Ya halatta a shariah mace ko mijinta su yi wasa da bakinsu a farji kafin saduwa, sai dai ya wajaba a tabbatar an tsaftace wurin musamman farjin mata, saboda yadda ALLAH TA'ALAH ya yi musu tasu halittar.
Domin kuwa guri ne da ake yin haila, ake kuma zuba
maniyyi, gashi kuma yana kusa da wajan yin bahaya, wasu masana likitanci suna
bada shawarar cewa: a rinƙa wanke gurin da gishiri kafin
a tsotsa, saboda neman kariya.
ALLAH TA'ALAH a cikin suratul Baƙara ayata: 223, ya kwatanta mace ga mijinta da gona, wannan
sai ya nuna dukkan ɓangarorin jikinta ya halatta
aji dadi dasu, in ban da cikin dubura wacce nassi ya togace.
Duba: Mawahibul-jalil 3\406.
ALLAH shi ne mafi sani.
ALLAH ka gafarta mana zunubanmu Ameen.
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.