Ticker

6/recent/ticker-posts

Matsayin Alƙunutu Da Ake Karantawa A Sallar Asuba

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Yaya Matsayin Alƙunutu Da ake Karantawa Asallar Asubahi?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

الحمد لله.

Asalin Alƙunutu asallar asuba malamai sun yi saɓani a kansa akwai waɗanda suke ganin shar'antuwarsa kamar malikiyyah da shafi'iyyah, akwai waɗanda basa ganin shar'antuwarsa kamar Hanafiyyah da Hanabila.

Ibnu ƙudama rahimahullah a cikin Almugni (1/449) Ya ce: Ba sunnah bane alƙunutu asallar asuba ko watanta daka cikin salloli, inba wutiriba, haka Assauri yace da Abu hanifa, haka aka ruwaito daka ibnu Abbas, da Abdullahi dan Umar da Ibnu mas'ud da Abul dar-daa'i.

Malik da Abi laila da hasan bin salih da shafi'i sukace: Sunnah ne yin alƙunutu asallar asuba adukkanin za munnah domin Anas ya ce: (Manzan Allah sallallahu Alaihi wasallam baigushe ba yana alƙunutu asallar asuba har yabar duniya) Imamu Ahmad a cikin Musnad ɗinsa.

Umar yakasance yana Alƙunutu agaban sahabbai da wasunsu.

da Abun da aka ruwaito Annabi Sallallahu Alaihi wasallam ya yi alƙunutu tsawon wata guda akan wasu larabawa rayayyu sannan yadena. Muslim.

Abu huraira yaruwaito irin wannan hadisin daka Annabi Sallallahu Alaihi wasallam,

(Annabi Sallallahu Alaihi wasallam yakasance baya alƙunutu asallar asuba saidai idan zai yiwa wasu mutane addu'a ta alkhairi, kozai musu addu'a mummuna.)

Alƙunutun Umar yakasance lokacin saukar musibu domin mafiya yawan ruwayoyi sunzo akan baya alƙunutu, jama'a dayawa sunruwaito haka daka gareshi, wannan yake nuna baya alƙunutu sai alokacin saukar musiba. Mausu'ah fiƙ-hiyyah (34/58).

Tare dacewa magana mairinjaye ita ce: Baya halatta yin alƙuntu asallar asuba ko da yaushe saidai idan masifa tasauka, Saidai babu laifi dankayi sallah abayan wanda yake alƙunutun asallar asuba ɗin, dayin Ameen a addur'asa.

Shaikul Islam ibnu taimiyyah rahimahullah ya ce: Idan mamu yabi limamin dayake alƙunutu asallar asuba ko sallar wutiri zai yi ƙunuti tare dashi, yana alƙunutunne kafin ruku'u ko bayan ruku'u. idan baya alƙunuti ba zai yi ba.

Koda liman yana ganin Mustahabbancin wani abu, mamu kuma baya ganin hakan sai ya barshi dan samun haduwar kai da hadewa yakyauta, Maj-mu'u fatawa (22/ 268).

Dan haka dai lazimtar yin alƙunutu ko da yaushe asallar asuba ba sunnah bane, saidai idan wata matsala ta tunkaro musulmi ko wani bala'i sai aita alƙunutu har sai Allah yakau da wannan matsalar.

WALLAHU A'ALAM

Zauren Tambaya Da Amsa Abisa Alkur'ani Da Sunnah. Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin mu...

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments