𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum Malam tambayata anan ita ce Malam Allah yana yafe laifin zina? ko kuwa sai anyi wa mutum bulala ɗari? Ko kuma idan yabari shikenan Allah yana yafewa tunda mutum baiyi aure ba, kuma babu wanda yasani sai Allah? Kuma yanzu wallahi na yi nadama malam yaya zanyi dan Allah?? Kuma dan Allah malam mutum zai iya aurar wanda bai taɓa yin zina ba? kuma idan mukayi aure alhakinsa yana kaina ko kuwa yana kan wancan mutumin da ya yaudareni? kuma idan mutum ya Tuba Allah zai yafe mai kuma yakoma kamar beyiba? malam ina son inji.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikis
salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.
Allah Madaukakin
Sarki ya faɗa a cikin
Alƙur'ani
mai girma cewa: "KA GAYA (MUSU) "YAKU BAYINA WAƊANDA
SUKA AIKATA ƁARNA
a kan KANSU!! KADA KU FIDDA TSAMMANI DAGA SAMUN RAHAMAR ALALH, HAKIKA ALLAH
YANA YAFEWA DUKKAN ZUNUBAI. SHI SHI NE MAI GAFARA, MAI JIN ƘAI".
Sayyiduna
Abdullahi bn Abbas (ra) ya ce: Dalilin saukar wannan ayar shi ne akwai wasu
mutane ne waɗanda suka
aikata kisan kai da yawa, kuma sukayi zinace-zinace da yawa, sai suka zo wajen
Manzon Allah ﷺ suka
tambayeshi "Abin da kake kiran mutane zuwa gareshi (wato Musulunci) abu ne
mai kyawu. To amma muna so ka bamu labari shin akwai wani abin da zai kankare mana
zunuban da muka aikata ne?"
To sai Allah
ya saukar da ayar nan ta cikin suratul Furƙan da kuma wannan ayar wacce na kawota
asama.
(Aduba Sahihu
Muslim hadisi na 122, da sunanul Kubra ta Imamun Nisa'iy hadisi na 11,449).
Hakanan Imamu
Ahmad bn Hanbal a cikin Musnadinsa ya kawo cewar bayan saukar wannan ayar sai
Annabi ﷺ ya ce
"Wannan ayar tafi mun duniya da abun cikinta".
Sai wani
Sahabi ya ce "Ya Rasulallahi har wanda ya yi shirka ma? Sai Annabi ﷺ ya ce "KU SAURARA!
HAR WANDA ya yi SHIRKA (SHIMA IDAN YA TUBA ALLAH ZAI YAFE MASA)".
Hakanan akwai
hadisi a cikin Musnadin Imamu Ahmad wanda aka ruwaito ta hanyar Sayyiduna Amru
bn 'Abisah (rta) ya ce "Wani mutum tsoho tukuf yazo wajen Manzon Allah ﷺ yana dogarawa da sanda, ya
ce "Ya Rasulallahi ina da wasu manyan laifukan da na aikata irin na
yaudara da fajirci. Shin Allah zai yafe mun kuwa?".
Sai Manzon
Allah ﷺ ya tambayeshi
"Shin ka shaida cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah?"
Sai mutumin ya
ce "Kwarai kuwa. Kuma na shaida cewa lallai kai Manzon Allah ne! ".
Sai Manzon
Allah ﷺ ya ce masa
"Ai an riga an yafe maka laifukanka".
(Musnadu Ahmad
4/385).
Abu mafi
muhimmanci dai ga duk wanda Allah ya jarrabeshi ya afka cikin kurakurai, shi ne
gaggauta yin cikakkiyar tuba zuwa ga Allah ɗin.
Allah ya ce:
"KU TUBA ZUWA GA ALLAH BAKI ƊAYANKU YAKU MUMINAI, DOMIN KU SAMU
RABAUTA".
Sannan Manzon
Allah ﷺ ya ce
"WANDA YA TUBA DAGA ZUNIBI, TAMKAR WANDA BASHI DA ZUNUBI NE".
Sai dai ita
tuba tana da wasu sharudda waɗanda
sai an cikasu sannan tubar take zama karbabbiya. Gasu nan kamar haka:
1. Dena aikata
saɓon, nan take ba
tare da jinkiri ba.
2. Yin nadama
bisa laifukan da mutum ya aikatasu abaya.
3. Ɗaukar niyyar
cewa mutum bazai Ƙara aikata wannan laifin ba, har abada.
4. Ɗaukar
matakin rabuwa da duk wata hanya ko dalilin da zai iya sanya mutum ya sake
komawa kan laifinsa na baya. Misali kamar rabuwa da miyagun samari (Har da
blocking ɗin
lambobinsu, dena alaƙa dasu ko da a kan facebook ko whatsapp da sauransu) ko
miyagun Ƙawayen
da ke aikata alfasha, tsayar da mijin aure, etc.
5. Idan laifin
ya shafi hakkin wani Bil Adama ne (misali kamar sata, ha'inci, da sauransu) to
wajibi ne amayar da hakkoki zuwa ga masu shi, ko kuma anemi yafewarsu.
In Shã Allahu
rayuwarki za ta gyaru mutukar dai kin tuba domin Allah. Kuma wannan laifin bai
shafi hakkin mijin da za ki aura ba. Don haka ba sai kin gaya masa ba. Kiyi
shuru da bakinki don kiyaye mutuncinki.
WALLAHU
A'ALAM.
Ga Masu Buƙatar
Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin
mu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/BSA30hdZD7V3WSJF8WVwUj
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.