Kulafa'ur rashiduna
Zana wake sai ku auna
Don ku gane dai batuna
Ba da wasa zana yo ba
Sirikin Manzo Sadiƙu
Ko Abubakari Atiƙu
Baba ga uwar unuƙu
Aisha ce ainu haƙƙu
Walla zargi ba ga ke ba
Shi Badaɗi ne na Manzo
Ko a Ƙur'ani
fa ya zo
Sahibi mai jure ƙwazo
Ko a kowasshe da ya zo
Bai sake da Munafukai ba
Ya yi limancin Musulmi
Tun gabanin za ta yaumi
Ta wafatin Al-hakimi
Wa siraɗal mustaƙimi
Ba a sam wani yai hakan ba
Ko a can gun Isira'i
Sanda anka yi yo nida'i
Ga Imamul Anbiya'i
Muryarsa ya yo sama'i
Ga waninsa ba ai hakan ba
USMAN IBRAHIM BULANGU
09064862386
0 Comments
Post your comment or ask a question.