Haƙƙa ayoyin alƙur'ani mai girma sun zo da kwaɗaitar da Musulmi a kan ciyarwa saboda ALLAH a lokacin Azumi da lokacin da bana azumi ba.
Da taimakawa talakawa da mabuƙata domin yaƙar talauci a tsakanin al'ummar musulmai.
Kuma yin haka na ƙara
tabbatar da '‘yan uwantakar
musulunci a tsakanin musulmai.
Daga cikin waɗannan ayoyin akwai fadar ALLAH {S.W.T}
cewa:
Waɗanda suke ciyar da dukiyoyinsu dare da
rana, ɓoye da bayyane, suna da sakamakon lada
a wurin UBANGIJIN su kuma basa tare da kowane irin tsoro ko baƙin ciki a ranar alƙiyama.
[Surah ta: Baƙarah
Ayata: 274]
Ku ciyar daga Abin da muka fitar muku na tsirrai daga ƙasa, kada ku nufi marasa kyau a cikinsa kuna ciyar dashi,
alhali ku baku
karɓarsa, sai in kun daure kun runtse ido,
ku sani ALLAH {S.W.T} mawadaci ne ga abin da duk za ku ciyar kuma wanda ya
cancanci yabo ne a cikin ko wani hali.
[Surah Baƙarah Ayata:267]
Ba za ku samu cikakkiyar lada, har sai kun ciyar da abin da kuke so, abin
da duk kuka ciyar na alkhayri, to ALLAH Masani ne game da shi.
[Surah ta Nisa'a Ayata: 92]
Manzon ALLAH {s.a.w} Ya ce:
Lallai bawa ya taɓe kuma ya yi asara idan ALLAH {S.W.T}
bai saka masa tausayin ‘yan
Adam a cikin zuciyarsa ba.
[Silsilatus Sahiha: 456]
Manzon ALLAH {s.a w} Ya ce:
Duk wanda ya ciyar da mai Azumi da abin buɗa
baki, yana da kwatankwacin ladarsa, ba tare da an tauye wani abuba daga ladar
mai Azumin.
[Ahmad 4/114] [Tirmizi, Ibn Majah 1746].
Manzon ALLAH {s.a.w} Ya ce:
Aikin wanda yafi falala shi ne ka shigar da murna a cikin zuciyar ɗan
uwanka mumini ko ka biya masa bashi ko kaciyar dashi.
[Silsilatus sahiha:1494].
Manzon ALLAH {s.a.w} Ya ce:
Kada ku ciyar da talakawa daga abin da Ku bakwa cinsa.
[Sisilatus sahiha: 2426]
Waɗannan ayoyi da hadisai dukkansu suna
mana nuni ne da abubuwa guda biyu,
Falalar ciyarwa ga mai Azumi dama wanda baya Azumi.
Sai kuma nuni da hani da ciyar da ko sadaka da abin da kasan kai idan an ba
ka ba za ka karɓa ba.
Kada ka yi kunu ko ƙosai
da geron da bai da kyau, ko waken daya lalace, wanda ku ba za kuniya cinsa ba.
Kada ka dafa shinkafar da kai kasan bakacin irinta, kuma ka bawa wani ita
sadaka.
Kada ka bayarda abin da kai inda an ba ka ba za kaci ba, kuma ba za ka karɓa
ba.
Kada ka yi sadaka da shadda ko Atampha wacce kai idan an ba ka ba za ka iya
sawa ba, a maimakon ka sami lada saika sami zunubi.
Kada ku ciyar da abincin daku bashi kuke ciba, bashi kuke ciyar da '‘ya'‘yanku
ba.
Kada ku yi sadaka da kuɗin da ya fatattake wanda ku idan anbaku
ba za ku karɓa.
Lallai kowa zai sami sakamakon abin da ya bayar wa mauƙata mai kyau ko mara kyau.
ALLAH ya baka da yawa kaima ka bayar da yawa, ALLAH ya baka abu mai kyau
kaima ka bayar da mai kyau.
Ba aneman Aljannah da abinci mara kyau, da abinsha mara kyau, da kaya
marasa kyau, lallai ALLAH mai shi ne mafi kyawu kuma yanason abu mai kyau.
ALLAH ka bamu ikon aiki da abin da muka karanta.
ALLAH ka gafarta mana zunubanmu baki ɗayanmu Ameen.
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.