Zata zauna tsawon lokacin da za ta yi haila. Idan
hailarta tazo koda sau ɗaya
ne, to shikenan ta samu tabbacin cewar ciki bai shigeta awannan fyaɗen da akayi mata ba. Amma idan har
ciki ya shiga, babu damar mijinta ya kwanta da ita sai bayan ta haife abin da
ke cikinta. Domin Manzon Allah ﷺ ya
hana mutum ya shayar da shukar da ba tasa ba.
Bayan ta haife cikin kuma sai ta cigaba da zaman
aurenta da mijinta. Domin wannan fyaɗen bai lalata aurensu ba.
Amma yanzu tun da har ta cigaba da mu'amalar
auratayya da mijinta, dole wannan abin da ta haifa ɗin ya zamto na mijinta ne. Tun da Manzon
Allah ﷺ yace
"YARO NA SHIMFIDA NE" (wato mamallakin shimfidar shi ne mamallakin
yaron).
Matar da aka yiwa auren dole tana da damar neman
yin khul'i da mijinta. Wato ta biyashi sadakinsa shi kuma ya saketa. Amma neman
sakin aure ba tare da wani kakkarfan dalili ba, haramun ne.
Hakanan kuma Manzon Allah ﷺ yayi gargadi mai tsanani game da duk
matar da taje tayi zina ta samu ciki sannan ta dangantashi zuwa ga mijinta
alhali ta san ba ɗansa
bane. Yace ba zata ɗanɗani komai na rahama ba. Ko kuma Allah
bazai dubeta da rahama ba.
Ya zama wajibi mai wannan tambayar kiji tsoron
Allah ki rika tunawa da lahirarki. Duk abin da kika aikata anan duniya fa, zaki
tarar da sakamakonsa aranar da babu damar yin Qarya, ko kin yi ma bazata rage
miki radaɗin
azaba ba.
Amatsayinki na matar aure, me ya kaiki har kika keɓance da wani Qato, har yayi miki fyaɗe? Kuma in da gaske fyaɗen akayi miki, me ya hana kiyi eehun sa
jama'a zasuji domin su kawo miki 'dauki?? Kuma me yasa baki sanar
da mijinki ko danginki don su ɗauki matakin sanar da hukuma don nema miki hakkin cin
zarafin da akayi miki ba??
Ki tuba ki nemi yafewar Allah da yafewar mijinki
domin hakika kin zalunci kanki kuma kin zalunci mijinki.
WALLAHU A'ALAM.
Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/JLojawdOWYsEOeSHZMNdjf
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
No comments:
Post a Comment
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.