Ticker

6/recent/ticker-posts

Zambo Da Habaici A Cikin Wasu Waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanba’u Gidan Buwai (4)

Habaici suka ce da ake yi kaikaice cikin wasu ɓoyayyun kalmomi na hikima masu ban sha’awa da ban dariya ga mai sauraro tare da cusa haushi da ban takaici da ɓata rai ga wanda ake wa. Habaici ba kai tsaye ake gane da wanda ake ba, sai wanda ya san abin da ke faruwa.

Zambo Da Habaici A Cikin Wasu Waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanba’u Gidan Buwai (4)

 

NA

SHEHU HIRABRI
08143533314

Kayan Kiɗan Hausawa


BABI NA HUƊU

HABAICI A CIKIN WASU WAƘOƘIN ALHAJI MUSA ƊANBA’U GIDAN BUWAI

4.0 Shimfiɗa

        A cikin wannan babi za a yi bayani tare da kawo misalai tun daga asalin kalmar habaici da ma’anarta da ire-irenta da dalilin da ya sa ake yin habaici da amfaninsa tare da yin sharhinsa a cikin wasu waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanba’u Gidan Buwai.

4.1 Asalin Kalmar Habaici

          Ra’ayin masana ya haɗu a kan cewa, asalin kalmar habaici, Bahaushiyar kalma ce wadda za a iya danganta ta da maganganun hikima da azanci da gwaninta da naƙaltar harshe da Hasuawa suka gada tun iyaye da kakanni. Saboda haka ba ta da alaƙa da kowane harshe sai Hausa. Haka kuma ba a iya cewa ga lokaci da aka fara amfani da ita. Hausawa sun taso suna shirya habaicinsu da kansu a cikin waƙoƙi da maganganunsu na yau da kullum. Habaici ya ƙara samun gata ta hanyar makaɗa da mawaƙa da manazarta.

4.2 Ma’anar Habaici

          Malamai masana da manazarta da dama sun bayyana ra’ayoyinsu dangane da ma’anar habaici. Ga wasu daga cikinsu:

          Ɗangambo, (1984: 42) cewa ya yi: “Habaici magana ce mai ɓoyayyiyar manufa, ba kasafai akan gane da wanda ake ba.”

          Garba, (1998: 18) cewa ya yi: “Habaici magana ce mai ɗaci da Bahaushe ke faɗa a sakaye domin ya sanya dabi’ar gyara kayanka a wanda ba ya zama sauke mu raba.”

          Zaruk da wasu (2005: 47-48) cewa suka yi: “Idan aka ce habaici ko gugar zana duk ana nufin abu ɗaya ne. Habaici shi ne yi da mutum a kaikaice. Habaici ya fi yawa inda kishi yake ko ƙyashi. Galibi mutane suna ɗauka cewa habaici salon mata ne, dalili kuwa shi ne a tsakanin mata kishi da gasa da ganin ƙyashi suka fi yawa. Duk da haka za a iya cewa habaici ana samun sa a mata ana kuma samun sa a maza. Wasu maza idan suna gaba ko ta sana’a ko ta wani abu na cigaba sukan yi wa juna habaici.

          Dunfawa, (2005: 20) cewa ya yi: ‘Habaici na nufin faɗa wa wani ko wasu aibin wani abu da suka yi, ko suke yi a fakaice ba tare da ambaton suna ko siffanta wanda ake yi wa ba wato ta yadda za ta sa a gane shi.”

          Ƙamusun Hausa, (2006: 187) cewa ya yi: “Habaici na nufin suka mutum a fakaice ta hanyar magana.”

Yahaya, da wasu (2006: 42) cewa suka yi: “Habaici kalmomi ne da ake amfani da su a fakaice don muzanta mutum. Shi ma zance ne na hikima da ake amfani da shi a yi da mutum a kaikaice. A wajen yin habaici ba a kan fito fili a bayyana wanda ake nufi ƙuru-ƙuru ba, sai dai akan yi amfani da wasu kalmomin sakaya kamar wanga ko wagga ko su wane da makamantansu.”

          Ɗanhausa, (2012: 13) cewa ya yi: “Habaici magana ce da ake yi cikin hikima da nufin gaya wa wani saƙo amma ba kai tsaye ba, a fakaice wato a ɓoyayyar manufa. Akan yi magana da nufin wani abu da ake yi domin shi, amma shi habaici idan ba mutum ya san kan zance ba, ba kasafai yake gane wanda aka yi habaicin domin shi ba.”

          Yahya, da wasu (2015: 75) cewa suka yi: “Habaici yana nufin magana ce mai ɗaci da Bahaushe ke faɗa wa ɗan uwansu a sakaye domin ya sanya shi ya gyara wani mummunan halinsa ko kuma domin faɗakarwa ga ‘yan uwa kowa ya shiga taitayinsa ko kuma kawai don ba da haushi.”

          Yahya da wasu (2016: 218) cewa suka yi: “Habaici wani nau’i ne na zancen hikima da ake amfani da shi a yi da mutum a fakaice don ɓata wa wani mutum rai ko yi masa ƙaimi da kuzari ko yi masa faɗakarwa, ba tare da bayyana mutumin da ake nufi ƙuru-ƙuru ba, amma shi wanda ake nufi wani lokaci zai gane, sai dai sauran jama’a da wuya su fahimta idan ba wanda ya san abin da ake ciki ba.”

          Ta la’akari da ma’anonin da malamai masana da manazarta suka bayar, a tawa fahimta ana iya cewa: Habaici suka ce da ake yi kaikaice cikin wasu ɓoyayyun kalmomi na hikima masu ban sha’awa da ban dariya ga mai sauraro tare da cusa haushi da ban takaici da ɓata rai ga wanda ake wa. Habaici ba kai tsaye ake gane da wanda ake ba, sai wanda ya san abin da ke faruwa.

 

4.3 Ire-iren Habaici

          A Hausa akwai ire-iren habaici kamar haka:

1.     Habaicin hannunka-mai-sanda

2.     Habaicin gugar zana

3.     Habaicin zagi a kasuwa

4.     Habaici mai karin magana

4.3.1 Habaicin Hannunka-mai-sanda

          Habaici ne da ake yi domin jawo hankalin wani mutum ko nuni kan wani abu da ake so ya lura da shi ko ya gyara ko kuma don a sa mutum ya kama kansa. Misali, a waƙar Ɗanba’u ta D.P.N. inda yake cewa:

Jagora: Ina horon wane,

            Kullum ya kauce ya ƙiya,

            Wane ka bar neman shiga,

            In ‘yan taron daba,

Yara:   siyasar ‘yan gurguzu,

           Ai siyasar ƙeta ce.

 

A wani ɗan waƙar kuma cewa ya yi:

 

Jagora: Ina jin tsoron mutum,

            Mai buƙatar gardama,

            Ban so haka nan ba,

            Wallahi Allah ya sani,

            Ina kallon wane ya kama daji

Yara:  Wane dawo ga hanya,

          Inda kowa ka murna ya hi kyau.

 

Gindi: D.P.N. ta yi daidai,

          Da ‘yan Nijeirya,

          Alheri yanzu kowa,

          Buƙatatai yake.

4.3.2 Habaicin Gugar Zana

          Habaici ne da ya shafi gugar zana. Akan yi shi ne a kaikaice ba tare da fitowa ƙuru-ƙuru ba, ta hanyar faɗin wasu daga cikin ɗabi’un ko halayen mutum ko kuma a yi masa ƙage. Misali a waƙar Alhaji Musa Ɗanba’u ta D.P.N. inda yake cewa:

Jagora: Mu ba duba mukai ba,

            Kuma ba tsafi mukai ba,

            Roƙon Allah mukai,

            D.P.N. dai ta hau,

Yara:   Mazanmu da matanmu,

            Kowa ya zauna lahiya.

A nazarin waƙa, duk inda aka sami irin wannan magana akwai wanda ko waɗanda suke yin abin. Kenan ma’ana masu duba da tsafi. ‘Yan jam’iyar da ke adawa da D.P.N.

A wani ɗan waƙa suke cewa:

Yaro: Mi ar ranak kilinge,

          Ga harka duniya,

          Ko ga shi cikin gida,

Yara: Kyalla shurewa takai,

                           

Jagora: Yanzu ko ga shi cikin gida,

                            Yara:     Kyalla shurewa takai.

 

 

 

Gindi: D.P.N. ta yi daidai,

          Da ‘yan Najeriya,

          Alheri yanzu kowa,

          Buƙatatai yake.

4.3.3 Habaicin Zagi a Kasuwa

          Habaici ne wanda ake yi ta hanyar jefa magana kai tsaye ba tare da nuna wanda ake da shi ba, sai dai kowa zai rasa da wanda ake nufi. Amma a mafi yawan lokuta mai yin habaicin ya san da wanda yake. Shi ne Bahaushe ke cewa: “Kowa ya yi zagi a kasuwa, ya san da wanda yake.” Misali a cikin waƙar Ɗanba’u ta PDP akwai inda yake cewa:

Jagora: “Yan siysa,

    Ku yi hakƙuri,

              Da Musa Ɗanba’u,

              Kun san ku nawa ne,

             Sannan ni naku ne,

             Ko da kun ƙi ni,

             Mai kama ta kuka so,

             In kuka ƙi ni da ɗa,

Yara:    Kun ganan da jika da goya.

 

Gindin Waƙa: Ya ‘yan Nijeriya,

            Siyasa ta tashi,

            Ku dawo mu yi ƙoƙari,

            Mu koma P.D.P.

4.3.4 Habaici Mai Karin Magana

          Habaici ne wanda ake yi cikin sigar karin magana. Ma’ana ana amfani da karin magana wajen bayyana manufar da ake son a bayyana. Misali:

Cin ɗanƙo har da su kaza.

Wani misali a cikin waƙar Ɗanba’u inda yake cewa:

 

Jagora: Na gaya ma mutane,

            Ɗauke dahi sai giwa,

            Maza tahi kauce zomo,

Yara:   Ba ka iya wa kai nan?

 

Gindin Waƙar: Ƙara shirawa,

            Aliyu zaɓaɓɓen gwamna,

            Mai ban tsoro magatakardan Wamakko,

            Sarkin Yamman Sakkwato bai san wargi ba.

 

A wata waƙa kuma yake cewa:

Jagora: Wane bai da kirki sam-sam-sam,

            Ya gama da dum masu biya tai,

            Yanzu babu mai kuɗi sai shi,

            Na ce Allah na gode ma,

Yara:   Da na san bari ba shegiya ba ce.

 

Gindin waƙa: P.D.P. hasken Nijeriya,

           Fati mai ƙarfi da martaba.

4.4 Dalilin Yin Habaici

          Akwai dalilai da dama da ke sa a yi habaici daga ciki akwai:

1.     Bayyana hasada

2.     Huce haushi

3.     Rowa

4.     Tsokanar faɗa

5.     Gargaɗi da hannunka-mai-sanda

6.     Ramuwar gayya

7.     Kishi ko rashin jituwa (Yahaya da wasu 2006: 43).

4.5 Amfanin Habaici

          Duk da kasancewar habaici suka ce da ake yi a kaikaice ta hanyar cin zarafi amma kuma, yana da amfani matuƙa. Daga cikin amfaninsa akwai:

1.     Habaici wata taska ce ta adana adabin Bahaushe.

2.     Habaici wani ado ne na harshe da ke ƙawata waƙa tare da ƙara mata armashi, da kuma zantukan yau da kullum.

3.     Habaici na faɗakar da mutum ta hanyar sanin miyagun ɗabi’u ko ƙazafi ko wani abin da jama’a ke zargin sa da shi.

4.     Habaici na sa mutum ya daina wasu miyagun ɗabi’u ko halaye.

5.     Habaici kan taimaka wajen ƙara soke abokin hamayya.

6.     Habaici na samar da nishaɗi da raha a cikin zukatan jama’a.

7.     Ƙwarewa wajen gina habaici a cikin waƙoƙi musamman na sarauta ko siyasa na ƙara wa makaɗi ɗaukaka da farin jini ga jama’a.

8.     Habaici na hana yin shisshigi watau mutum ya shiga sha’anin da bai shafe shi ba.

9.     Ƙwarewa wajen gina habaici na sa makaɗi ko maroƙi ya samu alheri.

10. Amfani da habaici a cikin waƙoƙi da zantuka na yau da kullum a cikin harshe yana ƙara bunƙasa harshe.

4.6 Habaici A Cikin Wasu Waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanba’u Gidan Buwai

          A sama an kawo ma’anar habaici da ire-irensa da dalilan da ke sa a yi shi tare da bayyana amfaninsa. A nan kuma za a yi sharhin habaici a cikin wasu waƙoƙin Alahaji Musa Ɗanba’u Gidan Buwai.

          Kamar yadda Yahya da wasu (2016: 218) ke cewa: “Habaici wani nau’i ne na zancen hikima da ake amfani da shi a yi da mutum a fakaice don ɓata wa wani mutum rai ko yi masa faɗakarwa ba tare da bayyana mutumin da ake nufi ba, wani lokaci zai gane sai dai sauran jama’a da wuya su fahimta, in ba wanda ya san abin da ake ciki ba.”

          Za a ga irin waɗannan bayanan da Yahya da wasu (2016: 218) suka yi a cikin littafinsu mai suna Alun Nan Dai kan habaici a cikin wasu waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanba’u Gidan Buwai.

A waƙar jam’iyar P.D.P. mai taken:

Ya ‘yan Nijeriya,

Siyasa ta tashi,

Ku dawo mu yi ƙoƙari,

Mu koma P.D.P.

          A cikin wannan waƙar Ɗanba’u ya yi habaici a wurare da dama a cikin ɗiyan waƙa kamar haka:

Jagora: Na yi mamaki wane,

            Don siyasa ta ƙare,

            Shi muddin yag ganan,

            Ya canza man huska,

            Ga siyasa ta dawo,

            Ga mu mu ko mun dawo,

            An ce a haɗe,

            Ba mu buƙata Ɗanba’u,

            Kowa ya tsaya wurinsa,

           A buga a gani,

Yara:  A gane wa zai rinjaye.

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa wani ɗan siyasa habaici ta hanyar wani abin da ya faru tsakaninsu, bayan wucewar siyasa da cewa, duk lokacin da ya gan shi ya canza mai fuska, yanzu kuma siyasa ta dawo, ya kira su ya ce a haɗe, shi ne yake ba shi amsa cewa kowa ya tsaya wurinsa a buga a gani a gane wa zai yi rinjaye. A nan ya kira shi da wane ba wanda zai haƙiƙance cewa ga wanda yake nufi, amma shi wanda ake wa ya sani, da kuma wanda ya san abin da ke tsakaninsu.

A wani ɗan waƙa yake cewa:

 

Jagora: ‘Yan siyasa,

  Ku yi hanƙuri,

  Musa Ɗanba’u,

            Kun san ku nawa ne,

            Sannan ni naku ne,

            Ko da kun ƙi ni mai kamata kuka so,

            In kuka ƙi ni da ɗa,

Yara:   Kun ganan da jika na goye.

          Bayan kammala ɗan waƙar sai Ɗanba’u ya ce: “Abin daga Allah ne.”

A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa wasu ‘yan siyasa habaici waɗanda ke jin haushinsa cewa su yi haƙuri da shi domin ko da sun ƙi shi mai kama tai suka so, in suka ƙi shi da ɗa, sun gan shi da jika ya goya. Ma’ana da su so shi da kar su so shi ba abin da za su iya yi masa. Haka kuma duk abin da za su ba shi ya sami fiye da haka, don haka babu yadda za su yi da shi.

A wani ɗan waƙa yeke cewa:

Jagora: Raƙumi na tafiya,

          Ɗauke da kayanai,

          Ya isko kunama yat taka,

          Naj ji ya buga ihu,

          Ƙasa akwai shaggu,

          ‘Yar abig ga ‘yar tcito,

          Ga shi yanzu ta halban,

Yara: Har na gaza ɗaukar kayan nan.

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa wani ɗan siyasa habaici ta hanyar kwatance. Inda ya kwatanta wani babban ɗan siyasa da raƙumi, da wani ƙaramin ɗan siyasa a matsayin kunama. Inda yake nuna wani babban ɗan siyasa ya faɗa wa wani ƙaramin ɗan siyasa, ƙaramin ya samu gagarumar nasara a kan babban ɗan siyasan. Shi ne yake cewa raƙumi na tafiya ɗauke da kayanai, ya isko kunama ya taka, sai nij ji ya buga ihu ya ce ƙasa akwai shaggu, ‘yar abig ga ‘yar tcito ga shi yanzu ta halban har na gaza ɗaukar kayan nan. A nan za a ga abin a dunƙule yake ba kowa zai iya fahimtar wanda ake nufi ba.

Haka kuma a cikin wata waƙar P.D.P. mai taken:

P.D.P. hasken Nijeriya,

Fati mai ƙarfi da martaba.

A wannan waƙar Ɗanba’u ya yi habaici a ɗiyan waƙa daban-daban kamar haka:

Jagora: Kai ji wane yai tahiyar kura,

          Yana gaba ya koma baya,

          Inda yan nuhwa ba a karɓai ba,

          Ya dawo bai ishe kowa ba.

          Yay yi shiru yar riƙe baki,

          Nac ce duk mai koraj jama’a,

Yara: Sai ya biɗi mai ba shi shawara.

          A wannan ɗan waƙar makaɗin ya yi wa wani ɗan siyasa habaici ta hanyar kiran sa da wane yai tahiyar kura yana gaba ya koma baya inda ya nufa ba a ɗaukai ba ya dawo bai ishe kowa ba. Ma’ana yana cikin jam’iyatai, ya fita ya koma wata jam’iya. Jam’iyar da ya koma ba su karɓe shi ba, ya dawo jam’iyyarsa ta farko suka ƙi karɓar sa. Wai sai ya yi shiru ya riƙe baki yana mamaki, sai yake cewa: “Kowa ke korar jama’a, sai ya biɗi mai ba shi shawara.” Ma’ana duk mai wulaƙanta jama’a sai ya neme su, domin da yana da abokan shawara da haka ba ta faru ba. Nan canza jam’iyya zuwa wata jam’iya ga ‘yan siyasa abu ne wanda ya zama ruwan dare. Don haka zai yi wuya a gane wanda ake nufi kai tsaye, sai waɗanda suka san abin tun farko.

A wani ɗan waƙa yake cewa:

Jagora: Mai ƙarƙarin hawan icen kwakwa,

          Idan ka hwaɗo ka ƙalle,

          Kai cikin dubu nika tona ka,

Yara: Baƙar magana wadda kai muna.

          A wannan ɗan waƙar makaɗin ya yi wa wani ɗan siyasa habaici da cewa mai ƙarƙarin hawan iccen kwakwa, ma’ana mai son shiga jam’iya mai alamar kwakwa. Idan ka hwaɗo ka ƙalle. Ma’ana idan ya shiga jam’iyar, aka yi zaɓe suka faɗi. Kai cikin dubu nika tona ka, ma’ana cikin taron jama’a za su tona mai asiri. Baƙar magana wadda kai muna. A nan ke nan akwai wata shawara da suka ba shi ya ƙi ji har ya yi musu baƙar magna. Shi ne yake yin ƙarin bayani domin wanda suka yi haka ya san da shi ake amma wani ba zai fahimci da wanda ake ba.

A wani ɗan waƙa yake cewa:

Jagora: Ku ji kyanwa mai saurin tafiya,

          Ƙarƙarin takai dai ta ci kifi,

          Dur radda ƙaya tal laƙe miki,

          Yau kowa bai tagaza miki,

          Sai dai ki mace ‘yar damƙon uwa,

Yara: Don mun kula ɓarnarki tai yawa.

          A wannan ɗan waƙar makaɗin ya yi wa wani ɗan siyasa habaici a kaikaice ta hanyar ɓoye sunansa ya kira shi da kyanwa mai saurin tafiya, ƙarƙarin takai ta ci kifi. Ma’ana wani ɗan siyasa ne ke ƙoƙarin shiga wata jam’iya ko kuma tsayawa takara a wata jam’iya. Duk rad da ƙaya ta laƙe miki yau kowa bai tagaza miki, ma’ana dur randa aka yi zaɓe ya faɗi ko suka faɗi ƙarya tai ƙare domin kowa bai taimaka masa sai dai ya mace, domin rashin kunyarsa ya yi yawa. A nan sai dai hasashe kawai ga mai saurare amma ba za a iya cewa ga wanda ake nufi ba. Don haka habaici ya amsa kirarinsa cewa habaici masu faɗa kowa amsa da shi ake.

A waƙar Tanimu Ɗangaladiman Kyaɗawa mai taken:

Dogo kana da shirin Yaƙi,

Tanimun na Alhaji Yakubu.

A wannan waƙar Ɗanba’u ya yi habaici a ɗiyan waƙa daban-daban kamar haka:

Jagora: Ni munahukin Gada na san shi,

          Don baƙin jininai ya yi yawa,

          Ɗazu ya wuce mu muna hira,

          Sai nij ji yara suna ihu,

          Wada nij ji ana karɗa-karɗa,

          Nac ce gudun ga na aura ne,

Yara: Shi bai yawo a cikin Gada,

          Kuma bai shiri da maƙwabtansa.

          A wannan ɗan waƙa Ɗanba’u ya yi wa wani mutum habaici ta hanyar gugar zana inda ya fito da wasu ‘yan halayensa a kaikaice ta yadda ba a iya gane wanda ake nufi kai tsaye, sai ya danganta shi da yadda mutane ke gudun munafuki da yadda kare ke samun barazana ga yara, idan sun haɗu. Don haka shi munafuki za a ga ba a cika yarda da shi ba, kuma mutane ba su ra’ayinsa.

A wani ɗan waƙa suna cewa:

Yaro: Kowa da abin da yake sauna,

          Kowa da abin da yake tsoro,

          Kusu kyanwa yaka jin tsoro,

Jagora/Yara: In ga kura a cikin gari,

          Aura ba za ya hitowa ba.

Jagora: A in ga kura a cikin gari,

          Aura ba za ya hitowa.

          A wannan ɗan waƙa sun yi wa wani ɗan siyasa habaici ta hanyar nasara da gogansu ke samu ga wanda yake wa habaici cewa kowa da abin da yake tsoro kusu (ɓera) kyanwa yaka tsoro. Aura (kare) kura yaka tsoro. Shi kuma wanda ake wa habaici, Tanimun yake tsoro. A nan za a ga abin a ɓoye yake ga mai sauraro ko karatu sai in an bayyana.

A waƙar Matawallen Sakkwato Aminu Waziri Tambuwal ma ya yi habaici a cikin ta kamar haka:

Jagora: Ko a siyasa in ta tashi,

           Mai jama’a shi ne aka zaɓe,

          Kai wane kar ka fito a gane ka,

          Baƙin jininka kare ya ɓaci,

Yara: Ko da ka je ka buga fosta,

          Ko a gida wani ba ya laƙa ta.

          A wannan ɗan waƙa Ɗanba’u ya yi wa wani ɗan siyasa wanda ke son ya yi takara habaici cewa ko a siyasa in ta tashi mai jama’a shi ne aka zaɓe, kai wane kar ka fito a gane ka. Ma’ana ko ya fito ba a zaɓen sa domin ba ya da jama’a saboda baƙin jinin da yake da shi, kamar yadda kare ke da baƙin jini ga yara. Don haka ya ji yana maganar zai buga fosta to ko ya je ya buga fosta ko a gida mutane ba su laƙa ta. A nan ya kira shi da wane kuma masu son su fito takara suna da yawa don haka zai yi wuya a gane wanda ake nufi.

A wani ɗan waƙar makaɗin ya ƙara da cewa:

Jagora: Abin da duk kura ka buƙata,

          Ba haka sarkin fawa ka so ba,

          Kura kwaɗanki har ya ɓaci,

          Ita dai kullum ta ci nama,

Yara: Dur randa ta shiga ba daidai ba,

          Sai ta sha kashi ga mutane.

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa wani habaici a kaikaice ta hanyar amfani da sunan sarkin fawa da kura da cewa abin da duk kura ka buƙata ba haka sarkin fawa ka so ba. A nan za a iya cewa maigida ne da yaronsa. Maigida shi ne sarkin fawa, yaron shi ne kura. Shi sarkin fawa duk lokacin da da ya yi yanka yana son ya sayar ya sami riba, ita kuma kura biɗa takai ta mamaye sarkin fawa. Ma’ana shi maigidan yana hasashen hanyar da za a bi a sami nasara, shi kuma yaron zagon ƙasa yake wa maigidan saboda kwaɗayin samun abin duniya har yake son ya zalunci maigidan. Du randa ta shiga ba daidai ba sai ya sha kashi ga mutane. Ma’ana duk randa ya kuskura maigidan ya gane sai ya ci kwakwarsa ɗanya.

A waƙar Attahiru Bafarawa mai taken:

Kada ka ji tsoron maza,

Riƙa zakin duniya,

Bai san tsoro ba,

Bafarawa Attahiru.

A wannan waƙar akwai habaici a ciki inda yake cewa:

Jagora: Ga ɗammanin Haji Ɗanba’u,

          Idan an je a wurin buki,

          Idan masu kuɗi sun haɗu,

          To da sun je kyauta sukai,

          Wani mai kuɗi ya barkace,

Yara: Rabon guraye yakai.

          A wannan ɗan waƙa Ɗanba’u ya yi wa wani mutum mai kuɗi habaici ta hanyar gugar zana da wani halin rowa da cewa ga ɗammanin Haji Ɗanba’u idan an je wurin buki, idan masu kuɗi sun haɗu da sun zo kyauta sukai, wani mai kuɗi ya barkace rabon guraye yakai. Ma’ana rowa gare shi bai iya kyauta amma gaba yake wurin rabon abinci. A nan wanda ake wa habaicin ya san da shi ake. Haka kuma duk wanda ya je wurin bikin ya ga lokacin da mai kuɗin ke rabon abinci zai fahimci da wanda ake. A nan ma’anar da Yahya da wasu (2016: 218) cikin Alun Nan Dai suka bayyana a sama ta fito fili.

A wani ɗan waƙa ya ce:

Jagora: Bafarawa Attahiru,

          Ga mota za ya ban,

          Katan keke ya hana.

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa wani mutum wanda ya hana a ba shi kyautar mota habaici da cewa Bafarawa ga mota za ya ban kata keke ya hana. A nan wanda ya hana Bafarawa ya ba shi mota ya san da shi ake kuma Bafarawa ya san da wanda ake domin ya san abin da ya faru, amma kuma wanda bai san abin da ke faruwa ba, ba zai gane ba.

A waƙar jam’iyar D.P.N. mai taken:

D.P.N. ta yi daidai da,

‘Yan Nijeriya,

Alheri yanzu kowa,

Buƙatatai yake.

          A wannan waƙa Ɗanba’u ya baje kolinsa wajen habaici a cikin ɗiyan waƙa da dama kamar haka:

 

 

 

Jagora: Mu ba duba mukai ba,

          Kuma ba tsahi mukai ba,

          Roƙon Allah muke,

D.P.N. dai ta hau,

Yara: Mazanmu da matanmu,

          Kowa ya zauna tahiya.

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa wasu ‘yan siyasa habaici. Irin wannan habaici da ya zo a cikin wannan ɗan waƙa shi ake kira habaicin zagi a kasuwa. A nazarin waƙa duk inda aka samu irin wannan magana akwai wanda ko waɗanda suke yi abin ke nan ma’ana masu duba da tsafi. Su roƙon Allah sukai, su kuma ‘yan wata jam’iya su ke duba da tsafi amma dai ba su ce musu suna yi ba, shi ya sa ake wa habaici kirari da maso faɗa kowa tamkar da shi ake.

A wani ɗan waƙa yake cewa:

Jagora: Ni mamaki nake,

          Mai duba shi da boka siyasa guda akai,

          Mai duba ya buga yace su za su ci,

          Boka ya yi tsahi da ‘yan kaji bakwai,

          Kuma Allah yai hani tona sirinai aji,

Yara: To du a gama ta sai sun yi kunya duniya.

          A wannan ɗan waƙa Ɗanba’u ya yi wa wasu ‘yan siyasa habaici a kaikaice ta hanyar gugar zana inda ya ɗan ƙyafato wasu ɓoyayyun halayensu waɗanda ba su fito fili jama’a suka sani ba, na duba da tsafi, domin Ɗanba’u da kansa a cikin layi na biyar a cikin wanann ɗan waƙar cewa ya yi: “Kuma Allah yai hani tona sirinai a ji.” Sai yara suka cika da cewa: “To du a gama ta sai sun yi kunya duniya.” Ma’ana ba kowa ya san suna tsafi ba amma duk a gama ta sai asirinsu ya tonu.

A wasu ɗiyan waƙa ya ƙara da cewa:

Jagora: Ina horon wane,

          Kullun ya kauce ya ƙiya,

          Wane ka bar neman shiga,

          Inda ‘yan taron daba,

Yara: Siyasar ‘yan gurguzu,

          Ai siyasar ƙeta ce.

 

Jagora: Ina jin tsoron mutum,

          Mai buƙatar gardama,

          Ban so haka nan ba,

          Wallahi Allah ya sani,

          Ina kallo wane ya kama daji,

Yara: Wane dawo ga hanya,

          Inda kowa ka murna ya hi kyau.

Jagora: Mutane ku yi hankali,

          Da sarkin ɓanna kare,

          Yana iya canye awakinku,

          In ta zaburo,

Yara: Ya ko runtce ido,

          Ya dawo ya ce ba shi ba ne.

          A irin wannan habaici da ya zo a cikin ɗiyan waƙar da suka gabata a sama shi ake kira habaicin hannunka-mai-sanda. Habaicin hannunka-mai-sanda habaici ne da ake yi domin jawo hankalin wani ko nuni a kan wani abin da ake so ya lura da shi ko ya gyara ko kuma don a sa mutum ya kama kansa. Za a ga ɗiyan waƙar uku da suka gabata dun hannunka-mai-sanda ne ake yi.

          A ɗan waƙa na farko yana yi wa wani mutum habaici ta hanyar yi masa hannunka-mai-sanda inda ya ambaci kalmar horo kai tsaye cewa ina horon wane kullun ya kauce ya ƙiya. Ma’ana yana hana shi shiga abin da bai da amfani ya ƙi, ya ƙara da cewa wane ka bar neman shiga inda ‘yan taron daba, siysar ‘yan gurguzu ai siyasar ƙeta ce. A nan ɗan waƙar ya fito da gargaɗi fili ba sai an yi dogon bayani ba.

          A ɗan waƙa na biyu shi ma yana jawo hankalin wanda ake wa habaici ta hanyar bayyana damuwa game da wanda ake faɗa wa gaskiya amma yana gardama. To ga shi an nuna masa hanyar gaskiya ya kauce mata, ya kama hanyar ƙarya. Duk da cewa ya kama hanyar da ba ta ƙwarai ba. ma’ana ya shiga jam’iyyar da ba D.P.N. ba, saboda soyayya da yake masa ya ƙara kiran sa da cewa wane dawo ga hanya inda kowa ka murna ya fi kyau. Ma’ana jam’iyar D.P.N.

          Shi ma ɗan waƙa na uku gargɗi ne yake yi ta hanyar habaicin hannunka-mai-sanda da cewa mutane su yi hankali da sarkin ɓarna kare. A nan yana kira ne ga mutane kaikaice su yi hankali da wani mutum wanda ya kira kare domin bai da amana, ana iya ba shi hakkensu ya cinye.

A waɗannan ɗiyan waƙar da suka gabata, za a ga abin a dunƙule ba za a iya cewa ga wanda ake nufi ba.

A wani ɗan waƙa ya ce:

Jagora: Baƙin kwaɗayin wane,

          Ya kai shi ɗaukar arkane,

Yara: Ga jirgin Makka,

          Ya taka motar Ɗandume.

          A wannan ɗan waƙar makaɗin ya yi wa wani habaici ta hanyar gugar zana ya kawo wani halinsa na kwaɗayi, sai ya kira shi da wane ta yadda ba za a iya gane wanda ake nufi ba kai tsaye.

A wani ɗan waƙa ya ƙara da cewa:

Jagora: Na san kissa kare,

          Ɗauke ƙahwa da ya yi,

          Ba ciyo ne takai ba,

Yara: Tsoro yaka yi,

          A korai da manyan dutsuna.

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa wani mutum habaici a kaikaice ta hanyar kwatance inda ya kwatanta abin da kare ta hanyar kissa da cewa, na san kissa kare ɗauke ƙafar da ya yi ba ciyo ne takai ba. ma’ana wani mutum ne ya bar zuwa wajen da suke zama. Shi ne ɗauke ƙafar da ya yi. Me ya sa ya bar zuwa wurin, sai ya ce: “Saboda bai da lafiya.” Shi ne yake cewa ba ciyo ne takai ba, ma’ana ƙarya yakai lafiyarsa lau. Dalilin da ya sa ya bar zuwa wurin shi ne yake cewa: “Tsoro yaka yi a korai da manyan dutsuna.” Ma’ana kada a yi masa wulaƙanci. A nan za a ga abin a dunƙule ba za a iya bayyana wanda ake nufi ba.

A wani ɗan waƙa yake cewa:

Jagora: In tafiya tai tsawo,

          Kai amali ka tsarsuwa,

          Jaki sarkin kuɗa,

Yara: Duk yada ka so ya kai,

          Inda zango bai zuwa.

          A wannan ɗan waƙa Ɗanba’u ya yi wa wani habaici ta hanyar kasawa a kan neman wata buƙata sai ya kwatanta abin da raƙumi da jaki da nuna cewa idan tafiya ta yi tsawo sai amali. Ma’ana raƙumi yana iya tafiya daga ƙasa zuwa wata ƙasa amma jaki bai iyawa. Shi ne Ɗanba’u ke kwatanta tafiya wasu ‘yan siyasa da nuna gwarzonsa shi ne amale. Shi ke iya wa tafiyar shi kuma wancan abokin adawa shi ne jaki duk yadda ake so yakai wani wurin ba zai iya ba.

A wani ɗan waƙa kuma yake cewa:

Jagora: Ni na san ungulu,

          Kolo rage taƙama,

          Taƙamar banza shi kai,

Yara: Yana iya tahiya,

          Da ya iske mushe yai ta ci.

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa wani ɗan siyasa habaici ta hanyar ɓoye sunansa ya kira shi da ungulu (kolo) kuma ya ɗan zoji wata ɗabi’arsa ta taƙama da cewa taƙamar banza ce tunda yana tafiya ya iske mushe ya sauka ya yi ta ci. Ma’anar mushe shi ne cin haƙin mutum ba da son ransa ba, don haka taƙamarsa ta banza ce tunda azzalumi ne.

A wani ɗan waƙa suke cewa:

Yaro: Mi ar ranar kilinge,

          Ga harkad duniya,

          Ko ga shi cikin gida,

Yara: Kyalla shurewa takai,

 

Jagora: Yanzu ko ga shi cikin gida,

Yara: Kyalla shurewa takai.

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa wani ɗan siyasa habaici a kaikaice ta hanyar ɓoye sunansa ya yi amfani da wani suna na daban wato kilinge da cewa mi ye ranar kilinge. Kilinge na nufin wuƙa wadda ta sallace ma’ana marar kaifi wadda ba ta iya yankan komai. Kyalla kuma na nufin babbar akuya lafiyayya. A nan abin da yake nufi shi ne, miye ranar wannan mutumin da ya ɓoye sunansa a cikin jam’iyyar siyasa tunda bai iya amfana mata komai.

A wani ɗan waƙa yake cewa:

Jagora: Ni na san,

          Maitatsine,

          Wuyal lamari garai,

          Don Allah dai mutane,

          Ku bar yarda da shi,

Yara: Ko an yi shiri da shi,

          Watce tsarin nan yakai.

          A wannan ɗan waƙar, Ɗanba’u ya yi wa wani ɗan siyasa habaici ta hanyar yi wa jama’a hannunka-mai-sanda game da shi, cewa su bar yarda da shi domin ko an ƙulla harka da shi ɓata tsarin yake.

A waƙar Alhaji Aliyu Magatakarda Wamakko mai taken:

 Ɗantakarar zama gwamna,

Magatakarda Wamakko,

Aliyu kar ka ɗau reni,

Kuma kar ka ɗau wulaƙanci.

          A wannan waƙar Ɗanba’u ya yi habaici a cikin wasu ɗiyan waƙa, kamar inda yake cewa:

Jagora: Ni na tabbata kana da basira,

          Na sani kana da tunani,

          To amma fa ka ƙara kulawa,

          Angulu munahukin Allah ne,

Yara: In ka ganai wurin yaƙi,

          Shi ba da gaske ya zo ba.

           A wannan ɗan waƙar makaɗin ya yi wa wani habaici ta hanyar yi wa ɗan takara hannunka-mai-sanda cewa ya san yana da basira kuma ya san yana da tunani, to amma fa ya ƙara kulawa, sai ya ɓoye suna, sai ya kira shi da angulu munafukin Allah ne in ka ganai wurin yaƙi shi ba da gaske ya zo ba. ma’ana duk yadda yake nuna goyon bayansa kada ya amince masa. Ba da gaske yake ba.

A wani ɗan waƙa kuma cewa ya yi:

Jagora: Ga magatakarda ga Muntari,

          To amma fa ku ƙara kulawa,

          In dai abin rabo ya samu,

          A danƙa ma masu imani,

Yara: Don kada a bai wa kuraye shiya,

          In sun haɗe shi an huta.

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa wasu habaici ta hanyar hannunka-mai-sanda ga ɗan takarar gwamna da mataimakinsa da cewa su ƙara kulawa in dai abin rabo ya samu a damƙa ma masu imani, ke nan waɗanda aka saba ba abin rabon suna zalunci, a canza su idan kuma aka ci gaba da ba su ba za su yi adalci ba canye shi za su yi. A nan za a ga an yi suka a kaikaice ta yadda ba za a iya gane da wa ake ba.

A waƙar Dr. Aliyu Magatakarda mai taken:

Maganin wargi ɗan Garba,

Aliyu sabon gwamna Sakwkato,

Ba a kai ma reni ko kusa.

          A wannan waƙar Ɗanba’u ya yi habaici a cikin wasu ɗiyan waƙa kamar haka:

Jagora: Ka ga mutum-mutumi da kamar mutum,

          Da ka ganai ka ga tsumma ne kurum,

           Bai hana komai bai tare komai,

          Ka yi shi don ya tsare ma gona,

Yara: Bai hana tsuntsu ɓata ma ita.

          A wannan ɗan waƙar makaɗin ya yi wa wani mutum habaici da cewa ka ga mutum mutumi da kamar mutum. Mutum-mutumi na nufin karare ko itace da aka haɗawa, a sa masa riga da hula a cikin gona matsayin mai tsaro musannan ga yara da tsuntsaye. Ma’ana ga mutum cikakke da ka gan shi ka ga kamilin mutum wanda ke iya yin abin kirki, amma bai iya komai ba, tsumma ne kawai, ma’ana girman ne kawai, bai da wani amfani ga jama’a, da shi da mutum-mutumi duk ɗaya. To in ka aje shi ne domin ya tsare ma gona, bai hana tsuntsu ɓata ma ita ma’ana idan an aje shi domin ya magance wata matsala, to aikin banza aka yi domin ba zai iya ba, kunya kawai za a ji. A nan za a ga abin a dunƙule ba za a iya gane wanda ake nufi ba.

A wani ɗan waƙa ya ƙara da cewa:

Jagora: Allah waddan gurun kolo,

          Da ɗai bai saba kashin kunya ba,

          Shi bai saba kashin kunya ba,

          Ba ka sani sai ka je gaisai,

          In ya yi ma kyauta ka duba,

          Ka dubi girmanai ka ga kyauta,

Yara: Abin akwai abin ban kunya ‘yan uwa.

          A wannan ɗan waƙar makaɗin ya yi wa wani babban mutum habaici ta hanyar raina kyautar da yake yi, da cewa idan ya yi ma kyauta ka dubi kyautar ka dubi girmansa ka dubi kyautar abin akwai kunya. A nan Ɗanba’u ya danganta girmansa da gurun kolo. Kasancewar gurun kolo bai da amfani domin ba a ra’ayinsa. Shi ma girmansa bai da amfani domin bai iya kyautata ma jama’a. Sai dai ya yi abin a kaikaice ta yadda ba za a iya gane wanda ake nufi ba.

 

A waƙar Alhaji Aliyu Magatakardan Wamakko mai taken:

Ƙara shirawa

Aliyu zaɓaɓɓen gwamna,

Mai ban tsoro Magatakardan Wamakko,

Sarkin Yamman Sakkwato bai san wargi ba.

         

A wannan waƙar Ɗanba’u ya gina habaici a ɗiyan waƙa daban-daban kamar haka:

Jagora: Mun sani Allah shi ka ba da mulki ya ba ka,

          Don kak ka bi shawarar buhun kowa,

          Mai so a ƙi wa kowa komai,

Yara: Ɗan Barade Alu,

          Kai ta wa mutane adalci.

 

          A wannan ɗan waƙar makaɗin ya jefi tsuntsu biyu da dutsi ɗaya ya yi wa wani mutum na tare da gwamna habaici kuma, ya yi wa gwamna hannunka-mai-sanda da cewa Allah shi ka ba da mulki kuma ya ba shi, kada ya bi shawara buhun kowa mai son a ƙi wa kowa komai, ɗan Barade Alu kai ta wa mutane adalci. A nan yana ƙara ba gawamna shawara cewa kada ya bi shawara wani mutum da yake tare da shi mai rowa wanda ba ya son a yi alheri.

A wani ɗan waƙa kuma yake cewa:

Jagora: In ka ji ƙi gudu Ɗanba’u,

          Sa gudu ne ab bai zo ba,

          Ranaz zaɓenka ɗan Barade na wamakko,

          Waɗansu maza hay Yamai suna ɓoyo,

Yara: Kahin a yi zaɓe sun tcere.

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa wasu mutane habaici ta hanyar tserewar da suka yi ranar zaɓe ganin cewa ba su da nasara, kafin a gama zaɓe a ƙidaya (ƙirga) sai suka tsere suka tafi Yamai a ƙasar Nijar. Shi ne yake sukar su cewa duk wanda ya ce ba ya gudu to wanda ke sa gudu ne bai zo ba, da mai sa gudu ya zo ma’ana ruwan ƙuri’ar da suka ga ana yi wa Alu, sai ga shi sun tsere da kafafunsu sun bar ƙasa sukutum saboda kunya da gudun wulaƙanci. A nan waɗanda ake wa habaici sun san da su ake, kuma duk wanda ya san lokacin da suka tsere sun san da wanda ake amma wanda duk saurare kawai yake bai san abin da ke faruwa ba, bai iya gane wanda ake wa habaicin.

 

A wasu ɗiyan waƙar kuma ga abin da yake cewa:

Jagora: Na gaya ma mutane ɗauke dahi sai giwa,

Yara: Maza tahi kauce zomo ba ka iyawa wa kai nan?

 

Yaro: Da ma hanƙurin kwaram sai goga,

          Wuyau ta sai ƙarfe,

          Jure fari sai tofa,

          Baba ruwa da kada ba a zuwa wanka,

          Sai dai a tsaya kallo.

Jagora/yara: Wani ya shiga zai wanka,

          Da ya shiga bai kai wajje ba.

          A waɗannan ɗiyan waƙar suna jifar tsuntsu biyu da dutsi ɗaya suna gwarzanta gogansu suna sukar abokin hamayyarsa kaikaice a kan kasawar da ya yi. Ɗauke dafi sai giwa, gogansu ne giwa. Maza tafi kauce zomo, abokin hamayya ne zomo, ba ka iya wa wa kai nan?

          A ɗa na biyu inda aka ce da ma hanƙurin kwaram sai goga, gwarzonsa ke nan, jure fari sai tofa, ruwa da kada sai kallo wani ya shiga zai wanka da ya shiga bai kai wajje ba. A nan duk habaici ne kaikaice ake wa abokin hamayya na kasawar da ya yi.

A waƙar Sardaunan Hamma’ali mai taken:

Sardaunan Hamma’ali zaki,

Malami Maigandi bi da arna.

A wannan waƙar ma makaɗin ya yi habaici a cikin ta inda yake cewa:

Jagora: Na sauka kware don in ga ciyaman,

          Na tahi ofis sai nig gaisai,

          Sai ya ce a ba ni kuɗɗin mai,

          Da ya ce a ba ni kuɗin mai,

          Ni yi jira ba a miƙa min ba,

          Ni mamaki ya kama ni,

          Ga rijiya ta ba da ruwanta,

Yara: Sai guga ta hana a ɗebo.

          Sai jagora ya ce: “Ke guga ‘yar baƙin ciki,” a nan dai ya ba da bayanin abin da ya faru da kansa a ƙarshe sai ya yi suka kaikaice rijiya ta ba da ruwanta sai guga ta hana a ɗebo. Ma’ana ciyaman shi ne shugaba kuma shi ke da iko a kan komai na ƙaramar hukumar, ya ce a ba shi kuɗin mai amma wanda an ka ce ya ba shi ya hana. A nan ciyaman shi ne rijiya. Wanda aka ce ya ba shi kuɗi shi ne guga.

A waƙar Dr. Sama’ila Sambawa mai taken:

Yaro ya ja maka a ƙarya,

Ɗan takarar Gwamnan Kebbi,

Dr. Sama’ila Sambawa.

          A cikin wannan waƙar Ɗanba’u ya yi habaici a cikin wasu ɗiyan waƙar kamar haka:

Jagora: Du ya da aura ya kai ƙarhi,

          Ba ya shiga ɗakin kura,

          Idan ba da bindiga ya zo ba,

          Ko da da bindiga ya zo ma,

          Kare ba ya i mata wa ash shi.

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa wani habaici da cewa duk yadda aura (kare) ya kai ƙarfi ba ya shiga ramin kura. Ma’ana duk yadda wanda ake wa habaici yake ganin yana da ƙarfi, to ya sani bai yi ƙarfin sambawa ba in ba da bindga ya zo ba, ma’ana sai ya yi gagarumin shiri, kuma ko da ya yi gagaruma shiri, ba ya iya wa da shi. Ma’ana wanda ake wa habaici duk yadda yake ganin yana da jama’a to bai iyawa da Sambawa.

A wani ɗan waƙa yake cewa:

Jagora: Wani ya ci tuwonsa na shinkahwa,

          Ya ɗauki Pure water ya sha,

          Sai ya gano bawan Allah,

          Mai cin tuwon dussa kullum,

          Ya ce ya hana masa dussatai,

          Ku al’umma na tambaiku,

          Shin wannan shi ne adalici?

Yara: Wannan ya yi babban zalunci,

          Ko ba a ce masa komai ba.

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa wani mutum habaici kaikaice cewa wani ya ci tuwonsa na shinkafa ya ɗauki pure water ya sha, ma’ana yana bisa babban aikinsa sai ya gano bawan Allah mai cin tuwon dussa kullum. Ma’ana shi wanda ke bisa ƙaramin aikin da ko cefane ba ya yi masa ya ce ya hana masa dussatai. Ma’ana ya kore shi daga aiki. Ku al’umma na tambai ku shin wannan shi ne adalci? Sai ya ba da amsa da kansa cewa wannan ya yi babban zalunci koba a ce masa komai ba. A nan za a ga abin a dunƙule yake. A taƙaice ambatar wani ke nuna habaici a cikin ɗan waƙar domin ba a fayyace ba.

A waƙar ciyaman ɗin Gwadabawa Alhaji Musa Lumu mai taken:

Gwabron giwa kullun yana halin yabo,

Alhaji Lumu Musa ciyaman zarumi.

 

A wannan waƙar Ɗanba’u ya yi habaici inda yake cewa:

Jagora: Baƙar akuya wance ke ad da ƙallallen ƙaho,

          Ban layya da ke kuma ba mu yin suna da ke,

Yara: Mu ba mu sayen ki bari masu yin tsahi su sai.

 

A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa wata mace habaici ta hanyar ɓoye sunanta da cewa: “Baƙar akuya wance ke ad da ƙallalen ƙaho ban layya da ke kuma ba mu yin suna da ke mu ba sayen ki bari masu yin tsafi su saye ma’ana ba su buƙatar ta a jam’iyyarsu, domin halayyarta da ɗabi’unta kamar yadda ba a buƙatar a yi layya da dabba mai ƙallalen ƙaho kuma ba a yin suna da ita. Don haka duk mai halayya irin tata ba a buƙatar ta a siyasa. A nan yana da wuya a fahimci wadda yake nufi. Rashin gane waddea ake nufi ya tabbatar da habaicin da ake bayani a kai.

4.7 Naɗewa

          Wannan babi an yi bayanin habaici tun daga asalin kalmar da ma’anarta da ire-irenta, daga ra’ayoyin masana da manazarta daban-daban tare da kawo dalilan da ke sa a yi habaici. Haka kuma an bayyana muhimmanci/amfani da ake samu ta hanyoyinsa. A ƙarshe an kawo sharhin habaici a cikin wasu waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanba’u Gidan Buwai ta hanyar fitowa da abubuwan da masana suka bayyana a matsayin habaici. Haka kuma an yi nazarin wasu waƙoƙinsa da ke ɗauke da habaici aka kawo misalai a wurare daban-daban.

Post a Comment

0 Comments