𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum Warahmatullahi. Dr ina tambaya ne kan
halaccin sallar idi a gida ga waɗanda suke da halin yin haka, sakamakon rashin
yiwuwar zuwa sallar idi, saboda kasantuwar annoba ta corona virus. Allah ya
saka da alkhairi
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikum assalam. Sallar Idin karamar Sallah na daga
cikin Shariar Musulunci, Allah ya yi umarni da ita saboda hadin-kan Musulumai
da kuma godewa Allah bisa ni’imar Azumi .
Wasu malaman sun tafi a kan wajabcinta, sai dai a mazhabar Malikiyya Sunna ce mai
muhimmancin gaske.
Asali ana yin sallar Idi ne a Musallah a wajen gari, duk
da cewa ana iya yinta a Masallatai.
Malamai suna cewa wanda bai samu damar yin Sallar idi ba
a cikin Jama’a ya halatta ya rama ta a gida, shi kaɗai ko kuma cikin jam’i,
saboda abin da aka rawaito daga Anas dan Malik (Sahabin Manzo Allah) cewa: yana
rama sallar Idi a gida idan ta kufce masa tare da iyalansa da barorinsa, kamar
yadda Ibnu-abi Shaibah ya rawaito a Musannaf a lamba ta (5853) haka nan Baihaki
a cikin Sunan a lamba ta (6031), yana daga cikin Ka’idojin Sharia sanannu :
aikin Sahabi Hujja ne, mutukar ba’a samu Sahabin da ya Saɓa masa ba kuma ita ce
fatawar Ada’a bn Abi-Rabah daga cikin manyan Tabi’ai kamar yadda ya zo a
Sahihul Bukhari 1/334.
Bisa abin da ya gabata wanda yake jin tsoran Corona ko
kuma aka sanya dokar hana sallar Idi a jaharsa, zai iya yin sallarsa a gida,
idan za ka yi sallar Idi a gida za ka yi ta da sifarta ta raka’a biyu da karatu
a bayyane, da kuma kabbarori Bakwai a raka’ar Farko, shida a raka’a ta biyu, sai dai ba za ka Yi huduba ba.
Don neman karin bayani duba: Mugni Almuhtaaj 2/286
Allah ne mafi sani
Amsawa✍️
DR. JAMILU YUSUF ZAREWA
Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin
mu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/DSdbBS8RZVoIKYG5exOuZE
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.