𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamou aleikoum, malam, ina cikin matsanantcin tashin hankali, ALLAH ya jarabche ni ina gani kamar saɓon da nake Ciki ne ALLAH ya jarabche ni da hakan, na bi hanyoyi da yawa dan neman mafita har da malaman tsibbu amma abun se kara chittira yake, shin malam idan na koma ga ALLAH, ALLAH zai karɓa min? Dan Na ji wani malami na cewa matukar bawa be yi hankuri ya meda al-amarinsa ga ALLAH tun da farko, idan se da ya yi iya iyawarshi ya kasa samun biyan bukata, to wai ALLAH ba ya karɓar irin wannan adou'a?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus
salam, ‘yar
uwa Allah mai gafarta wa bawansa dukkan zunubansa ne matuƙar ya
nemi tubar, duk yadda zunuban mutum suka kai wurin yawa, idan bawa ya nemi
gafarar Allah, to Allah zai gafarta masa waɗannan
zunubai, ko da shirka bawa yake yi, idan har ya daina kuma ya tuba cikakkiyar
tuba kafin ya mutu, to lallai ana fatan Allah zai gafarta masa wannan shirka ɗin, matsalar ita ce idan
har mutuwa ta riski mutum yana shirka kafin ya tuba, Allah Ta'ala a wurare
mabambanta a Alƙur'ani ya ce:
"Ka faɗa masu (ya Manzon Allah) Ya
ku bayina waɗanda suka
aikata wa kawunansu zunubai, kada ku ɗebe
tsammani da rahamar Allah, lallai Allah yana gafarta zunubai baki ɗaya, lallai shi Mai gafara
ne mai jin-ƙai".
Suratuz Zumar: 53.
A wani wurin
kuma ya ce:
"Shi ne
Mai karɓar tuba daga
bayin sa, kuma yana share munana, ya kuma san abin da kuke aikatawa".
Suratus Shúra: 25.
Sannan kuma
shi ne ya ce: "Shin ba za su tuba zuwa ga Allah su nemi gafararsa ba,
Allah mai gafara ne mai jin-ƙai". Suratul Má'ida: 74.
‘Yar
uwa dukkan waɗannan
ayoyi suna nuna cewa idan bawa ya tuba zuwa ga Allah, lallai Allah zai gafarta
masa waɗannan zunubai
nasa, duk yadda ko zunuban nasa suke wurin yawa da muni, babban abin da ya dace
ki yi shi ne ki tuba zuwa ga Allah bisa bin hanyar ‘yan tsibbu da kika ce kin
yi domin neman biyan buƙatunki, saboda harka da ‘yan tsibbu hanya ce ta zuwa Jahannama kai
tsaye.
Kuma ki yi
dauwamammiyar nadama a kan wannan babban laifi, ki ɗaura niyar ba za ki sake aikata wani laifi
makamancin wannan ba, tare da yawaita yin istigfári, lallai idan kika yi hakan
in Allah ya so duk Allah zai share maki waɗannan
laifuka, saboda Allah ya kasance mai share munana da tabbatar da kyawawa ne,
kuma ya kasance mai tsananin tausayi da jin-ƙan bayin sa ne, mai karɓar tubarsu ne a duk lokacin
da suka nemi tubar. Hakan ya sa na fi tunanin wata ƙila ke ce ba ki fahimci
abin da wancan malami yake nufi ba.
Allah S.W.T ne
mafi sani.
Jamilu Ibrahim
Sarki, Zaria.
Ga Masu Buƙatar
Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin
mu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/K7RkƘRMf2b57l3UENoJ1Or
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.