FA’IDARTA GA MAI BAYARWA
Zakka tana da amfani ga wanda ya fitar da ita ta fuskoki kamar haka:
1• Tana koyawa mai fitar da ita kyauta, ta fitar masa da rowa daga cikin zuciyarsa.
Wato zai koyi yin kyauta ya bar
rowa, rowa mummunar ɗabi’a ce wacca ke cutar da mai yin ta.
ALLAH {SW.T} ya ce:
Duk wanda aka kareshi daga rowar
kansa, to waɗannan su ne masu rabauta.
Manzon ALLAH {s.a.w} ya ce:
Ku kiyayi rowa, hakiƙa
waɗanda suke gabaninku sun halaka ne ta
hanyar rowa.
[Abu Dauda ne ya rawaito shi].
2• Tana fitar da mai bayar da ita daga ƙangin bautawa dukiya, izuwa mallakarta.
Domin duk wanda zai tara dukiya amma ba zai iya bayar da ita ba, to bauta
mata yake yi.
Ita, ta mallake shi, bashi ya mallake ta ba.
Manzon ALLAH {sa.w} ya yi addu’a mummuna ga wanda abin duniya ya tsokane
masa ido, kamar haka:
Bawan dinare ya halaka, da bawan dirhami, da bawan riga ko mayafi, ALLAH Ya
tuntsurar dashi ta fuska.
ALLH ya tuntsurar dashi ta ka,
Kai idan ma ya taka ƙaya,
kada ALLAH ya sa ta fita.
[Bukhari ne ya rawaito].
3• Tana koyawa mai bayar da ita godiyar ALLAH a aikace.
Domin idan bawa ya sarrafa ni’imar
da ALLAH ya yi masa ta umarninsa to shi ne ya yi godiya a aikace.
Idan har mawadaci zai dubi halin da matalauci ke ciki amma yaƙi taimaka masa, to babu shakka bai gode wa ALLAH ba.
4• Yakan sami ƙaruwar
dukiyarsa,
Za ta yi albarka sosai ta zarce har ‘ya’ya da jikoki, wannan ita ce babbar
albarka, kuma alkhairinta yana tafiya har lahira.
Kada kuma mu manta cewa ALLAH ya yi rantsuwa da cewa idan muka gode masa
zai ƙara mana.
5• Yakan sami soyayya da ƙauna
daga mutane.
Domin duk mai taimakawa mutane yana tare da samun ƙaunarsu.
FA’IDA GA MASU KARƁARTA
Zakkah tana da fa’idoji masu yawa ta ɓangaren masu karɓarta.
Daga ciki akwai:
1• Wanda ya sami zakka, yadda ya kamata a bayar da ita, wato yadda ALLAH
yace a bayar da ita, za ta fitar dashi daga talauci ko bauta ko bashi.
2• Tana tsarkake zuciyar matalauta daga yin hassada ga mawadata, da jin ƙiyayya da ƙyashi
a garesu.
3.• Tana ƙara mutunci da
kuzari ga wanda ya karɓeta.
Domin tsananin talauci yakan kawar da waɗannan
suffofi daga mutane.
Musamman ma a wannan zamani da muke ciki.
ALLAH ka ba mu ikon aiki da abin
da muka karanta.
ALLAH ka gafarta mana zunubanmu baki ɗayanmu Ameen.
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.