𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum, malam ina da tambaya, Don Allah idan
mace ta yi ɓarin ciki na wata biyu wannan jinin ya zama na ciwo ko za
ta daina azumi da sallah ?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikum assalam
To dan'uwa wannan jini ba zai hana sallah da azumi ba, saboda ba jinin haihuwa
ba ne, malamai suna cewa : duk cikin da ya zube kafin a busawa yaro rai, to ba
zai hana sallah da azumi ba, ana busawa yaro rai idan ya kai watanni huɗu a ciki, kamar
yadda hadisin Ibnu Mas'ud, wanda Bukhari da Muslim suka rawaito ya nuna Hakan,.
Saboda haka duk cikin da ya zube kafin haka, to jininsa,
ba zai hana sallah ba, ba zai hana azumi ba, amma mutukar an busawa yaro rai ko
kuma halittarsa ta fara bayyana, to za’a bar sallah da azumi.
Allah ne mafi sani.
DR. JAMILU YUSUF ZAREWA
Ku Kasance Damu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa Tare
Da Fadakarwa a Sunnah.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/K1yƘoPioh30H8XeBGg4iPF
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
No comments:
Post a Comment
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.