Ticker

6/recent/ticker-posts

Me Zan Yi Idan Na Dace Da Daren Lailatul Qadri, Alhalin Ina Haila?

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu aliakum malam barka da asuba ya ibada ya kokari ALLAH ya taimaka ameen dan ALLAH malam tambaya ce da ni ni ce haila tazomin to shi ne nake so amin bayani ya ya zan yi dan dacewa da daren lailatul ƙadr alhalin ina haila ba damar in yi sallah nagode ALLAH yasaka malam da mafificin alkhairi

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikumus salam wa rahmatullahi wa barakatuh. Alhamdu lillahi rabbil alamin wassalatu wassalamu ala rasulillah wa ala alihi wa sahbihi ajma'in.

Wannan al'amari In shã Allahu, abu ne mai sauƙi, haila ba za ta hana maki dacewa da falalar daren lailatul ƙadri ba, ko da falalar da sauran musulmi ke dacewa da ita idan ba ta sallah ba a wannan dare.

Alhamdu lillahi, ba a yin azumi da dare, falalar sallar nafila ce kaɗai za ki rasa, amma duk sauran ibadu idan kika yi, za ki dace da lada da falalar su kamar yadda kowa yake samu. Don haka ki dage da addu'a, karatun alƙur'ani, istighfari, salatin Annabi , sadaka da duk sauran ababen da maras haila ke yi, ban da sallah da saduwa da iyali a wannan dare. Dalili kuwa shi ne haka Annabi sallallahu alaihi wa sallama ya ce da Nana Aisha lokacin da haila ta zakke ma ta, a daidai lokacin da ta ɗauki harami domin gabatar da aikin Hajji da Umrah, sai ya ce ta aikata duk abin da duk mahajjaci yake aikatawa ban da ɗawafi ɗoriya a kan ababen da suka haramta ga mai haila.

 

فَدَخَلَ عَلَيَّ النَّبِيُّ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ وَأَنَا أَبْكِي فَقَالَ: ((مَا يُبْكِيكِ)). قُلْتُ لَوَدِدْتُ وَاللَّهِ أَنِّي لَمْ أَحُجَّ الْعَامَ. قَالَ: ((لَعَلَّكِ نُفِسْتِ)). قُلْتُ نَعَمْ. قَالَ: ((فَإِنَّ ذَلِكَ شَيْءٌ كَتَبَهُ اللَّهُ عَلَى بَنَاتِ آدَمَ، فَافْعَلِي مَا يَفْعَلُ الْحَاجُّ، غَيْرَ أَنْ لاَ تَطُوفِي بِالْبَيْتِ حَتَّى تَطْهُرِي)).

 

A taƙaice dai haila ba za ta hana maki dacewa da falalar daren lailatul ƙadri ba, rashin aiki ne zai hama maki samun falalar wannan daren, kamar yadda ya gabata, za ki iya yin duk sauran ibadu ban da sallah a wannan daren, Allah ya datar da mu da wannan dare da kuma aikata alkhairi.

WALLAHU TA'AALA A'ALAM.

 Amsawa:

 Malam Aliyu Abubakar Masanawa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/Fc3hX6HoDt65aKhhKOiDpX

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments