Ticker

6/recent/ticker-posts

Za mu iya sallar idi a gida, saboda tsoran corona ?

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu Alaikum Warahmatullahi. Dr ina tambaya ne kan halaccin sallar idi a gida ga waɗanda suke da halin yin haka, sakamakon rashin yiwuwar zuwa sallar idi, saboda kasantuwar annoba ta corona virus. Allah ya saka da alkhairi

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikum assalam. Sallar Idin karamar Sallah na daga cikin Shariar Musulunci, Allah ya yi umarni da ita saboda hadin-kan Musulumai da kuma godewa Allah bisa ni’imar Azumi .

Wasu malaman sun tafi a kan wajabcinta, sai dai a mazhabar Malikiyya Sunna ce mai muhimmancin gaske.

Asali ana yin sallar Idi ne a Musallah a wajen gari, duk da cewa ana iya yinta a Masallatai.

Malamai suna cewa wanda bai samu damar yin Sallar idi ba a cikin Jama’a ya halatta ya rama ta a gida, shi kaɗai ko kuma cikin jam’i, saboda abin da aka rawaito daga Anas dan Malik (Sahabin Manzo Allah) cewa: yana rama sallar Idi a gida idan ta kufce masa tare da iyalansa da barorinsa, kamar yadda Ibnu-abi Shaibah ya rawaito a Musannaf a lamba ta (5853) haka nan Baihaki a cikin Sunan a lamba ta (6031), yana daga cikin Ka’idojin Sharia sanannu : aikin Sahabi Hujja ne, mutukar ba’a samu Sahabin da ya Saɓa masa ba kuma ita ce fatawar Ada’a bn Abi-Rabah daga cikin manyan Tabi’ai kamar yadda ya zo a Sahihul Bukhari 1/334.

Bisa abin da ya gabata wanda yake jin tsoran Corona ko kuma aka sanya dokar hana sallar Idi a jaharsa, zai iya yin sallarsa a gida, idan za ka yi sallar Idi a gida za ka yi ta da sifarta ta raka’a biyu da karatu a bayyane, da kuma kabbarori Bakwai a raka’ar Farko, shida a raka’a ta biyu, sai dai ba za ka Yi huduba ba.

Don neman karin bayani duba: Mugni Almuhtaaj 2/286

Allah ne mafi sani

Amsawa✍️

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin mu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/DSdbBS8RZVoIKYG5exOuZE

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments