Ticker

6/recent/ticker-posts

Allah Ba Ya Karɓar Duk Aikin Da Ba Ikhlasi A Ciki Komin Kyansa

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum, don Allah Mlm ina da tambaya, Mlm na kasance mai son aikin alkairi kuma idan na tashi aikatawa sai na dinga ji zuciyata na raya min don riya nake yi, ko sadaka idan na zo zan yi in dai da mutane a gun sai na fasa saboda zan rika jin ai za su ce ina yi dan a fada, ni kuma sai na fasa, wallahi Mlm ko karatun Alqur'an nake yi wasu suka shigo gidanmu sai na ji muryata ta sauya, in na ji haka sai na daina, saboda ba na son na dinga aiki dan wanin Allah, kuma  duk lokacin da zan yi aikin alkairi ln dai da mutum a gurin sai na fasa don Allah Mlm idan da akwai addu'ar da zan dinga yi nadaina a taimaka mini da ita, ban son na dinga aiki dan riya,  na gode Allah ya saka da alkairi ya sa mu dinga aiki da abun da za mu ji Mu amfana.

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa'alaikumus Salamu, Tabbas Allah ba ya karɓar duk wani aiki da aka yi shi ba tsarkin ninya (ikhlasi), dole ne kowani musulmi ya yi iya qoqarinsa wajen ganin ya riqa yin duk wani aiki don Allah, ba don mutane su gani su yaba masa ba, matuqar ba a sami wannan a cikin ayyukan bawa ba, to waɗannan ayyukan Allah ba zai karɓe su ba, kamar yadda ayoyi da hadisai da dama suka yi gargaɗi, daga ciki, Allah S.W.T a hadisul Qudusiy yana cewa: "Ni na wadatu daga mushirikai game da shirka, duk wanda ya aikata kowane irin aiki ya haɗa ni da wani na a cikinsa, to na bar shi da shirkarsa".  Sahihu Muslim 2985 .

Wannan na nufin duk wanda ya aikata wani aikin Allah don mutane su gani su yaba masa, to Allah ya bar shi da wannan aikin da ya yi, ba zai karɓa masa ba. A wani hadisin da Abuhurairata ya ruwaito, Annabi ya ce: "Duk wanda ya jiyar da aiki Allah zai jiyar masa da shi, haka duk wanda ya nunar Allah zai nunar masa da shi".

Bukhariy 6499, Muslim 2986.

Wannan na nufin duk wanda ya yi wani aikin lada don mutane su ji su yaba masa Allah zai sa mutane su ji aikin, haka nan wanda ya yi aiki don mutane su gani su ce ya iya, to Allah zai nunawa mutane su gani su yaba masa, amma ba shi da sakamako na lada a lahira, har ma zai sami zunubi na haɗa Allah da wani a cikin aikinsa, saboda mai yin riya yana yi ne don mutane su yaba masa, sannan ta wani ɓangaren kuma yana son Allah ya ba shi lada, don haka wannan shirka ce qarama in ji wasu malaman. Allah ya tsare mu da yin riya a cikin dukkan ayyukanmu.

Game da addu'a da kike nema wanda za ki riqa yi don Allah ya raba ki da riya, to ni a gaskiya ban san wata addu'a keɓantacciya da ake yi don Allah ya raba mutum da riya ba, amma dai qofar addu'a a buɗe take, matuqar ba ta saɓa wa shari'a ba, wato kenan za ki iya yin addu'a a kan Allah ya raba ki da aikata riya, ki nace a kan hakan a duk lokacin da kika yi sujjada, kuma ki riqa tashi cikin dare kina roqon Allah ya raba ki da riya, in Allah ya so Allah zai taimaka maki a kan hakan. Kuma za ki iya haɗawa da wannan addu'ar ta Manzon Allah  :

يَا مُقَلِّبَ القُلُوبِ ثَبِّتْ قَلْبِي عَلَى دِينِكَ.

Shahru bin Haushab ya tambayi Ummu Salamata  cewa wace addu'a ce Manzon Allah ya fi yawan yi idan yana wurinki? Sai ta ce: "Addu'ar da ya fi yi ita ce:

يَا مُقَلِّبَ القُلُوبِ ثَبِّتْ قَلْبِي عَلَى دِينِكَ.

 Sai ta ci gaba da cewa: "Na tambayi Manzon Allah cewa; mene ya sa mafi yawan addu'arka ita ce wannan? Sai ya ce: "Lallai babu wani ɗan'adam face zuciyarsa tana tsakanin yatsu biyu daga cikin yatsun Allah"".

Sunanut Tirmizhiy 3522.

Allah ne mafi sani.

Jamilu Ibrahim Sarki, Zaria.🏻

Ga Masu Buqatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin mu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/DSdbBS8RZVoIKYG5exOuZE

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments