Ticker

6/recent/ticker-posts

Falalar Karanta Suratul Mulk A Kowane Dare

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum malam, barka da warhaka da fatan an tashi lafiya, Allah ya qara lfy da nisan kwana, amin. Malam tambayata ita ce game da wani labari da na ji cewa wata mata ta mutu gawarta tana kamshi sai aka ce tana karanta suratul mulk ne idan za ta yi bacci. Ina son qarin bayani malam game da wannan magana.

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa'alaikumus Salám. 'yar uwa a iya abin da na sani ban taɓa jin ko da wannan labari ba daga wurin malamai, kuma ban taɓa ganinsa a karatu ba, sannan kuma bai yi kama da ingantaccen labari ba. Abin da kawai na san ya tabbata daga Manzon Allah shi ne abin da Attirmizhiy da Annasá'iy suka ruwaito cewa:

i. Haqiqa Annabi ya ce: "Lallai akwai wata sura a cikin Alqur'ani mai ayoyi talatin, ta ceto wani mutum har sai da aka gafarta masa zunubansa ita ce suratu تبارك الذي بيده الملك" Attirmizhiy (2891).

ii. Daga Jabir Allah ya qara masa yarda cewa: Lallai Manzon Allah ya kasance ba ya yin barci har sai ya karanta الم تنزيل  (suratus Sajada), da تبارك الذي بيده الملك (suratul Mulk). Attirmizhiy (2892).

iii. Daga Ibn Mas'ud Allah ya qara masa yarda ya ce: "Duk wanda ya karanta (تبارك الذي بيده الملك) a kowane dare, to Allah zai hana masa azabar qabari da ita, mun kasance a zamanin Manzon Allah muna kiranta da suna ALMÀNI'A (mai hana azaba), lallai tana cikin littafin Allah, sura ce da wanda duk ya karanta ta a kowane dare, haqiqa ya  yawaita lada, kuma ya sami dacewa". Assunanul Kubra Linnasá'iy (10479).

Don haka, 'yar uwa wannan shi ne abin da na san ya tabbata daga Manzon Allah da Sahabbansa a game da karanta suratul Mulk a kowane dare. Wancan labarin kuwa na cewa wata mata gawarta tana qamshi saboda karanta wannan sura da take yi ban san inda masu wannan labarin suka qwaqulota ba.

Allah Ta'ála ne mafi sanin dai-dai.

Jamilu Ibrahim, Zaria.

Ga Masu Buqatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin mu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/JoWs3feDfdyGE9yBsa1RSC

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments