𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum Malam da fatan
kana lafiya, tambayata Anan ita ce nakasance ina yawan tunani a cikin sallah,
menene mafita? Nagode
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
الحمد لله
Yawan tunani a cikin sallah ko
aduk wani aiki na ibada da mutum yake aikatawa yana daka cikin aikin Shaiɗan
wanda yake cutar da bayin Allah muminai dashi, har sai yasanyawa mutum damuwa
dakunci darashin nutsuwa dangane da aikinda yagabatar, shi ne ya saka masa
damuwa dangane aikinda yake aikatawa, sai aikin ya zamarwa mutum wahala da bakin
ciki da danuwa, maimakon ya zamto masa kwanciyar hankali da nustuwa da hutu da
azuciyarsa.
Maganin yawan tunani asallah yana
cikin abubuwa biyu masu sauki, sune: riko da ambaton Allah, da kau da kai daka
yawan tunanin, dazarar tunanin yazowa mutum asallar sa ya kau dashi daka
zuciyarsa, ya saka mata tunanin wani abun na lahira, maganin dai shi ne dauke
zuciya daka tunanin dayazo masa asallarsa zuwa wani abun daban.
Kada mutum yadamu da abun da yake
zuwar masa narashin cikar tsarkinsa ko alwalarsa ko cewa anya ban yi tusa ba ko
anya awajan tsarki fitsari bai tabamun tufafi ba, ko bai fallatsarminba, ko
bayan nagama tsarki ragowar fitsarin bai digo min ba, duk lokacin da mutum yaji
wannan ya yi wurgi dashi, shi ne yadaukeshi bai faruba bashida yakini, bai faruba
kawai yaci gaba da sallarsa.
Annabi sallallahu Alaihi wasallam
yashiryar damu akan wanda yawan tunani yake zuwar masa asallarsa ya ce: (yanemi
tsarin Allah daka Shaidan yabar tunanin ) bukhari (3276) da muslim (134).
Amma biyewa tunanin dacigaba dayinsa,
wannan yana jefa mutum cikin damuwa da takura dabakin ciki, kuma zai iya kai
mutum ga hauka, yafitar dashi daka jerin masu hankali.
Asar ya zo daka Ai'isha Allah
yakara yarda da ita ta ce: (Wanda aka jarraba dayawan tunani ya ce: mun yi imani
da Allah da manzansa sau uku, wannan tunanin zaitafi daka gareshi).
Yazo a cikin sahihu muslim daka
usman bin Abil Ãaas yace : Shaiɗan yana rikitani tsakanina da sallah ta da
karatuna, sai Annabi salallallahu Alaihi wasallam ya ce: (Wannan wani Shaiɗan
ne da'ake ce masa kanzab, kanemi tsarin Allah dashi ka yi tofi abangaren
hagunka sau uku,) ya ce: sai nayi haka sai Allah yatafiyarmin dashi,.
Imamun nawawi rahimahullah ya ce:
wasu malamai sukace: an so wanda tunani ya zo masa asallah ko alwala ko tsarki ya
ce: La'ilaha illallahu, domin Shaiɗan idan yaji an ambaci Allah yana dakatawa baya
iya karasowa wurin, la'ilaha ilallahu kuma ita ce tushen duk wani ambaton
Allah.
Mafi amfani wajan magance
matsalar tunani asallah shi ne yawaita ambaton Allah, Fatawa fiƙhiyyah Alkubra (1/149).
Maganin yawan tunani asallah shi
ne yawaita ambaton Allah, dakuma rokonsa waraka akan hakan, darashin mika wuya
ga tunanin, wajibi ne mutum yakauda tunanin duk sanda ya zo masa, kamar ka yi tsarkin
fitsari ko wankan janaba, sai tunani yafado maka cewa baka wanke kankaba to
kada kaci gaba da tunanin baka wanke kankaba, kawai zaka sawa ranka karyane
kawanke kanka, kawatsar da tunanin gaba daya haka za ka yi asauran ibadoji,
zakana watsar da duk wani tunanin dayazo maka, kada kaci gaba dayinsa, domin
daka Shaiɗan ne, kayawaita neman tsarin Shaiɗan wajan Allah.
Fatawa lajnatul da'imah (5/226)
Koda asallah ne idan tunani ya zo
maka ka yi kayi wajan wurgar dashi amma yana dawo maka, yahalatta kai a'uziyya
ka yi tofi a ɓarin hannun hagu dinka sau uku.
WALLAHU A'ALAM.
Zauren Tambaya Da Amsa Abisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin
mu...
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
Post your comment or ask a question.