Ticker

6/recent/ticker-posts

Wajabcin Kwanciya Da Niyyar Azumi

Daga Hafsatu Uwar Mumunai R.A) ta ce:

 Haƙiƙa Manzon ALLAH {}  ya ce:

Wanda bai kwanta da niyyar azumi kafin alfijir ba, ba shida azumi.

A cikin wani ruwayan Dara ƙuɗini  ya ce:

Babu azumi ga wanda bai farlanta shi ba daga dare.

SHARHI:

Wannan hadisi yana mana nuni da cewa idan mutum yanaso yatashi da Azumi washe gari, to wajibi ne ya kwanta da niyyar Azumin a zuciyarsa, idan kuwa bai yi hakan ba, to ba shi da Azumin wannan ranar.

ALLAH ka karɓi ibadunmu, ka gafarta mana zunubanmu baki ɗayanmu Ameen.

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments