𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum malam, barka da warhaka da fatan an tashi lafiya, Allah ya qara lfy da nisan kwana, amin. Malam tambayata ita ce game da wani labari da na ji cewa wata mata ta mutu gawarta tana kamshi sai aka ce tana karanta suratul mulk ne idan za ta yi bacci. Ina son qarin bayani malam game da wannan magana.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus
Salám. 'yar uwa a iya abin da na sani ban taɓa
jin ko da wannan labari ba daga wurin malamai, kuma ban taɓa ganinsa a karatu ba,
sannan kuma bai yi kama da ingantaccen labari ba. Abin da kawai na san ya
tabbata daga Manzon Allah ﷺ
shi ne abin da Attirmizhiy da Annasá'iy suka ruwaito cewa:
i. Haqiqa
Annabi ﷺ ya ce:
"Lallai akwai wata sura a cikin Alqur'ani mai ayoyi talatin, ta ceto wani
mutum har sai da aka gafarta masa zunubansa ita ce suratu تبارك الذي بيده الملك"
Attirmizhiy (2891).
ii. Daga Jabir
Allah ya qara masa yarda cewa: Lallai Manzon Allah ﷺ ya kasance ba ya yin barci har sai ya karanta
الم تنزيل (suratus Sajada), da تبارك الذي
بيده الملك (suratul Mulk).
Attirmizhiy (2892).
iii. Daga Ibn
Mas'ud Allah ya qara masa yarda ya ce: "Duk wanda ya karanta (تبارك الذي بيده الملك)
a kowane dare, to Allah zai hana masa azabar qabari da ita, mun kasance a
zamanin Manzon Allah ﷺ
muna kiranta da suna ALMÀNI'A (mai hana azaba), lallai tana cikin littafin
Allah, sura ce da wanda duk ya karanta ta a kowane dare, haqiqa ya yawaita lada, kuma ya sami dacewa". Assunanul
Kubra Linnasá'iy (10479).
Don haka, 'yar
uwa wannan shi ne abin da na san ya tabbata daga Manzon Allah ﷺ da Sahabbansa a game da
karanta suratul Mulk a kowane dare. Wancan labarin kuwa na cewa wata mata
gawarta tana qamshi saboda karanta wannan sura da take yi ban san inda masu wannan
labarin suka qwaqulota ba.
Allah Ta'ála
ne mafi sanin dai-dai.
Jamilu Ibrahim,
Zaria.
Ga Masu
Buqatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin
mu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/JoWs3feDfdyGE9yBsa1RSC
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
FALALAR KARANTA SURATUL MULK A KOWANE DARE
Tambaya:
An ji labari cewa wata mata ta mutu gawarta tana ƙamshi
saboda tana karanta Suratul Mulk kafin barci. Shin wannan gaskiya ne? Kuma
menene sahihin abin da ya tabbata game da karanta Suratul Mulk?
Amsa:
Assalamu alaikum wa rahmatullah.
1. Game da labarin cewa wata mata gawarta tana ƙamshi
saboda karatun Suratul Mulk —
babu wani tushen sahihi.
Babu hadisi, ba daga Sahabbai, ba daga Attabi'ai, kuma babu
malamin Sunnah wanda ya kawo wannan labari.
Saboda haka, wannan ya fi kama da labarin kirkirarre da
mutane suka yada.
Abin da ya tabbata da dalili sahihi:
① Suratul Mulk tana kare mutum daga
azabar kabari
Hadisi:
عَنْ ابْنِ مَسْعُودٍ رَضِيَ اللهُ عَنْهُ قَالَ:
«سُورَةٌ تَبَارَكَ الَّذِي بِيَدِهِ الْمُلْكُ،
هِيَ الْمَانِعَةُ مِنْ عَذَابِ الْقَبْرِ»
—
النسائي في الكبرى
(10479)
Ma’ana:
“Surah Tabārakalladhī biyadihil-mulk ita
ce mai hana azabar kabari.”
② Suratul Mulk ta ceton mutum har sai da
aka gafarta masa
Hadisi:
قَالَ رَسُولُ اللهِ ﷺ:
«إِنَّ سُورَةً مِنَ الْقُرْآنِ ثَلَاثُونَ آيَةً،
شَفَعَتْ لِصَاحِبِهَا، فَغُفِرَ لَهُ، وَهِيَ تَبَارَكَ الَّذِي بِيَدِهِ الْمُلْكُ»
—
الترمذي
(2891)
Ma’ana:
“Wata sura daga Alƙur’ani ayoyi talatin, ta yi wa
mai karanta ta shafa’a
har Allah ya gafarta masa —
ita ce Suratul Mulk.”
③ Annabi ﷺ ba ya yin barci sai
ya karanta Suratul Sajada da Suratul Mulk
Hadisi:
كَانَ النَّبِيُّ ﷺ لَا يَنَامُ حَتَّى يَقْرَأَ:
«الم تَنزِيلُ» (السجدة) وَ «تَبَارَكَ الَّذِي
بِيَدِهِ الْمُلْكُ»
—
الترمذي
(2892)
Ma’ana:
Manzon Allah ﷺ ba ya yin barci sai ya karanta Surat
As-Sajda da Suratul Mulk.
Kammalawa
Suratul Mulk tana da falala mai girma, kuma:
• tana hana azabar kabari,
• tana kawo shafa’a,
• Annabi ﷺ yana karanta ta duk
dare.
Amma labarin cewa:
“Wata mata gawarta tana kamshi saboda
Suratul Mulk”
— ba shi da asali, kuma bai kamata a
jingina shi ga addini ba.
Allah Ta'ala ne mafi sani.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.