𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum malam, ina kwana? Tambayata ita ce mutum idan ya tashi da safe ba zai iya addu'a ba akwai wata addu'a dan kar bacci ya dauke shi, kuma shin idan yayi bacci ya yi laifi? Allah ya taimaka Ameen.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus
salam, Ba wata addu'a a Sunnah da ake karantawa don ta hana mutum yin barci
bayan sallar Asubahi, idan kuma akwai to ni ban san ta ba, babu laifin komai ga
wanda ya yi nufin yin azkar sai barci ya ɗauke
shi kafin ya kai ga wannan azkar ɗin,
Allah shi ke cire ran mutane a lokacin da barci ya ɗauke su, saboda haka ba ki da laifin komai don
kin yi nufin yin azkar ɗin
Safiya sai barci ya ɗauke
ki, ko Bahaushe ma ya ce "barci ɓarawo
ne", duk lokacin da kika farka sai ki yi azkar ɗin.
Allah S.W.T ne
mafi sani.
Jamilu Ibrahim
Sarki, Zaria.
Ga Masu
Buqatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin
mu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/Fb6qgYPXfEeHb8CD1SWAkK
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ
ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
[11:42 PM,
5/6/2023] Malam Khamis Yusuf Tambayoyi 2: BARCI YA ƊAUKE NI KAFIN SALLAR
ISHA'I HAR LOKACINTA YA WUCE, YA ZAN RAMA TA?
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu
alaikum malam Allah ya saka ma da alkhairi, tambayata ita ce wani lokacin in na
zauna sai bacci ya dauke ni kuma ban yi sallar Isha ba, shin meye ne matsayina,
shin zan raba sallah ne ko yaya?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus
Salamu, wanda barci ya kwashe shi bai sami damar yin sallar Isha'i ba har sai
da lokacinta ya wuce, to da zarar ya farka daga barci zai rama wannan sallar ce
ta Ishá'i, sannan sai ya yi sallar Asubahi, idan kuma ya ga zai rasa jam'i na
sallar Asubahi idan ya tsaya rama ta, ko kuma lokacinta zai fita, to sai ya yi
sallar Asubahin, sannan sai ya rama sallar Ishá'i ɗin daga baya.
Idan kuma mace
ce da take sallah a gidanta, to ita ma sai ta rama sallar Ishá'i ɗin, daga nan kuma sai ta yi
Asubahi, idan kuma ta ga lokacin asubahi zai fita idan ta tsaya rama Ishá'i ɗin, to ita ma za ta fara
yin sallar Asubahin ne, daga bisani sai ta rama sallar Ishá'i ɗin.
Allah ne mafi sani.
Jamilu Ibrahim
Sarki, Zaria.✍🏻
Ga Masu
Buqatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin
mu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/IqsWWSpUkwk6b8hWJ6vXOO
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
Post your comment or ask a question.