𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum
Malam ni ce na haihu toh sai na yi wanka na fara ibada
sai jini ya dawo har yadauke na fara ibada sai nazo nagan shi ɗan kaɗan wanda bekai ya
stain pant ba amma kuma jini ne jajur nagani da asuba sai bangane ba, kuma ya
hukuncin azumi na kuma mene ne kayadadden lokacinsa don nakai kwanaki 40.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Walaikumus salamam
Idan mace ta haihu Jini yakan zo mata a dalilin haihuwa.
Wannan jinin shi ake kira Nifaas (Jinin biƙi), ita
kuma macen ita ake kira Nufasa'u (Mai jinin biƙi), idan
mace na cikin jinin haihuwa, toh baza ta yi sallah ko azumi ba, kuma mijinta
bazai zo mata ba har sai ta samu tsarki ko ta cika adadin kwanakin jinin
haihuwa, adadin kuwa shi ne kwanaki 40.
Imam Tirmizi (rahimahullah) ya ce: Mutanen ilimi daga Sahabban Manzon Allah (sallallahu alaihi wa
sallam) da tabi'ina da wadanda suke bayansu sun haɗu a kan cewa mace
mai jinin biƙi za ta daina yin sallah da azumi na tsawon kwanaki 40
har sai idan ta samu tsarki kafin cikar kwanaki 40 din. Idan Jini ya dauke
kafin cikar kwanaki 40 toh za ta yi wanka ta yi sallah.
Idan ta ga Jini bayan kwanaki 40, mafi yawan malaman
ilimi sukace bazata daina sallah ba bayan kwanaki 40, za ta cigaba da sallah da
ibaada. Wannan shi ne ƙaulin mafiya yawan malamai. Daga
cikinsu akwai Sufyaan Athuuriy da Ibn Mubaarak da Shafi'i da Ahmad da Ishaaƙ. (Sunan Tirmizi, 1/256).
Malaman Al-Lajnatu al-da'imah lil iftaa'a sunce: Idan
mace ta ga tsarki (Jini ya dauke) kafin cikar kwanaki 40, toh za ta yi wanka ta
yi sallah da azumi kuma mijinta ya zo mata (ya sadu da ita). Idan Jini ya
cigaba da zuwa mata bayan kwanaki 40, toh za ta cigaba da daukar hukuncin
tsarki ne. Saboda kwanaki 40 su ne adadin kwanakin da jinin haihuwa yake hana
ibaada a cikinsu abisa zancen malamai mafi inganci. Jinin da ya zo mata bayan
kwanaki 40 za ta dauke shi a matsayin jinin rashin lafiya kuma yana daukar
hukuncin istihaadha ne. Saifa idan jinin ya zo mata ne a lokacin da ta saba yin
al'adarta.
WALLAHU A'ALAM
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/I08Ƙc4ehEctLMSfks5awuZ
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.