𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Shin Ya Halatta Wanda Bashi Da Ikon Zuwa Sallar Idi
Yayita Agida?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
الحمد لله والصلاة والسلام على رسول الله.
Sallar idi farillace a kan dukkkan wani namiji wanda yake da iko.
Idan bazaka iya zuwa Wajan sallar idi ba, saboda rashin
lafiya ta jiki, Babu komai akanka, To Shin an halarta maka kayita agid?
Akwai Saɓanin malamai akai, Jamhurdin malamai Sukace: ya
halatta Saɓanin Hanafiyya, Muzni ya ruwaito daka shafi'i Rahimahullah A cikin Muktasarul Ummu, (8/125) Zai yi
Sallar idi shi kaɗai agidansa da matafiyi da bawa da mace duk zasuyi Sallar idi
agida.
Alkarshi Almaliki ya
ce: Mustahabbine gawanda Sallar idi takubuce masa tare da liman ya sallaceta
shi kaɗai, Shin a cikin jama'a zai sallaceta koshi kaɗai? Maganganu biyune
Sharshin Kurshi (2/104).
Marudi A cikin (Insaaf)
ya ce: Idan sallar idi takubucewa mutum Anso yaramata ayanda take, (Kamar yanda
liman yake sallatarta).
Ibnu ƙudama a
cikin "Almugni" Ya ce: Wanda Sallar idi takubuce masa yanada zabi, inya
ga dama ya sallaceta ajam'i inya ga dama ya sallaceta shi kaɗai.
Ibnu Abidin Alhambali yaec: Bazai Sallaceta Shi kaɗai ba
idan takubuce masa.
Shaikul Islam Ibnu taimiyya yazabi maganar Hanafiyya,
Shaik Usaimin yarinjayar da ƙaulinsu A
cikin Sharhin Mumti'i (5/156).
Ya zo Afatawa Lajnatul Da'ima (8/306) "Sallar idi
farilla ce dawani yake daukewa wani ita, idan Wasu Suka yita waɗanda Sun
wadatar Zunubi yafadi a kan Sauran
Mutane.
Wanda takubuce masa kuma yanasan yaramata Anso masa
hakan, Ya sallaceta a Sifarta batare dayin khuduba abayantaba, Kamar yanda
Imamu Malik da Shafi'i da Ahmad Da Naka'i dawasunsu daka cikin malamai sukace,
Asalin hakan shi ne fadin Annabi sallallahu Alaihi wasallam (Idan zakuje sallah
kutafi kuna masu nutsuwa Abun da kuka riska ku Sallata Abun da yakubuce muku ku
cikaso).
Da hadisin Anas bin Malik Allah yakara yarda dashi, ya
kasance idan Sallar idi takubuce masa yana tara iyalansa da bayinsa, Sannan Sai
Abdullahi bin Abi utbah bawansane ya yi musu
sallah raka'a biyu, Yana kabbara a
cikinsu.
Wanda yaje idi yatarar Angama Sallah liman yana khuduba,
Zai saurari khuduba, sannan saiya rama sallar bayan khuduba danya haɗa Maslaha
guda biyun, sallah da sauraren khuduba.
WALLAHU A'ALAM.
Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin
mu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/CƘ9TMXMrWDx1y7sYye2znU
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.