𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum malam Dan Allah meye alamomin lailatul ƙadar da falalarsa kuma Ya ake gane daren lailatul ƙadri?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus Salaam Warahmatallahi Wabarkatahu
Allah ﷻ ya fifita wani dare a cikin watan Ramadan ya ba shi wata
daraja da ɗaukaka ta musamman, kuma ya keɓance shi da wata
falala ta musamman wadda bai bawa sauran darare ba, wannan kuma zaɓi ne da ganin dama
ne daga gare shi maɗaukakin sarki, domin yana yin abin da ya ga dama a cikin
halittarsa.
Allah ya ce, “Daren Lailatul Ƙadari ya fi
wata dubu alheri” (Alƙadri : 3).
Ma’ana aiki a cikin wannan dare ya fi aikin wata dubu ba
a daren Lailatul Ƙadari ba.
Allah Mai Girma Da Buwaya ya ce, “Aminci ne a cikinta har
zuwa ɓullowa alfijir”.
(Alƙadri : 5)
Ma’ana dukkan wannan dare alheri ne, babu wani sharri a
cikinsa tun daga farkonsa har zuwa ɓullowa alfijir.
Dare Ne Mai albarka. Allah Ya ce, “Haƙiƙa mun saukar da shi a cikin dare mai
albarka. Haƙiƙa mu masu gargadi ne”. (Addukhan : 3).
Abdullahi dan Abbas ya ce, “Yana nufin daren lailatul Ƙadri”.
A Cikinsa Ne Aka Saukar Da Alkur'ani. Allah ya ce “Haƙiƙa Mun saukar da shi a cikin daren
Lailatul Ƙadri” (Alƙadri : 1).
A Cikinsa Ake Ƙaddara Dukkan Abubuwan Shekara, Allah
ya ce, “A cikinsa ake rarrabe kowanne lamari abin hukuntawa”
(Addukhan : 4).
Allah ya ɓoye wannan dare don musulmi ya yi ƙoƙari da himma a goman ƙarshe ta
Ramadan, musamman ma a dararen da suke mara, waɗanda su ne daren
21, 23, 25, 27, 29, saboda faɗin Manzon Allah ( صلى الله عليه وسلم ) “Ku kintaci daren Lailatul Ƙadri a
cikin marar goman ƙarshe ta Ramadan” [Bukhari da Muslim ne
suka rawaito shi].
Wasu malamai sun yi bayanin cewa daren Lailatul Ƙadri yana yawo a tsakanin waɗannan darare (Wata
shekarar wannan, wata shekarar wancan) saboda a yi aiki da dalilan da suka zo a
kan haka baki ɗaya.
1 – Dare Ne Mai Haske, Babu Zafi Ko Sanyi A Cikinsa. An
karbo daga Jabir ɗan Abdullahi – Allah ya yarda da shi – ya ce, “Haƙiƙa ni an nuna min daren Lailatul Ƙadri, sannan an mantar da ni shi, yana goman ƙarshe na Ramadan, dare ne babu sanyi ko zafi a cikinsa,
kuma mai haske ne, ba zafi ba sanyi (mai cutarwa a cikinsa)” [Ibn Khuzaima ne ya rawaito shi].
2 – Rana Tana Fitowa Da Safiyar Daren Fara Tas Ba Haske
Tare Da Ita. Yayin da aka tambayi Ubayyu dan Ka’abu – Allah ya yarda da shi – a
kan alamomin daren Lailatul Ƙadri, sai ya ce, “Alamar da Manzon
Allah ( صلى الله عليه وسلم ) ya ba mu labari
ita ce, rana tana ɓullowa a wannan rana babu haske tare da ita” [Tirmizi ne
ya rawaito shi].
Manzon Allah ( صلى الله عليه وسلم ) ya ce, “Wanda ya yi tsayuwa daren Lailatul Ƙadri yana mai imani da neman lada, an gafarta masa abin
da ya gabata na zunubansa” [Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi].
An karbo daga Aisha – Allah ya yarda da ita – ta ce, na
ce, ya Rasulallahi, idan na dace da daren Lailatul Ƙadri, me
zan yi addu’a da shi? Sai ya ce, ki ce;
اللّٰهُمَّ إِنَّكَ عَفُوٌّ تُحِبُّ الْعَفْوَ فَاعْفُ عَنِّيْ
“Allahumma Innaka
Afuwwun Tuhibbul Afwa Fa’afu Anni*”
Ma’ana “Ya Allah kai mai afuwa ne, kana son afuwa, ka yi
min afuwa” [Tirmizi ne ya rawaito shi].
Allah ne mafi sani.
Daren Lailatul Qadri
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum malam Dan Allah
meye alamomin lailatul qadari da falalarsa kuma Ya ake gane daren lailatul
qadri?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus Salaam
Warahmatallahi Wabarkatahu
Allah ﷻ ya fifita wani dare a
cikin watan Ramadan ya ba shi wata daraja da ɗaukaka
ta musamman, kuma ya keɓance
shi da wata falala ta musamman wadda bai bawa sauran darare ba, wannan kuma zaɓi ne da ganin dama ne daga
gare shi maɗaukakin
sarki, domin yana yin abin da ya ga dama a cikin halittarsa.
Allah ya ce
لَيْلَةُ الْقَدْرِ خَيْرٌ مِّنْ أَلْفِ شَهْرٍ
“Daren Lailatul Qadari ya fi wata dubu
alheri” (suratul qadri aya ta 3).
Ma’ana aiki a cikin wannan dare
ya fi aikin wata dubu ba a daren Lailatul Qadari ba.
Allah Mai Girma Da Buwaya ya ce
سَلَامٌ هِيَ حَتَّىٰ مَطْلَعِ الْفَجْرِ
“Aminci ne a cikinta har zuwa ɓullowa alfijir”. (Suratul
Qadr Aya ta : 5)
Ma’ana dukkan wannan dare alheri
ne, babu wani sharri a cikinsa tun daga farkonsa har zuwa ɓullowa alfijir.
Dare Ne Mai albarka. Allah Ya ce
إِنَّا أَنزَلْنَاهُ فِي لَيْلَةٍ مُّبَارَكَةٍ ۚ إِنَّا كُنَّا مُنذِرِينَ
“Haqiqa mun saukar da shi a cikin dare mai
albarka. Haqiqa mu masu gargadi ne”. (Suratul Dukhan Aya ta 3).
Abdullahi Ɗan Abbas ya ce, “Yana nufin daren lailatul
Qadri”.
A Cikinsa Ne Aka Saukar Da
Alkur'ani. Allah Yace
إِنَّا أَنزَلْنَاهُ فِي لَيْلَةِ الْقَدْرِ
“Haqiqa Mun saukar da shi a cikin daren
Lailatul Qadri” (suratul qadr aya ta 1).
A Cikinsa Ake Qaddara Dukkan
Abubuwan Shekara, Allah ya ce
فِيهَا يُفْرَقُ كُلُّ أَمْرٍ حَكِيمٍ
“A cikinsa ake rarrabe kowanne lamari abin
hukuntawa” (suratul Dukhan Aya ta 4).
Manzon Allah Sallallahu alaihi
Wasallam ya kasance yana ƙara ɗamara
a goman karshe, yana raya dukkan dararrakinsa, kuma yana tada iyalansa.
Wanda ya tsayu ma wannan dare
yana mai imani mai neman lada an gafarta masa zunubansa da suka gabata (Bukhary
da Muslim).
Allah ya ɓoye wannan dare don musulmi ya yi qoqari da
himma a goman qarshe ta Ramadan, musamman ma a dararen da suke mara, waɗanda su ne daren 21, 23,
25, 27, 29, saboda faɗin
Manzon Allah ( صلى الله عليه وسلم ) “Ku kintaci daren
Lailatul Qadri a cikin marar goman qarshe ta Ramadan” [Bukhari da Muslim ne
suka rawaito shi].
Wasu malamai sun yi bayanin cewa
daren Lailatul Qadri yana yawo a tsakanin waɗannan
darare (Wata shekarar wannan, wata shekarar wancan) saboda a yi aiki da dalilan
da suka zo a kan haka baki ɗaya.
Dare Ne Mai Haske, Babu Zafi Ko
Sanyi A Cikinsa. An karbo daga Jabir ɗan
Abdullahi – Allah ya yarda da shi – ya ce, “Haqiqa ni an nuna min daren
Lailatul Qadri, sannan an mantar da ni shi, yana goman qarshe na Ramadan, dare
ne babu sanyi ko zafi a cikinsa, kuma mai haske ne, ba zafi ba sanyi (mai
cutarwa acikinsa)” [Ibn Khuzaima ne ya rawaito shi].
Rana Tana Fitowa Da Safiyar Daren
Fara Tas Ba Haske Tare Da Ita. Yayin da aka tambayi Ubayyu ɗan Ka’abu – Allah ya yarda
da shi – a kan alamomin daren Lailatul Qadri, sai ya ce, “Alamar da Manzon
Allah ( صلى الله عليه وسلم ) ya ba mu labari ita
ce, rana tana ɓullowa
a wannan rana babu haske tare da ita” [Tirmizi ne ya rawaito shi].
Manzon Allah ( صلى الله عليه وسلم ) ya ce, “Wanda ya yi
tsayuwa daren Lailatul Qadri yana mai imani da neman lada, an gafarta masa abin
da ya gabata na zunubansa” [Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi].
An karbo daga Aisha – Allah ya
yarda da ita – ta ce, na ce, ya Rasulallahi, idan na dace da daren Lailatul
Qadri, me zan yi addu’a da shi? Sai ya ce, ki ce;
اللّٰهُمَّ إِنَّكَ عَفُوٌّ تُحِبُّ الْعَفْوَ فَاعْفُ عَنِّيْ
Ma’ana “Ya Allah kai mai afuwa
ne, kana son afuwa, ka yi min afuwa” [Tirmizi ne ya rawaito shi].
Yan uwa! Wannan addu'ar ita za mu
yawaita yi a cikin Wadannan kwanaki goma har mu dace da lailatul Qadr in shaa
Allah, Addu'a ce da sunnah ta koyar.
Wanda Allah Yasa ya dace da
wannan dare, to ya yawaita Ibada da Addu'a, Karatun Alkur'ani.
Allah ya datar damu da dukkanin
alkhairin da ke cikin wannan dare mai albarka Allah ya bamu ikon lizimtar ta.
WALLAHU A'ALAM
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/CƘ9TMXMrWDx1y7sYye2znU
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.