Ticker

6/recent/ticker-posts

Raya Wasu Dararraki Cikin Goman Karshe Ba Tare Da Wasu Ba

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Wasu cikin mutane suna raya daren lailatul ƙadr (ranakun da a ke sa ran lailatul ƙadr) da salloli da ibadu, amman ba sa raya wasu dararrakin da ba wannan ba a ramadan din. shin hakan ya dace da daidai?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

A'a bai dace ba, domin daren lailatul ƙadr na caccanzawa, ta yiwu ya kasance a daren 27, ta yiwu kuma ya kasance a wani daren da ba wannan ba, kamar yanda hadisai da dama su kayi nuni a kan hakan. Sannan shi tsayuwan dare ba ya halatta ga mutum ya keɓanceshi da daren da ya ke fatan ya kasance lailatul ƙadr, dagewa da tsayuwa a duka dararrakin ƙarshen duk yana cikin koyarwan Annabi tsira da aminci su tabbata agareshi.

Abin da yake kamata ga Mumini mai ƙwazo shi ne ya dage ya raya duka goman saboda kar lada ya kubuce masa.

Shaykh Muh'd Saleh Al'uthaimeen

RAYA WASU DARARRAKI CIKIN GOMAN QARSHEN RAMADAN BA TARE DA WASU BA

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Wasu cikin mutane suna raya daren lailatul qadr (ranakun da a ke sa ran lailatul qadr) da salloli da ibadu, amman ba sa raya wasu dararrakin da ba wannan ba a ramadan ɗin. shin hakan ya dace da daidai?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

A'a bai dace ba, domin daren lailatul qadr na caccanzawa, ta yiwu ya kasance a daren 27, ta yiwu kuma ya kasance a wani daren da ba wannan ba, kamar yanda hadisai da dama su kayi nuni a kan hakan.

Sannan shi tsayuwan dare ba ya halatta ga mutum ya keɓanceshi da daren da ya ke fatan ya kasance lailatul qadr, dagewa da tsayuwa a duka dararrakin qarshen duk yana cikin koyarwan Annabi tsira da aminci su tabbata agareshi.

Abinda ya kamata ga mumini mai qwazo shine ya dage ya raya duka goman saboda kar lada ya kubuce masa.

Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam ya kasance yana ƙara ɗamara a goman karshe, yana raya dukkan dararrakinsa tare da iyalansa.

Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam ya tabbatar da cewa za a dace da daren nan na Laylatul Qadr mai albarka a cikin ‘yan kwanakin nan na 10 na karshen watan Ramadan inda ake kasafin duk wani alheri a shekarar.

Ibada a cikin daren kamar yadda ya zo a Al-kur’ani cikin Suratul Qadr ya zarce ibada har na watanni dubu wanda idan aka lissafa zai bada kusan shekaru 84. Manzon Allah (Sallallahu alaihi Wasallam) ya nemi a lalubi daren a cikin kwanaki na mara watau daren 21, 23, 25, 27 da kuma daren azumi na 29.

Manzon Allah (Sallallahu alaihi Wasallam) yayi umarni da cewa anemi wannan dare mai albarka acikin waɗannan kwanaki goman ƙarshen, hakanan kuma yayi umarni da anemeta acikin bakwai ɗin ƙarshe, kamar yadda hadisin Sahabi Ibnu Umar Allah ya ƙara yarda dashi ya nuna, wannan duka cikin hikima ta manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ne domin ƙara sauƙaƙawa Al'ummarsa wurin riskar wannan dare mai tarin albarka.

WALLAHU A'ALAM

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/DSdbBS8RZVoIKYG5exOuZE

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments