Yabbata cewa ana ɗaure shaiɗanu a lokacin da Ramadan ya shigo, amma ana ɗaure manya-manyan shaiɗanu ne, ana ƙyale kananu.
Hakan ya sa idan mace tana da iska a jikinta koda a lokacin Ramadan ne suna iya tashi, saboda shi wannan Aljanin dake jikinta ƙaramin shaiɗani ne, ba babba ba,baya daga cikin wamda ake ɗaurewa.
Haka kuma idan kana sallah za ka
ji ba ka rabuwa da wasi-wasin shaiɗan, to suma waɗannan
shaiɗanun da suke zuwa suna sakawa mutum
tunani a cikin sallah ba aɗauresu, saboda suma ƙananun shaiɗanu ne.
Su dai waɗannan ƙananun shaiɗanun su ne suke
haddasa rigima tsakanin mijin da mata a cikin watan Ramadan harma akai ga
mutuwar aure.
Su ne waɗanda suke hana mutune zagewa a kan ayyukan
alkhairi a cikin watan Ramadan, su rinƙa
sawa mutane kasala, kuma suke jefawa mai Azumi sha'awa harma wani yakai ga
karya Azuminsa.
Su ne malaman tsubbu ke amfani da su a cikin watan Ramadan, sai suce ai
Ruhanai ne, to ai duk Aljanin da mutum zai kirashi ya zo kuma ya sa Aljanin
aiki ya yi koda musulmi ne Aljanin, to baya tsoron ALLAH shaiɗani
ne, domin kuwa Aljani mai tsoron ALLAH baya amsa kiran kowa inba na ALLAH ba.
Su ne waɗanda idan da mace ko namiji zai kwanta
bacci da rana ko dare a cikin Ramadan, sai ya zo masa da siffar mace ko namiji,
taganta ana saduwa da ita, to wannan mai saduwa da mutum a cikin baccinsa shi
ma ƙaramin Aljanine.
Su ne wanda inda za ka shiga banɗaki babu addu'a
zai iya shiga jikinka ya rinƙa
cutar dakai, manyan shaiɗanun Aljanu basa zama a banɗaki
sai ƙananu, su kuwa ƙananun shaiɗanun ba aɗauresu
cikin Ramadan.
Don haka zamu ga koda a cikin watan Ramadan ana saɓawa
ALLAH, sai dai ba kowa ba, saboda su manyan suke umartar ƙananun da tunzura mutane a kan saɓon
ALLAH,.
Su manyan su ne suke shan jinin mutum kona dabba, suke sawa ana zubar da
jini, ana kashe rayuka, shiysa idan Ramadan ya zo ake samun sauƙin kashe-kashen rayuka, hatta ƴan ta adda sukan saurara sai bayan Ramadan, saboda manyan
shaiɗanun dake shan jini an ɗauresu,
dama kuma su ne ke tunzurasu su kashe rayuka.
Amma da zarar an ɗauresu, suma ƙananun Aljanun ba su samun ƙwarin gwiwa sosai, sai dai suna zuwa su sawa mai sallah
was-wasi damai karatun Alƙur'ani
su sashi hamma dssr.
Don haka kada mu shagaltu da wasa da
azhkar na neman tsarin ALLAH daga shaiɗanun Aljanu da
mutane ko da a cikin Ramadan ne.
ALLAH ka kare mu daga sharrin
shaiɗan babba da ƙarami.
ALLAH ka gafarta mana zunubanmu baki ɗayanmu Ameen.
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.