𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Aslm malam.
Dan Allah Ina so na ji falalar sitta shwwal. Wannan shi ne tambaya ta.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Azumin shittu
shawwaal Mustahabbine Sunnah ne da'akeson mutum ya daure ya aikata, saboda
akwai falala mai girma a cikin azumtar kwanaki shida na watan shawwal, da kuma
lada Babba, wanda ya azumta za a rubuta masa ladan azumin shekara guda, kamar
yanda ya tabbata daka Annabi Sallallahu Alaihi wasallam kamar yanda yazo a cikin
hadisi Abu Ayyubar Ansary Allah yaƙara yarda da shi ya ce: (Wanda ya Azumci
watan ramazhaan sannan yabi bayansa da Azumin kwanaki shida na watan shawwal kamar
ya azumci zamani guda ne.
Muslim, Abu
Dauda, Turmuzy, Nisa'i, Ibnu Majah
Annabi
Sallallahu Alaihi wasallam ya fassara wancan hadisin da fadinsa ya ce: { Wanda
ya Azumci kwana shida na watan Shawwal bayan ƙaramar Sallah, ya kasance cikwan shekara (Wanda
ya aikata kyakkyawan aiki yanada lada goma na kwatan-kwacinsa) Awata ruwayar
Allah yana maida ladan kyakkyawan aiki da goma irinsa, watan Ramaḍān
yana amatsayin watanni Goma, Azumin kwanaki shida na watan Shawwaal sune cikwan
shekara.
"Nisa'i
da Ibnu majah, hadisin yana cikin #Saheehu Targeeb wattarheeb, (1/421) ibnu
kuzaima ya ruwaitoshi da lafazin [ Azumin watan Ramaḍān yana dai-dai da goma
irinsa,
Azumin sittu
shawaal yana dai-dai da wata biyu, inka haɗa
yazama azumin shekara guda.
Daga cikin
fa'idojin masu muhimmanci na Azumtar Sittu shawwaal shi ne cike gibin tawayar
data faru a cikin Azumin farillah na Ramaḍān, saboda mutumba ya kubuta daka
gajiyawa ko aikata zunubi wanda zai tasiri a azuminsa, ranar ƙiyama
za a dauka daka ayyukansa na nafila acike masa gibin daya bari na tawayar
ayyukansa na wajibi.
Kamar yanda
Annabi Sallallahu Alaihi wasallam ya ce: Farkon Abun da za a fara yiwa ɗan Adam hisabi a kansa
ranar Alƙiyama
daka cikin Aikinsa shi ne Sallah, Allah zai cewa mala'ikunsa kuduba kuga bawana
yana da wani aikin na nafila, idan yanada nafila sai ya ce: kucikewa bawana
gibin daya samu a aikinsa na farillah da aikinsa na nafila, sannan sai aci gaba
da karbar sauran ayyuka a kan hakan.
Abu dauda.
Ataƙaice
azumin Sittu shawwal akwai hikimar Allah wajan shar'antashi, Sannan yanada
fa'idoji masu tarin yawa.
WALLAHU
A'ALAM.
Ga Masu Buƙatar
Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin
mu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/IƘUc0RxgCwA3JFiEKl8j5E
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.