𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum malam ina son na
san suwaye aure yawajaba a kansu?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
الحمد لله.
Hukunci Aure yana Sabawa da saɓanin
halin da Mutum ya Samu kansa da Kuma Abun da yake dashi, Aure wajibi ne akan
Wanda ya Samu iko, Idan ransa yana so kuma yana tsoran Aukawa zina, domin tsare
kai, da Kame kai daka haram dolene, hakan ba zai Samu ba saida Aure.
Ƙurduby ya ce: Wanda yake da
damar Aure yake tsoran cutar da kansa da Addininsa daka sha'awar da bata
gushewa saida Aure, Babu Wani saɓani akan Wajabcin Aure a kansa.
Marudi Rahimahullahu a cikin
littafinsa Al-Insaaf ya ce: Wanda yake tsoran fadawa zina, Aure a kansa Wajibi
ne kai tsaye, .
Duba Al-Insaaf Mujalladi na (8)
Kitabul Nikah, Ahkamul Nikah.
Idan ransa yana Son Aure, amma
yasan ba zai iya ciyar da matar ba, sai ya kame.
Fadin Allah madaukakin sarki ya
wadatar Masa (Waɗanda Basu samu halin yin Aure ba, su kame har sai Allah ya
wadatasu daka falalarsa...
Ya kuma ya waita Azumi, domin
azumi kariya ne daka Sha'awa.
Kamar yanda Abdullahi dan Mas'uud
ya ruwaito daka Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam.
Duba Fiƙhussunnah (2/15-18).
Wajabcin Aure baya faduwa akan
Wanda yasan ba zai iya haƙura da Saɓawa Allah ko fadawa zina ba ko kallace
kallace da Sauran Abubuwa da Shari'a ta tsoratar..
Duk Wanda ya yi nazarin Wannan
zamanin da Muke ciki da Abun da yake tattare dashi na ayyukan ɓarna kala-kala,
zai gamsu cewa wajabcin yafi tsanani da Ƙarfi sama da Za munnan da Suka wuce..
Muna Roƙon Allah ya tsarkake zuƙatanmu
ya Nisantar da tsakaninmu da Haram, ya Azurtamu da Kamewa.
Zauren Tambaya Da Amsa Abisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin
mu...
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.