Ticker

6/recent/ticker-posts

Zambo Da Habaici A Cikin Wasu Waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanba’u Gidan Buwai (3)

Habaici suka ce da ake yi kaikaice cikin wasu ɓoyayyun kalmomi na hikima masu ban sha’awa da ban dariya ga mai sauraro tare da cusa haushi da ban takaici da ɓata rai ga wanda ake wa. Habaici ba kai tsaye ake gane da wanda ake ba, sai wanda ya san abin da ke faruwa.

Zambo Da Habaici A Cikin Wasu Waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanba’u Gidan Buwai (3)

 

NA

SHEHU HIRABRI
08143533314

 

Kayan Kiɗan Hausawa

BABI NA UKU

ZAMBO A CIKIN WASU WAƘOƘIN ALHAJI MUSA ƊANBA’U GIDAN BUWAI

3.0 Shimfiɗa

          Wannan babi zai yi bayani tare da kawo misalai a kan asalin kalmar zambo da ma’anrta da ire-irenta da dalilin da ya sa ake yin zambo da amfanin sa ga al’umma tare da yin sharhinsa a cikin wasu waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanba’u Gidan Buwai.

3.1 Asalin Kalmar Zambo

          An samu bambancin ra’ayi dangane da asalin kalmar zambo. Masana da manazarta da dama sun tofa albarkacin bakinsu dangane da asalin kalmar. Abdullahi, (1995: 21) cewa ya yi: “Asalin zambo abu ne mai wuya a ce ga lokacin da aka fara samun sa a cikin waƙa kamar yadda ba a iya cewa ga rana ko lokacin da aka fara waƙa gaba ɗayanta. A nan ina ganin tun lokacin da ɗan Adam ya fara buɗe baki da sunan yin waƙa ya ƙirƙira dabarar yin zambo don yi da wani ko musguna masa a kaikaice. Da haka dai zambo ya ci gaba da yawaita a cikin waƙar baka ta Hasua har kawowa wannan lokaci da ya zama ruwan dare a cikin waƙoƙi.”

          Yahaya da wasu (2006: 40) cewa suka yi: “Asalin kalmar zambo, Bahaushiyar kalma ce, ba aro ta an ka yi ba.” Dalilin da suka kafa shi ne, zambo daɗaɗɗen abu ne a cikin tarihin adabin Bahaushe na gargajiya.

          Wasu na ganin asalin kalmar zambo daga harshen Larabci aka samo ta, wato “alzammu” mai ma’ana da Larabci zargi. Sannu a hankali kalmar ta tashi daga zammu ta koma zambo (Yahaya da wasu, 2006: 40).

          Bunza, (2009: 132) cewa ya yi: “kalmar zambo ta fuskar furuci da rubutunsu da ma’anarsu ta fi kusa da kalmar zamba.”

3.2 Ma’anar Zambo

          Masana malamai da manazarta da dama sun bayyana ra’ayi dangane da ma’anar zambo kamar haka:

          Gusau, (1979: 39) cewa ya yi: “Zambo kalma ce wadda ake amfani da ita a matsayin kishiyar yabo, wato a siffanta wani mutum da wasu siffofi munana waɗanda za su walaƙanta shi da jawo masa rashin martaba a idon ‘yan Adam tare da kau da kai cewa wannan mutum yana da waɗannan siffofi ko ba shi da su.”

          Dangambo, (1984: 32) cewa ya yi: “Zambo zagi ne na kai tsaye, cikin zambo ana siffanta mutum da halayensa da ɗabi’unsa da danginsa da iyayensa da dai duk wani abu da ya shafe shi wanda zai taimaka a gane da shi ake.”

          Gusau, (1988:315) cewa ya yi: “Zambo wasu kalmomi ne na muni da ci wa mutum mutunci da ake amfani da su kai tsaye ga wanda ake buƙata. A wajen zambo ana iya fitowa fili a faɗi wata fitacciyar siffa ta mutum wanda nan take ake saurin gane wanda ake nufi.”

          Modibbo, (1989: 32) cewa ya yi: “Zambo dai shi ne faɗin mugun abu ga mutum, kuma zambo kishiyar yabo ne. akan ɓaci mutum da abin da yake na gaskiya, amma maras kyau ko kuma ƙage.”

          Abdullahi, (1995: 21) cewa ya yi: “Zambo magana ce da akan shirya a cikin waƙa domin muzanta mutum. Mawaƙan Hausa na baka da marubuta suna amfani da zambo a cikin waƙoƙinsu don musgunawa abokan hamayyarsu ko abokan hamayyar waɗanda suke yi wa waƙa, ta fitowa ƙuru-ƙuru su muzanta su ta siffanta su da wasu abubuwan munana marasa kyau kamar rowa rashin fara’a da dai sauransu.”

          Shinkafi, (1998: 20) cewa ya yi: “Zambo siffanta mutum da wasu siffofi munana domin a muzanta shi ga idon mutane ko da ba ya da su. Zambo kishiyar yabo ne.”

          Dumfawa, (2005:19) cewa ya yi: “Kalmar zambo tana nufin aibanta wani mutum ko wani abu dangane da sifarsa ko aƙidarsa ta yin amfani da wasu lafuzza na aibantawa ko muzantawa ko munanawa.”

          Ƙamusun Hausa na Jami’ar Bayero (2006:489) an bayyana cewa: “Zambo na nufin ƙaga wa mutum magana wadda za ta muzanta shi ta ɓata masa suna ba tare da bayyana wanda ake yi wa ba. Maroƙa sun fi yin haka a cikin waƙa.”

          Bunza, (2009: 132) cewa ya yi: “Kalmar zambo ta fuskar makusanciyar ma’ana tana da alaƙa da habaici, ta fuskar furucinsu da rubutunsu da ma’anarsu tafi kusa da kalmar “zamba”. Zambo ya fi habaici zafi domin ƙaga shi ake yi a liƙa wa wanda ake yi wa. Daga cikin kayan cikin zambo akwai:

i.                   Wulaƙanta wanda ake yi wa da wani abu na ƙasƙanci ga irin matsayinsa.

ii.                 Ƙara gishiri ga halinsa, ko wani aibi da aka san shi da shi.

iii.              Ƙago abin da bai ji ba bai gani ba, a ce ya yi, ko ya ce ko nasa ne.

iv.               Yi masa muguwar fata.”

 Zaruk da wasu (2011) cewa suka yi: “Zambo ɗan uwan habaici ne. sai dai shi zambo ya fi habaici tsanani. Galibi idan an yi wa mutum zambo domin a tozarta shi a idanun jama’a idan za a yi wa mutum zambo akan ɗauki wani hali nasa ko sifa a yi masa zambo da shi.”

          Ɗanhausa, (2012) cewa ya yi: “Zambo ana yin sa ne musamman dan faɗakar da mutum ta hanyar ɓata shi, wato fallasa shi domin a nuna ana sane da ire-iren miyagun ɗabi’u da ke tare da shi haɗe da ba shi shawara amma ba kai tsaye ba, ta cikin hikima wato rara-gefe idan an misalta shi da zambo.”

          Yahya da wasu (2015: 17) cewa suka yi: “An bayyana zambo a matsayin kalma wadda ake amfani da ita a matsayin kishiyar yabo wato a siffanta wani mutum da wasu siffofi munana waɗanda za su wulaƙanta shi da jawo masa rashin martaba a idon ‘yan Adam tare da kau da kai cewa wannan mutum yana da waɗannan siffofi ko ba shi da su.”

          Yakasai (2012: 171) cewa ya yi: “Zambo salo ne da ‘yan siyasa musamman mawaƙa suke amfani da shi domin su muzanta wani ko wasu ƙungiyoyin siyasa ta fuskar ambata tare da ƙirƙiro wasu miyagun ɗabi’u ko asali su danganta su ga wanda suke son su naƙƙasa domin mutane su kauce wa jefa masa ƙuri’a lokacin zaɓe.”

          Idan aka yi la’akari da waɗanna ma’anonin da suka gabata, a tawa fahimta ana iya cewa: Zambo suka ce da ake yi kai tsaye ta hanyar kawo hoton mutum, ko wani abu cikin surarsa ko halayensa ko kuma duk wani bayani wanda zai taimaka a fahimce da wanda ake kai tsaye domin a ɓata masa rai tare da walaƙanta shi da kuma kadar masa da ƙima da mutunci a idon jama’a.

 

 

3.3 Ire-Iren Zambo

An samu bambancin ra’ayi dangane da ire-iren zambo. Barmo (2014: 15) da Modibbo (1989:32) sun bayyana ire-iren zambo kamar haka:

1.     Zambon halitta

2.     Zambon asali

3.     Zambon sarauta

4.     Zambon hali

Shi kuwa Tuluwa (2012: 75) ya kawo ire-iren zambo kamar haka:

1.     Zambon kama ko halitta

2.     Zambon asali

3.     Zambon matsayi

4.     Zambon hali

A nan an samu bambanci tsakanin zambo sarauta da zambon matsayi.

1.3.1      Zambon kama ko Halitta: Zambo ne da mawaƙa ke yi ta hanyar bayyana wata halitta da Allah ya yi wa mutum ko kuma su kalli wani abu da ya yi kama da halittar ya kira mutum da sunan wannan abin ko ya kwatanta su. Misali, a waƙar Alhaji Musa Ɗanba’u Gidan Buwai inda yake cewa:

Jagora: Ga wani ɗan takara da doro,

            Abu dai zuƙui-zuƙui,

             Ke kuma bushiya ki ɓoye doronki,

             Ba ki bakin komai.

Yara:    Wurin hwarauta banza ce.

 

Gindi:  ‘Ya’yan Nijeriya,

            Siyasa ta tashi,

             Ku dawo mu yi ƙoƙari,

             Mu koma PDP

 

1.3.2      Zambon Asali: Zambo ne da mawaƙa ke yi wa mutum ta hanyar bayyana wani abu da ya shafi tushen asalin mutum ta fuskar tozartawa ko muzantawa. Misali kamar zambon da Audu Stim ya yi wa wani sharifi inda yake cewa:

Wane ba mu zagin babanai,

Don darajar kakansa,

Wurin uwa tai muka komawa

Mu yi mai gora,

Mun san asalin wance

Tasha tat tashi.

 

Gindi: Bafarawa Gwamnan Sakkwato,

           Mai adalci mu muna tare da kai,

           Gwamna muna bayanka.

 

Wani misali a cikin waƙar Ɗanba’u inda yake cewa:

Jagora: Kowat taso tare da manya,

            Ka san yana da tarihi,

            Don haka manya sunka gaya mini,

Yara:    Danginsu Maguzawa ne.

 

Gindi:  Ɗantakarar zama gwamna,

            Magatakarda wamakko,

            Aliyu kar ka ɗau reni,

            Kuma kar ka ɗau wulaƙanci.

 

1.3.3      Zambon Matsayi: Zambo ne da ke da fuska biyu. A fuska ta farko mawaƙa kan yi amfani da matsayin da mutum ya samu musamman lokacin da aka yi jayayyar sarauta ko mulki ko wani abu makamancinsu, sai su yi amfani da wannan matsayi su wa abokan hamayya zambo. Misali a waƙar Ɗanba’u ta ciyaman ɗin Gada Tanimun Ɗangaladima inda yake cewa:

Jagora:  Ƙara hanƙuri kar ka ji komai,

             Hanƙurinka shi na kai ka haka,

             Hak ka yi ciyaman ƙasar Gada

             Ka kada biri sarkin ƙwalama,

             Ci ƙungurguma a ci buzuzu,

Yara:    Na ce biri a yi a hankali

             Wata ran cikinka ya ɓaci.

 

          A fuska ta biyu mawaƙan sukan yi zambo domin ƙoƙarin ɓata wani matsayi da wani mutum yake da shi a idon jama’a domin muzanta shi ko a ɓata masa rai. Misali a waƙar Ɗanba’u ta Aliyu Magatakarda Wamakko inda yake cewa:

Jagora: Aliyu kai ka gadi sarauta,

            Ka yi naɗi daidai da sarauta,

            Wanda duk bai gadi sarauta ba,

            Yara ko ga naɗi sai mun gani.

Yara:    Wane naɗi nai ya cika girma,

             Wanga uban huni sai ‘yan dako.

 

Gindi:   Ƙi sake bajini gwarzon maza,

             Ali sarkin Yamman Sakkwato.

 

1.3.4      Zambon Hali: Zambo ne da mawaƙa kan yi ta hanyar amfani da mugun halin mutum sai a yi masa zambo a kai nai. Wani lokaci kuma sukan kwatanta halin mutun da na wata dabba mai irin halinsa sai su yi zambo su ɗora a kansa. Misali, ana iya wa mutum zambo ta hanyar rowa da sata da zina da kushili da ƙarya da munafunci da zalunci da makamantansu. Haka kuma ana wa mutum zambo da halin dabba kamar biri da jaki da kusu (ɓera) da muzuru da bunsuru da kare da makamantansu. misali a waƙar Ɗanba’u ta Matawallen Sakkwato Aminu Waziri yake wa abokin hamayya zambo da halin rowa inda yake cewa:

Jagora: Ga wani na neman Matawalle,

             Kai ƙwanƙiro wa za ya naɗa ka,

             Kowa ya san bai alheri,

Yara:    Bai iya kyauta ba a yaba mai,

 

Gindi:   Ɗan waziri ka ƙara shirawa

             Aminu yau kai am matawalle.

 

          Wani misali a cikin waƙar Narambaɗa ta mazan gabas tsayaye yana yi wa wani ɗan sarki zambo da halin ƙarya da rowa, inda yake cewa:

Jagora: Ka ga ɗan sarki da kurruwa da hwaɗi

            Ga ya da ƙarya ga ya da rowa,

Yara:    Ko ka girmama shi ba ya sarki.

 

Gindi:  Masu gari mazan gabas tsayayye

 

 

 

3.4 Dalilin Yin Zambo

          Dalilai da dama ke sa a yi zambo, daga cikinsu akwai:

i.                   Duk lokaci da aka yi jayayya ta siyasa ko sarauta ko neman aure ko nema wani muƙami ko wani matsayi da makamantansu. Mawaƙa da waɗanda ba mawaƙa ba kan yi zambo ga abokan hamayya.

ii.                 Ana yin zambo domin a muzanta mutum ko wulaƙanta shi ko cin zarafinsa.

iii.              Ana yin zambo domin a bayyana wani mugun hali ko ɗabi’a da mutum ke da.

iv.               Ana yin zambo domin a huce haushi musamman in akwai wata adawa ko husuma a tsaknin wasu.

v.                 Ana yin zambo domin tsoratarwa a kan wani abu da wani ke son ya yi ga wani mutum ko wani al’amari kamar sarauta ko siyasa ko wani abin da ya shafi zamantakewar al’ummar Hausawa.

vi.               Ana yin zambo don samar da nishaɗi da raha a cikin zukatan al’umma.

vii.            Ana yin zambo don a ɓata wa mutum rai.

3.5 Amfanin Zambo

          Duk da yake zambo suka ce da ake yi kai tsaye ta fuskar ɓatanci, amma kuma yana da amfani matuƙa. Daga cikin amfanin zambo akwai:

1.     Zambo yana hana yin shishigi watau mutum ya shiga sha’anin da bai shafe shi ba.

2.     Zambo wani ado ne da ke ƙawata waƙa tare da ƙara mata armashi, ba waƙa kawai ba har sauran zantukan yau da kullum.

3.     Zambo na sa mutum ya san miyagun ɗabi’unsa ko ƙazafi ko wani abin da jama’a ke zarginsa da shi.

4.     Zambo na sa mutum ya daina wasu miyagun halaye ko ɗabi’u

5.     Zambo na bayyana miyagun ɗabi’un jama’a cikin hikima domin a ƙaurace musu.

6.     Zambo kan taimaka wajen ƙara soke abokan hamayya.

7.     Ƙwarewa wajen gina zambo a cikin waƙoƙi musamman na siyasa ko sarauta na ƙara wa mawaƙi ɗaukaka da farin jini ga jama’a.

8.     Ƙwarewa wajen gina zambo a cikin waƙoƙi, na sa mawaƙi ko maroƙi ya samu alheri.

9.     Zambo wata taska ce ta adana adabin al’ummar Hausawa.

10. Zambo na samar da nishaɗi cikin raha da wartsakewar rayuwa.

3.6 Zambo A Cikin Wasu Waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanba’u Gidan Buwai

          A sama an kawo ma’anar zambo da ire-irensa da dalilan da ke sa a yi shi tare da bayyana amfaninsa. A nan kuwa za a kawo zambo a cikin wasu waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanba’u tare da yin sharhinsa a bisa mizanin nazari.

          Kamar yadda Yahya( 1997) ya bayyana cewa: “Zambo wasu zantuka ne ake yi ta hanyar zaɓen wasu kalmomi da za su ɓata ko musguna wa wanda ake wa. Akan kwatanta kama ko ɗabi’a ko hali na mutum da wasu siffofi don a wulaƙanta shi. Kenan zambo yakan bayyana wanda ake wa shi a fili ba tare da wata wahala ba.

          Za a ga irin waɗannan bayanan da Yahya, (1997) ya bayyana a kan zambo a cikin wasu waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanba’u. Haka kuma Ɗanba’u na amfani da hanyoyi biyu wajen gina zambo a cikin waƙoƙinsa.

          Hanya ta farko Ɗanba’u kan dubi abin da ke faruwa tsakanin wanda yake wa waƙa da abokin hamayyarsa sai ya gina zambo. Hanya ta biyu Ɗanba’u kan gina zambo ta hanyar bayyana wani abu da ke faruwa tsakaninsa (shi mai kiɗi) da wani mutum sai ya gina zambo a cikin waƙa.

A waƙar Alhaji Musa Ɗanba’u mai taken:

Ciyaman bugun ciyamomi:

Bala ba a jan ka ɗan Musa.

Wadda ya yi wa ciyaman ɗin Yabo Alhaji Bala Musa Yabo, inda yake cewa

Jagora: Wani ya sha karo da ɗan Musa,

            Ado na ji Bala ya kasai,

            Can nig gane shi Dagawa,

            Wawa ya ɗau buhuhuwan lalle

Yara:   Ya ce za ya kasuwa muza.

          Idan an lura, wannan ɗan waƙa mawaƙin ya bayyana wata gwagwarmayar da aka yi a lokacin zaɓen ciyamomi inda Bala Musa ya samu nasarar lashe zaɓen, sai ya yi amfani da galabar da ya samu sai ya wa abokin takararsa zambo da cewa ya sha karo da ɗan Musa. Kuma an kasai. A nan kowa zai fahimci da wanda ake wato abokin takararsa, kuma don ya ƙara bayyana wanda yake wa zambo sai ya kawo sunan garin Muza saboda abokin hamayyarsa ɗan garin Binjin Muza ne. Haka kuma a wani ɗan yake cewa:

Jagora: Kansiloli daban-daban Audu,

            Kansiloli daban-daban Ada,

            Ga kowane yana ta ƙiba,

            Ɗan tsuntsun tsorolo tsomodo,

Yara:   Shi har yanzu bai yi gwaɓi ba.

 

          A wannan ɗan waƙar mawaƙin ya kawo siffar wani kansila wadda za ta sa a fahimci wanda ake wa zambo. Saboda ya nuna shi wannan mutum siriri ne kuma bai da ƙiba.

Duk dai a cikin wannan waƙar ya ƙara da cewa:

Jagora: Wani ciyaman na duba,

             Ƙazami ne ku mun san shi,

             Taro munka je da shi Legas,

             Kwana ukku bai yi wanka ba,

             Yadda ya mammatso ni sai nic ce,

Yara:    Tahi dan nan kana yi man wari.

          A wannan ɗan waƙa ya yi wa wani ciyaman zambo ne a kan wata halayyarsa ta zama da dauɗa, domin idan aka gan shi kamar ba ciyaman ba, ga shi da rowa kuma ko kansa bai amfana ba.

 

 

Waƙar Gwamnanmu Mun yi Mun Ƙare Ta Alhaji Aliyu Magatakarda Wamakko

Amshi: Ɗantakarar zama gwamna,

            Magatakarda Wamakko,

            Aliyu kar ka ɗau reni,

            Kuma kar ka ɗau wulaƙanci.

 

          A cikin wannan waƙar Ɗanba’u ya baje kolinsa ta hanyar gina zambo a ɗiya da dama, kamar haka:

Jagora:  Tun sadda wane yai gwamna,

              Martabar jaharmu ta hwaɗi,

              Mai ilimi da da marar ilimi,

              Dole ne a samu bambanci,

              Ku Sakkwatawa albishirinku,

              Ga ɗan uwanku nan ɗanku,

              Shi za ya takarar gwamna,

              Ku daure ku ba shi goyon baya,

 

Yara:     In Aliyu ya zamo gwamna,

              Martabar jaharmu ta tashi.

 

          A wannan ɗan waƙar mawaƙin ya kawo bayanai kai tsaye waɗanda ke sa a fahimci da wanda ake, kamar “gwamna da ilimi” a nan kowa zai fahimci gwamnan da ake magana wato gwamnan da ke jayayya da ɗan takarar da ake yi wa waƙa. Haka kuma ya kawo maganar ilimi kasancewar gwamnan bai yi karatu mai zurfi ba daga firamari sai takardar kammala karatun piɓotal. Shi kuma wanda ake yi wa waƙa a ƙasar Amurika ya yi karatunsa na digiri. A nan ya soki gwamna da cewa tun lokacin da wannan gwamnan ya fara mulki martabar jiharsu ta faɗi saboda ba ya da ilimin gudanar da mulki. Sannan ya yabi ɗan takararsa da cewa idan suka zaɓe shi martabar jaharsu za ta dawo saboda yana da ilimin gudanar da mulki.

Haka kuma a cikin wani ɗan waƙar yake cewa:

Jagora: Tsaya abin ga na da mamaki,

            Birni da ƙauye na duba,

            Kuma manya da yara na duba,

            Duk inda ka ishe ɗan abarba,

Yara:    Ya iya shirin munahucci.

 

Jagora: wannan

Yara:    Ya iya shirin azuranci.

 

          A wannan ɗan waƙar mawaƙin ya yi amfani da alamar wata jam’iya mai hoton abarba ya kira su da suna ‘yan abarba’ wanda kowa zai fahimci ‘yan jam’iyar da yake nufi. Ya soke su ta hanyar mamaki da cewa ‘yan birni da ƙauye manya da yaransu duk sun iya munafucci da azuzanci.

Duk a cikin waƙar ya ƙara da cewa:

Jagora: Ni Ɗanba’u hamdullahi,

            Na yi godiya wajen Allah,

            Siyasar su wane ta watse,

            Yau shekara takwas suna mulki,

            Girman sarakuna sun kasai,

            Ga ɗan talakka ya sha ƙwaya,

            Wai za ya kori sarkinmu,

            Kahin ya kori sarkinmu,

            Allah ya biya buƙatunmu.

Yara:   Sai ga sakamako ya yi,

            Shi ya rigayi hisshe shi.

 

          A wannan ɗan waƙar mawaƙin ya yi zambo ga wasu ‘yan siyasa abokan hamayyar wanda yake yi wa waƙa ta hanyar ayyana wasu abubuwa da suka faru tsakaninsu bayan sun yi mulki shekara takwas daga ƙarshe suka samu rabuwar jam’iya. Haka kuma ya bayyana wasu raɗe-raɗin da ake yi cikin gari na cewa shi jagoran mai mulki ya ce sai ya tuɓe sarkin garin daga karagar mulki. Wannan bayani da ya kawo ƙarara za a fahimci da waɗanda ake wa zambo.

Haka kuma a wani ɗan waƙar yake cewa:

Jagora: A yanke mutum a yanke dabba,

            Don tattalin baƙin tsahi,

            Don a hau kujerar mulki.

Yara:   In lokacinka ya ƙare,

           Tsahinka dun na banza ne.

 

Jagora:  wawa

Yara:    In lokacinka ya ƙare

            Tsahinka duk na banza ne,

 

Jagora: Saga!

Yara:    In lokacinka ya ƙare,

            Tsahinka dun na banza ne.

 

          A wannan ɗan waƙar, mawaƙin ya yi zambo ne a kan wani shugaba wanda al’ummar garin ke zarginsa da yin tsafi domin ya samu mulki. Shi ne mawaƙin ke cewa in lokacinka ya ƙare tsafinsa duk na banza ne bai tasiri.

          Haka kuma a cikin wani ɗan waƙa ya ƙara da cewa:

Jagora: An tsai da wane takarar gwamna,

             Kare mai baƙin jini da yawa,

Yara:    Du inda ya bi ya hurce,

             ‘Yan yara na yi mai yihu

 

Jagora:  Yihu kare

 

          A nan Ɗanba’u ya yi amfani da wasu abubuwa da suke faruwa ga wannan ɗan takara cewa magoya bayan wannan jam’iyar sun camfa shi da cewa baƙin jini gare shi ba su son sa a canza shi. shugabansu ya nuna sai shi, shi ne Ɗanba’u ke kira kare mai baƙin jini da yawa ma’ana a jam’iyarsa ma ba a son sa balantana ‘yan adawa sai ya siffanta shi da kare kasancewar kare bai da farin jini ga yara, duk inda suka gan shi ƙaryarsa ta ƙare, sai jifa. A nan kai tsaye za a iya fahimtar da wanda ake yi wa zambo, wato abokin takarar wanda yake yi wa waƙa kuma ya kira shi kare domin ya ƙara wulaƙanta shi da rage ƙimarsa a idon jama’a.

          A wani ɗan waƙa cewa ya yi:

Jagora: Ina ɗan buga-buga wane?

            Ya leƙa Gabas ya leƙa Yamma,

            Ya leƙa Gusun ya leƙa Arewa,

            Kullum wurin munahucci,

            Ba Sakkwato noz ba da Sakkwato Sawuz,

Yara:   Ko Isa mun hi ƙarhinka,

 

Jagora: Wawa,

Yara:    Ko Isa mun hi ƙarhinka.

 

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u na yi wa jagoran jam’iyar adawar wanda yake yi wa waƙa zambo lokacin da yake shige-shige domin ya koma jam’iyar da ke mulkin ƙasar don su haɗe su samu nasarar lashe zaɓe daga ƙarshe dai bai samu nasara ba. Yana sukar su cewa ba su da kowa shi adda mutane. Shi ne mawaƙin ke cewa ba Sakkwato Noz ba da Sakkwato Sawuz, ko a garinsu Isa sun fi ƙarfinsa.

          Waɗannan bayanai da mawaƙin ya kawo tare da ambata sunan garin wannan mutum ya bayyana wanda ake wa zambo kai tsaye.

A wani ɗan waƙar yake cewa:

Jagora: Kowa taso tare da manya,

            Ka san yana da tarihi,

            Don haka manya sun ka gaya mini,

Yara:   Danginsu Maguzawa ne.

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa jagoran jam’iyyar da ke adawa da wanda yake yi wa waƙa zambo ta hanyar raɗe-raɗin da ke yawo cikin gari cewa asalinsu Maguzawa ne, wannan ya faru ne lokacin da ya fito takarar gwamna domin a sa mutane su ƙyamace shi. shi ne a nan Ɗanba’u yake sukar sa da wannan kalmar ta Maguzanci. Har yake ƙara tabatar da abin, da ƙara masa gishiri cewa manya ne suka faɗa masa. A nan wannan kalmar ta Maguzanci ta bayyana wanda yake yi wa zambo.

          Haka kuma a wani ɗan waƙar yake cewa:

Jagora: Ku ƙara shiri in za ku shirawa,

            Ku ja ɗama in za ku shirawa,

           An ce mahaukaci ya rantce,

           Ya shedi ba ya kaffara,

           Sai ya yi gwamna Sakkwato binni,

           In kunka yarda yai gwamna,

Yara:  Irin ta dauri ta dawo,

           Har yau muna cikin ƙangi.

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa wani ɗan siyasa zambo a kan ɗabi’a shi ta rantsuwa musamman a wurin kamfe. Sau da yawa idan ya je kamfen yakan yi rantsuwa a cikin jawabansa, kusan kowane ɗan gari ya san shi da wannan ɗabi’ar. Wata rana a garin Wamakko wajen ƙaddamar da ɗan takararsu, al’umma sun taru ga kafafen watsa labarai na jiha da na ƙasa da na ƙasashen waje irin su BBC da ƁOA da makamantansu ya yi rantsuwa cewa ko kansila abokan hamayya ba za su ci ba balle gwamna. Shi ne Ɗanba’u ke yi masa zambo ta hanyar ɗabi’arsa ta rantsuwa domin jama’a su fahimci da wanda yake.

          Haka kuma a cikin wani ɗan waƙar ya ƙara da cewa:

Jagora: Mun san masu takarar gwamna,

            ‘yan takara zama mun san su,

            Yan shaye-shaye mun san su,

             Mun bar wane ɗan wiwi ne,

Yara:    Can niga ganai cikin lungu,

            Ya laɓe ana yi mai moli.

 

          A nan Ɗanba’u yana yi wa wasu ‘yan takara zambo ta hanyar bayyana wata ɗabi’a ta shaye-shaye da wani ɗan takara yake da ita. Wannan ɗabi’a ce da kusan kowa ya san wannan ɗan takarar. Shi kuma ɗan takarar guda wanda ya kira ɗan takarar zama shi kuma jam’iyarsa ba ta da ƙarfi ko mazaɓarsa ba ya iya ci balantana ya ci zaɓe.

Haka kuma duk a cikin wannan waƙar ta Gwamnanmu mun yi mun ƙare yake cewa:

Jagora: Yanzu kowa ka cin amana jama’a,

             A kwan a tashi Ɗanba’u,

             Sai ka ganai cikin tarko,

             Tarkon da ba ya hishe shi,

             Ji wanda a cikin jama’a tai,

            Sai ga shi yanzu ya bar su,

            Waɗanga nan da ya samu,

            Ya biɗo abara don ya raba musu,

Yara:   Sai ga abarba ta tsutsu.

 

Jagora: Da ya biɗo abarba don ya raba musu,

Yara:   Sai ga abarba ta tsutsa.

 

Jagora: Sakkwato mun canza musu suna,

            Ba ‘yan abarba as sunansu ba,

Yara:  Yan tukuwa ɗiyan ɗiɗi.

 

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa wani jagoran siyasa zambo da magoya bayansa ta hanyar sukar jagoran da ke cin amanar jama’a a cikin jagorancinsa kuma duk mai cin amanar jama’a sai ya shiga cikin tarko kuma tarkon da ba ya fita. Shi ne Ɗanba’u a cikin zambo yake nuna amanar da ya ci ta jama’arsa ma’ana yana cikin jam’iyar da aka zaɓe shi shekara takwas yana mulki cikinta amma yau ga shi ya fita ya ɗauko wata jam’iya mai alamar abarba. A nan kai tsaye za a fahimci da wanda yake. Haka kuma ya kira ‘yan jam’iyya mai alamar abarba da suna ‘yan tukuwa ɗiyan ɗiɗi. Ɗiɗi sunan wata mahaukaciya ne.

A waƙar Dr. Samaila Sambawa mai taken:

   Amshi:  Yaro ya ja maka a karya,

        Ɗan takarar gwamnan Kebi,

        Dr Sama’ila Sambawa.

 

          A cikin wannan waƙar Danba’u ya yi amfani da zambo a ɗiyan waƙoƙi da dama kamar haka:

Jagora: Jahar Kebbi ba wargi ce ba,

  Kuna da ɗinbin al’umma,

  Ku zaɓi mutum cincimtace,

  Irin Sama’ila Sambawa,

  Don kar ku yarda da jemage,

  Ko yaushe kai nai soke yake,

Yara:   Ba za ya yarda da kowa ba.

 

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya jefi tsuntsu biyu da dutsi ɗaya. Ya yi amfani da salon jan ra’ayi ta hanyar yabon al’ummar Kebbi sannan ya tallata ɗan takararsa, kuma ya soke abokin hamayyar Sambawa inda ya kira shi jemage. Jemage wani ƙazamin tusntsu ne da ke kashi a baki kuma duk inda yake wurin bai shaƙuwa kuma jemage bai da farin jini ga mutane. Ya kuma siffanta shi da wata mugunyar ɗabi’a ta soke kai, Bahaushe na da tunanin duk mai yawan soke kai mugu ne kuma mugu bai cika yarda da mutane ba. A nan kusan kowa ya san da wanda ake wato shi ne abokin takarar Sambawa.

A wani ɗan waƙar kuma cewa ya yi:

Jagora: A Jahar Kebbi kowa ya waye,

             Ba su koma zaɓenka ɓarawo

            Ya kwashe kuɗin talakawanai,

            Ya je ƙasar waje ya ɓoye,

Yara:    Har na ji mutane suna hwaɗin

            Olle raga muna nerori.

 

          A nan zambon ƙarara yake domin abokin takarar Sambawa an zaɓe shi a karo na farko a matsayin gwamna yanzu kuma a karo na biyu ne za su kara da Sambawa. Shi ne Ɗanba’u ke cewa al’ummar Kebbi sun waye, ma’ana sun gane ba su koma zaɓensa. Sun fahimci ɓarawo ne ya kwashe kuɗinsu ya je ƙasar waje ya ɓoye. Wai a kan tsananin yawan kuɗin da ya sata har ya ji mutane suna faɗin olle raga muna nerori. Olle a harshen Yarbanci na nufin ɓarawo. A daidai wannan lokacin ana raɗe-raɗin cewa an kama gwamnonin Sakkwato da Kebbi da Zamfara da kuɗaɗe a ƙasar waje. Shi ne Ɗanba’u ya yi amfani da wannan raɗe-raɗin ya gina zambo.

Haka kuma a wani ɗan waƙa Ɗanba’u cewa ya yi:

Jagora: Mulkinka wane mulkin banza ne,

            Mulkinka ba ya da tasiri,

            Tun randa wane ya zam gwabna,

            A jahar Kebbi kowa na kuka,

            Talakawa sun damu da kai,

            Na ji suna roƙon Allah

Yara:   Yada munka ga hwarkon mulkinka,

            Ya Allah gwada muna ƙarshe nai.

          A wannan ɗan waƙar ba a buƙatar wani dogon bayani domin an fito da hoton wanda ake wa zambo ƙarara ma’ana an ambaci muƙaminsa  wato gwamna kuma kowa ya san shi ne abokin hamayyar Sambawa.

Duk a cikin wannan waƙar yake cewa:

Jagora: Wani ya ga alamun ya hwaɗi,

            Can nis same shi Ɗanwarai

            Ya ɗauko shatar babban mota,

            An shaƙe mai ita da albasa,

Yara:    Ya ce a kai mai a Ibadan,

             Can za a kai ta a saisam mai.

 

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya gina zambo ne ta hanyar yi wa abokin hamayya burga da kuma ɗebe tababa da nuna Sambawa zai sami nasara domin shi kansa abokin hamayya ya ga alamun faɗuwa shi ya sa ya raba hannu biyu domin ko ya faɗi zai ci gaba da sana’ar albasa tai. A nan kamar yadda ƙamusun Hausa na Jam’ar Bayero (2006) ya bayyana cewa: “Zambo na nufin ƙagawa mutum magana wadda za ta muzanta shi ko ɓata masa suna.” Irin wannan ne Ɗanba’u ya yi ta hanyar ƙaga wa abokin hamayyar Sambawa wanda ke riƙe da kujerar gwamna cewa an gane shi Ɗanwarai, Ɗanwarai wani gari ne kusa da Alieru wai ya ɗauko shatar babbar mota an shaƙe ta da albasa ya ce a kai mai Ibadan a sayar mai.

A wani ɗan waƙar kuma yake cewa:

Jagora: APP kun ɓata shirinku,

             Kun kada girman sarakuna,

             Ga wanda ya gadi sarauta,

             Sai ɗai ku ƙwace rawaninai,

Yara:    Ku ɗauka ku ba maginin laka.

 

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa wani wanda ya ci zaɓen gwamna a ƙarƙashin jam’iyar APP zambo ta hanyar kama sunan jam’iya ƙarara da sukar su a kan sun kada girman sarakuna ta hanyar tuɓe wani baban sarki a jahar Kebbi wanda ya gadi sarautar. Haka kuma ya soke sabon sarkin da aka naɗa ta hanyar kiransa ‘magini’ kuma ko maginin na laka. A nan abu ne a bayyane, inda gwamnatin jahar Kebbi ta tuɓe babban sarki na jahar suka naɗa wani. Shi ne Ɗanba’u ya yi amfani da shi ya gina zambonsa.

 

 

Waƙar Yusuf Musa Illela Mai Taken:

Riƙa bari wargi,

Karo da kai ba ya da daɗi,

Isuhu Musa Ciyaman,

Kai ne suka sauna.

          Wannan waƙar ita ma ba a bar ta a baya ba domin Ɗanba’u ya yi amfani da zambo a ciki inda yake cewa:

Jagora: Koma ganin bushiya a birnin Illela,

            Ƙila ko ta tahiyatta,

Yara:   Tana nan Illela,

            Don ko jiya mun ganat,

            Ga ‘yan yara ga hannu.

 

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa abokin takarar Yusuf Musa zambo ta hanyar fito da wata siffa ta ƙirar jikinsa domin ya bayyana wanda yake yi wa zambo ƙarara cewa yana da doro. Sai ya siffanta shi da bushiya domin kowa ya fahimci da wanda yake. Sannan shi kuma ya ƙara baƙanta masa rai.

 

 

Haka kuma ya ƙara de cewa:

Jagora: Duk baƙo ya shigo Illela,

            Sai ka ji ya ce,

            Garinga maye nika shakku,

            Baƙin angulu,

            Ka yi hurhura ka gama aski,

Yara:   Kai ka shafa muna lahiya,

           A bar ce muna mayu.

 

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u na yi wa wani mutum zambo a kan wani zargi da ake ma zuri’arsu da shi wato “maita”. Shi ne Ɗanba’u ya yi amfani da wannan zargin da ake yi musu ya yi masa zambo.

Haka kuma a wani ɗan waƙa yake cewa:

Jagora: Adamu Bakane,

  Ka yi dangali bana ka huta,

 Adamu Bakane,

           Mai gida baban Shehu da Inuwa,

           Yi zamannka ka huta,

           Ƙattan banzan ga masu kuri Illela,

Yara:  Ƙyale su da ‘yan yara su ka ruga musu kashi.

 

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa manya-manyan masu kuɗin Illela zambo kasancewar sun taru a jam’iya ɗaya shi kuma Adamu Bakane ɗai ne sai yaronsa guda kuma Allah ya ba su nasarar lashe zaɓe shi ne Ɗanba’u ya haɗe su duk ya kira su da ƙattan banza domin duk taronsu da dukiyarsu sun kasa cin zaɓen ƙaramar hukuma.

A wani ɗan waƙar yake cewa:

Jagora: Wanda Allah ya ba,

            A bi shi shi ad daidai,

            Waɗanda ba su buƙatak ka,

            Ga su nan sun muzanta,

Yara:   Tun da ba su da komai

            Ƙasa ga kuma ba su da kowa.

 

          A nan ya yi wa ‘yan adawar ciyaman zambo cewa sun muzanta ba su da komai. Kuma ba su da kowa dan haka tun da Allah ya zaɓe shi to abi shi shi ad daidai.

A wani ɗan waƙar ya ƙara da cewa:

Jagora: Ar! Ga wani ya yi takarab bayis,

           Ta ruhe da shi ya hwasa kuka,

           Yanzu swata yaka nema,

           Bakin dutse ka kai ka iske,

Yara:  Tun da ɗan asali ba ya kasuwanci da ƙazami.

          A wanna ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa ɗan takarar mataimakin ciyaman wanda ya faɗi zaɓe zambo ta hanyar muƙamin da ya nema wato bayis bai samu nasara ba. waɗannan kalmomi na takara da bayis ƙarara sun bayyana wanda ake wa zambo,. Haka kuma ya ƙara sukar sa da wasu kalmomi masu zafi kamar swata da ƙazami.

Haka kuma a cikin wani ɗan waƙar yake cewa:

Jagora: Buhun lalle yai kama da buhu bai yi buhu ba,

Shi buhun lalle yai kama da buhu ba yada  nauyi,

            Da ina tsoron wane, yanzu na bar tsoron shi.

Yara:  Tun da bakin garkassu munka watce musu

kaya.

 

          A nan Ɗanba’u ya yi wa wani babban mutum ɗan siyasa na garin Illela zambo ta hanyar kiransa buhun lalle. Saboda shi buhun lalle ana kiran sa buhu matsawar dai an cika shi kamar yadda ake cika buhun hatsi ko na shinkafa. Amma ba matsayinsu ɗaya ba, kuma nauyinsu da darajarsu ba ɗaya ba. Haka kuma Ɗanba’u ya ƙara fito da zambo a fili cewa: “A da ina tsoron wane” ma’ana akan kuɗinsa da sauran abin da ya mallaka dun wanda zai yi jayayya da shi zai ji tsoro. Ya ƙara da cewa: “Yanzu na bar tsoron shi tun da bakin garkarsu munka watce musu kaya.” Ma’ana a bakin garkarsu aka kashe shi zaɓe. A nan a taƙaice ya yi wa wannan ɗan siyasa zambo ne a kan gashi da girma da dukiya amma ba su amfane shi ba. duk zamansa babban jagora ya kasa cin rumfar gidansu.

Haka kuma a wani ɗan waƙa duk a cikin wannan waƙar yake cewa:

Jagora: Bambaɗawan lokal,

            Su wane sanƙira,

            Ka da ka hwaɗa Ɗanba’u,

Yara:   Wanga lokaci ba ka da ƙarhi,

 

Jagora: Da kai nike kai wane,

            Raƙumi ɗan atololo bana ina za ka da kaya?

Yara:    Za ya je ɓantala gindi,

             Inda mata suke banza.

 

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi amfani da matsayin wannan mutum ma’ana muƙaminsa na PRO ya fassara shi da bambaɗawa lokal da kuma kalmar sanƙira domin ya baƙanta masa rai tare da bayyana shi ta hanyar da kowa zai fahimci da wanda ake. Haka kuma ya ƙara yi masa zambo ta hanyar siffarsa kamar tsawonsa, da idanunsa da wuyansa za a gansu kamar na raƙumi. Shi ne ya kira shi raƙumi. Haka kuma ya yi amfani da wata ɗabi’arsa ta neman mata ya danganta shi da ɓantalagindi. A yanayin tunanin Bahaushe idan ya ce ɓantalangindi to yana nufin wurin da matan banza suka keɓanta suna holewa.

Waƙar Sarkin Yamman Sakkwato  Mai Taken: Alhaji Aliyu Magatakardan Wamakko

Ƙi sake bajini gwarzon maza,

Ali sarkin Yamman Sakkwato.

 

          A wannan waƙar Alhaji Musa Ɗanba’u ya gina turken zambo a ɗiyan waƙa a wurare daban-daban kamar haka:

Jagora: Aliyu kai ka gadi sarauta,

            Ka yi naɗi daidai da sarauta,

            Wanda duk bai gadi sarauta ba,

            Yara ko ga naɗi sai mun ganai,

Yara:   Wane naɗi nai ya cika girma,

            Wanga uban huni sai ‘yan dako.

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa wani basarake abokin hamayyar sarkin Yamma a gefen siyasa wanda aka naɗa su lokaci ɗaya zambo a kan gadon sarauta, kasancewar shi sarkin yamma ɗan gidan sarauta ne. ya gadi sarautar kuma an naɗa shi. shi kuma wanda yake yi wa zambo ba inda ya gadi sarauta kuma sarautar da aka yi masa ba a taɓa yin ta a Sakkwato ba shi aka fara yi wa ita. Shi ne yake yin zambo cewa wanda duk bai gadi sarauta ba yara ko ga naɗi nai za a gane bai gadi sarauta ba, saboda haka naɗinsa ya cika girma kamar gammo. A nan za a fahimci wanda ake yi wa zambo kasancewar bai gadi sarauta ba kuma ba a taɓa yin sarautar ba sai gare shi.

A wani ɗan waƙar yace:

Jagora: I taƙamarka Alu daidai kake,

            Taƙama sai dai ɗan sarki,

            Jan biri in dai ya yi taƙama,

Yara:   Tabbata hwadaman nan ya gani,

            Yana nuhwa ya kare geron wani.

 

          A wannan ɗan waƙar ma ya yi zambo ne a kan gadon sarauta cewa Alu ya gadi sarauta shi kuma bai gada ba. kamar dai yadda aka yi bayani a ɗan waƙar da ya gabata. Sai dai a wannan ɗan waƙar ya ƙara kawo siffar wanda yake yi wa zambo ta yadda za a ƙara fahimtar sa, ta hanyar launin jikinsa tare da danganta shi da biri don ƙara baƙanta masa rai.

Haka kuma a wani ɗan waƙa yake cewa:

Jagora: Ran Juma’a na kwan mamaki,

            An yi sarautu Sakkwato bunni,

            Mai kurin shi ad da mutance,

            An yi naɗi kowa ya watce,

            Mai jama’a ya kwashi abinai,

            Sai nib biya garkar wani sarki,

            Ni ishe ‘yan banga sun taru,

Yara:   Da haka ‘yan sholi ɗai ɗan nig gani.

 

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa wani basarake da aka naɗa su tare da Alu zambo ta hanyar wani abin da ya faru a ranar da aka naɗa sarautar bayan kammala naɗi. Da ma akwai jayayyar siyasa tsakaninsu duk da kasancewarsu jam’iyarsu ɗaya amma shi wanda ake wa zambo koyaushe yana bugun gaban cewa ya fi Alu mutane sannan kuma shi a tare da gwamna shi kuma Alu ya samu saɓani da gwamna ga shi mataimakin gwamna amma komai ba a yi da shi ta hanyar gudanar da mulki. Wannan rashin kulawar da ake wa Alu shi ya ja ra’ayin al’ummar garin suke ƙaunar sa saboda tausai, ranar naɗi bayan watsewa sai jama’a suka yi gidan Alu. Shi ne domin ya ƙara bayyanar da wanda yake, saboda ‘yan banga ke gadin gidansa, haka kuma a sashen gidansa akwai dabar ‘yan shaye-shaye babba kasancewar hukuma ba ta zuwa wurin kamun ‘yan shaye-shaye.

A waƙar jam’iyar P.D.P. mai taken

Ya ‘yan Nijieriya,

Siyasa ta tashi,

Ku dawo mu yi ƙoƙari

Mu koma PDP

 

Ita ma wannan waƙar ba a baro ta a baya ba wajen gina turken zambo kamar inda yake cewa:

Jagora: Babu mai cin bashi,

            Cikin siyasar PDP

            In kana son ka shigo

            Cikin siyasar PDP,

            Ka biya bashin banki,

            Ka je mu je tare da kai,

            Kar tafiya ta yi nisa,

Yara:   Ka je ka goga mai laɓo.

 

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa wani babban jigon siyasa na fatin da ke adawa da PDP, mai kuɗi ne kuma ɗan kasuwa ne wanda ake raɗe-raɗi a cikin gari cewa ba kuɗinsa ne yake kasuwanci da su ba, banki ne ya ba shi bashi. Shi ne Ɗanba’u yake yi masa zambo da wannan kalma ta bashi domin kowa ya fahimci wanda yake wa zambo.

A wani ɗan waƙa yake cewa:

Jagora: Ko cikin mata,

            Wance ‘yar jidalin mata ce,

             Kullun habshi takai,

             Kamar karyar zango,

Yara:    An yi an ƙare,

             Ke baƙin jidali ya hwarma.

 

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa wata mata ‘yar siyasa zambo a kan halayyarta ta faɗa da mutane musamman a fagen siyasa har ma ‘yan siyasa na amfani da ita wajen cin zarafin abokan adawa.

          Haka kuma a cikin wani ɗan waƙa yake cewa:

Jagora: Wanda duk ke kwakwa,

             Ba mutumen kirki ne ba,

Yara:    Da ɗan ƙwaya,

             Sai ɗan dara,

             Sai ko ɗan daga.

 

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa ‘yan wata jam’iya mai alamar icen kwakwa zambo ta hanyar kiran su ‘yan kwakwa, tare da zagin su da rashin kirki da miyagun ɗabi’u na shaye-shaye da caca.

A wani ɗan waƙar kuma yake cewa.

Jagora: Ashe wane barazanarka,

            Aikin banza ce,

            Ba ya da kowa,

            Garinsu koran,

            Shi ɗai ne,

Yara:   Mun ji labarin ko gidansu,

           An ce ya sai da.

          A wannan ɗan waƙa Ɗanba’u ya yi wa wani mai goyon bayan jam’iyar da ke adawa da PDP zambo ta hanyar nuna cewa barazanar da yake yi aikin banza ce saboda bai da kowa ma’ana ba ya da mata ba ya da ɗa, kuma bai da mutum ɗaya da yake a ƙarƙashinsa, ƙuri’arsa kaɗai ya mallaka. Sai ya ƙara bayyana shi ta hanyar da kowa zai fahimci shi da cewa har gidansu an ce ya sai da kuma gaskiya ne dai-dai lokacin ya sai da gidansu.

Haka kuma a wani ɗan waƙa yana cewa:

Jagora: Ga wani ɗan takara da doro,

            Abu dai zuƙui-zuƙui,

            Ke kuma bushiya ki ɓoye doronki,

Yara:    Ba ki bakin komai,

             Wurin hwarauta banza ce,

 

Jagora: Na ga baki bakin komai,

Yara:    Wurin hwarauta banza ce.

 

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa wani ɗan takara zambo ta hanyar wata halitta da Allah ya yi masa ta doro sai ya siffanta shi da bushiya kasancewar ta a dunƙule da doro da cewa a wurin hwarauta banza ce don yara ka kama ta don ba ta iya gudu kamar zomo ko kurege kuma ba ta iya tashi sama kamar tsuntsaye saboda haka shi ma kayar da shi zaɓe ba wani abu ne mai wuya ba.

A wani ɗan waƙa yake cewa:

Jagora: Bana duna baƙin kare,

             Dubara ta ƙare,

             Kai kare ɗauke ƙafarka,

             Na ga gungu ‘yan yara,

Yara: Kar su ɓata ma tsari.

 

Jagora: In kai kare  ɗauke ƙafarka,

            Na ga gungu ‘yan yara,

Yara:   Kar su ɓatama tsari.

 

          A wannan ɗan waƙa Ɗanba’u ya yi wa wani ɗan siyasa zambo a kan wata halitta da Allah ya yi masa ta launin jikinsa wato baƙi ya kuma danganta shi da kare don ya wulaƙanta shi. Duna na nufin mutum mai baƙi da yawa. Wannan kalma ta duna ita ta bayyana wanda yake wa zambo.

 

A waƙar Aliyu Magatakarda Wammako mai taken:

Ƙara shirawa,

Aliyu zaɓaɓɓen gwamna,

Mai ban tsoro magatakarda Wamakko,

Sarkin Yamman Sakkwato bai san wargi ba.

 

          A wannan waƙar Ɗanba’u ya gina zambo a ɗiyan waƙa da dama kamar inda yake cewa:

Jagora: Mugun madambaci kake Ali,

            Baba da ka tattako, ka bugi bakin dogo,

            Ya tahi ba ban kwana,

Yara:   Bar maganar guntu,

           Shi hadda ciki nai ya hude.

 

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa wasu abokan hamayyar Alu da suka sha kaye a zaɓen 2007 zambo ta hanyar faɗuwa zaɓe, tare da bayyana ƙirar halittarsu ta yadda kai tsaye za a fahimci su. Inda ya kira babban jigon da dogo shi kuma wanda jigon ya tsaisuwa takara, ya kira shi guntu. Masu waɗannan siffofin a Sakkwato ba ɓace suke ba, domin da an ce dogo kusan kowa ya san da wanda ake.

A wani ɗan waƙa kuma yake cewa.

Jagora: Waɗansu maza, sun yi rantsuwa kuma sun ƙara,

             Sun ce maka ɗan Barade ba ka zama gwamna,

             Allah ya yarda yau Alu ka zama gwamna,

             Bamaguje kai kuma ya za ka yi zancen kononka,

Yara:    Du hatcin Sakkwato kaf ba su cire mai kahwara

 

          A wannan ɗan waƙar makaɗin ya yi wa wani babban jigo na siyasa a jam’iyar da ke adawa da Alu a kan wata ɗabi’arsa ta rantsuwa musamman awajen yaƙin neman zaɓe inda yake rantsuwa cewa ba gwamna ba ko kansila jam’iyarsu Alu ba ta ci. Mai wannan ɗabi’ar a Sakkwato kowa ya san shi, haka kuma ya ƙara kiran sa da kalmar Bamaguje wadda da yawan masu adawa da shi sukan jefi shi da ita. Dalilin da ya sa ake kiransa Bamaguje shi ne Bagobiri ne saboda  irin rigimar da Usmanu Bini Fodiyo ya yi da Gobirawa a kan Musulunci.

A wani ɗan waƙa yake cewa:

Jagora: Wane Sakkwatawa sun ɗaukai mutumen kirki,

             Dab baya ya yi lalata,

             Ya tafka abin kumya.

Yara:     Dan nan daraja tai ta hwaɗi,

 

Jagora:  Mun gane shi mutumci madara ne,

             Da ya zube a ƙasa,

Yara:    Ban san wani mai kwasa tai ba.

 

          A wannan ɗan waƙar, makaɗin ya yi wa wani ɗan siyasa zambo wanda Sakkwatawa suka karɓe shi hannu biyu-biyu suka goya masa baya ya ci zaɓe har sau biyu, daga baya sai ya juya masu baya a kan wata ‘yar matsala har dattijawan garin suka roƙe shi wata alfarma domin a samu zaman lafiya a garin ya yi amfani da ƙarfin mulki ya ƙi. Daga nan su kuma suka juya masa baya wannan matsala ta yi sanidiyar faɗuwa zaɓe daga baya ya yi biɗa shiri abin ya ci tura. Shi ne Ɗanba’u ke yi masa zambo da cewa Sakkwatawa sun ɗauke shi mutumin kirki daga baya ya yi lalata, daraja tai ta faɗi don haka shi mutumci madara ne idan ya zuɓe bai kwasuwa.

A wani ɗan waƙa kuma yake cewa:

Jagora: Ji wane ɗan hwaɗin rai wai bai biɗar sanata,

            Shugaban ƙasa yaka so,

             Bana ya yi ɓakan-ɓakatantam,

             Bai yi president ba,

             Kuma nan ga jiha tai ya hwaɗi,

             Ba zama Sakkwato,

Yara:    Sai dai ya tsaya Kwatano,

          Ko kuma ya wuce birnin Ghana.

 

          A wannan ɗan waƙar zambo a fili yake ba ya buƙatar dogon sharhi. Amma a taƙaice ga al’adar siyasa Nijeriya, idan gwamna ya yi mulki a zangon na biyu ya ƙare, zai nemi kujerar sanata, shi wannan gwamna ya ƙi neman kujerar sanata sai ya nemi kujerar shugaban ƙasa bai samu nasara ba kuma ɗan takararsa na gwamna bai samu nasara ba. shi ne Ɗanba’u ke yin zambo da kiran sa ɗan faɗin rai wai bai biɗar sanata shugaban ƙasa yake so daga ƙarshe ya ƙara bayyana wanda yake wa zambo ta hanyar ambatar sunann garinsu da cewa ba zama Sakkwato, ambatar Sakkwato. Ya bayyana kai tsaye wanda ake nufi.

Haka kuma a wani ɗan waƙa yake cewa:

Jagora: Mai jamai’as siyasa,

            Bana ya hwaɗi ina magana,

            Ɗan Sakandare ya kasai,

            Ya shiga sabbatu,

Yara:   Bana ko magana tai ya noce.

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa wani ɗan siyasa zambo ta hanyar waƙar da wani makaɗi ya yi masa inda yake kiran sa mai jami’ar siyasa ƙasar ga kowa iya ta sai ya ambaci sunan wannan wanda yake wa waƙa, ya ce shi ya koya masa. Wannan kalamin da makaɗin ya yi na mai jama’ar siyasa sai ya zama sara a wannan lokaci. Shi ne Ɗanba’u ke mai da martani ta hanyar zambo cewa mai jama’ar siyasa ya faɗi ina magana? Ɗan sakandare ya kasai. Mai jama’ar siyasa a Sakkwato sananne ne.

A waƙar Tanimu Ɗangaladiman Ƙyaɗawa mai taken:

Dogo kana da shirin yaƙi,

Tanimu na Alhaji Yakubu.

          A wannan waƙar Alhaji Musa Ɗanba’u ya fito da zambo a cikin ɗiyan waƙar wurare da dama kamar haka:

Jagora: Ranar zaɓen Gada Ɗanba’u,

            Ban gani ba labari naj ji,

            Waɗansu maza sun ji azaba,

            Wani ya bar hula da agogo,

            Wani kau ya mance gilashi nai

            Wasu kau sun ɗauko ƙahwahunsu,

Yara:    Can sun ka mance kubuttansu.

          A wannan ɗan waƙa Ɗanba’u ya yi amfani da wasu abubuwan da suka faru a ranar da aka yi zaɓen ciyaman a Gada. An yi gwagwarmaya sosai kuma an samu tashin hankali bayan kammala zaɓe. Tanimun ya samu nasara sai aka fara yi wa ‘yan adawa kuwa daga ƙarshe aka biyo manyan ‘yan adawa da gudu to a nan fa wasu suka yadda hula, wasu agogo, wasu gilashi wasu a guje ba takalma. Shi ne Ɗanba’u ke yin zambo cewa ranar zaɓen Gada wasu maza sun ji azaba. Wani ya bar hula da agogo wani ya mance gilashi nai wasu ko sun hawo ƙafafunsu can sun ka mance kubuttansu. Kubuttai na nufin rufaffen takalmi na roba. A nan a Gada kowa ya san waɗanda wannan abin ya faru a kansu.

A wani ɗan waƙa kuma yana cewa:

Jagora: Ƙara hanƙuri kar ka ji komai,

            Hanƙurinka shi nak kai ka haka,

            Hak ka yi ciyaman ƙasar Gada,

            Kak kada biri sarkin ƙwalama,

            Ci ƙurgurguma a ci buzuzu,

            Nac ce biri  a yi a hankali,

Yara:   Wata ran cikinka yana ɓaci.

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa abokin takarar Tanimun zambo a kan nasarar da aka samu a kansa. Shi ne yake cewa ka kada biri sarkin kwalama. A nan ya kira shi biri ne domin a wulaƙanta shi tare da muzanta shi a idon duniya. A nan kowa ya san wanda ake wa zambo wato wanda Tanimu ya kasuwa zaɓe.

Haka kuma a wasu ɗiyan waƙa yake cewa:

Jagora: Nai roƙo Ɗanba’u wajenka Tanimun na ƙara,

            Dauda ƙiri nike kallo ka ba shi wuri nai ya dace,

            Na so a hidda ɗan gwadda mai ja,

Yara:    Mun gane bai muna alheri.

 

 

 

 

Jagora: A in kun yi mitin kuma kun ƙare,

            Don Allah kira Dauda Ƙiri,

            Ka san aikin nai dattijo,

            A ba shi babban aikinai,

            Tunda wurinai ya saba,

            A hid da wanga hwarin doki,

Yara:    Don na ga bai muna alheri.

          A waɗannan ɗiyan waƙa Ɗanba’u ya yi wa wani mai riƙe da muƙami lokal gwammen a Gada zambo ta hanyar siffar jikinsa mai launin ja ko fari inda ya kira shi da jar gwadda da kuma farin doki. Sannan ya bayyana halayarsa ta rowa tare da kawo wasu bayanai ta hanyar kawo sunan Dauda Ƙiri domin ya ƙara fito da abin fili kasancewar Dauda Ƙiri aka cire aka sa shi tare da yi wa Dauda Ƙiri roƙo cewa a maisam mai muƙaminsa a fid da wancan farin doki tun da bai masu alheri.

          A waƙar Ciyaman ɗin Shagari, Alhaji Muhammadu Galadima Horo mai taken:

Dogo kana halin kyauta,

Alhaji Ɗan’ige ɗan dattijo,

Mamman ciyaman Shagari,

          A wannan waƙar ma Ɗanba’u ya yi zambo a cikin wasu ɗiyan waƙa kamar haka:

Jagora: Na san karo da kai,

            Ba ya da daɗi,

            Kai ji wane ya sha kaye,

            Don na gane shi can malisa,

Yara:   Ya tara leda yana ƙullin magi,

 

Jagora: wawa

Yara:    Ya tara leda yana ƙullin magi,

Jagora: saga

Yara:    Ya tara leda yana ƙullin magi.

Jagora: Ka gama da tsohon kolo,

            Wane ya bar gidanai,

Yara:    An ce yanzu kulun,

             Yana loja kwance.

 

          A waɗannan ɗiyan waƙa Ɗanba’u ya yi wa abokin takarar Ɗan’ige zambo da cewa ya sha kaye, kuma an gama da shi ya kira shi tsohon kolo, sannan ya soke shi da wurin zamansa, wato loja sannan ya kira shi wawa da saga. A nan kalamun shan kaye da kuma zama loja sun bayyana wanda ake wa zambo. Domin an san wanda ya sha kaye kuma kowa ya san ya daina zama garinsu garin da ya koma akwai wata loja nan ne wurin zama nai kullum.

A wasu ɗiyan waƙa suke cewa:

Yaro: Wani ciyaman na nan mai rowa,

          Da du, ya gane ni ya sha toka,

          Wani mai idanun ‘yabin,

Yara: Kuma ya yi kan ‘yan jarirai.

 

Jagora: Ina mai idanun mussoshi,

Yara:    Kuma ya yi kan ‘yan jarirai.

 

A wani ɗa yake cewa:

 

Jagora:  Wani ciyaman ne,

             Sarkin rowa,

             Sai son a zo a yi mai waƙa,

             To ba ni yin aikin banza,

Yara:    Na daina yin waƙa kyauta.

 

Jagora:  Wawa,

Yara:    Na daina yin waƙa kyauta.

 

Jagora: Saga!

Yara:   Na daina yin waƙa kyauta.

          A waɗannan ɗiyan waƙa Ɗanba’u da yaransa sun yi wa wani ciyaman zambo ta hanyar halinsa na rowa tare da bayyana siffofinsa ta yadda kowa zai iya fahimtar da wanda ake kamar inda yake cewa mai idanun ‘yabin kuma ya yi kan ‘yan jarirai. A wani layin waƙa Ɗanba’u ya bayyana ‘yabin a karin harshen Sakkwatanci da cewa mussa (ma’ana kyanwa) ke nan shi wannan yana da irin idon kyanwa, kuma yana da ƙaramin kai kamar na jarirai. A nan sun yi amfani da nau’o’in zambo iri biyu na hali da kuma na halitta.

A waƙar ciyaman ɗin Gwadabawa Alhaji Musa Lumu mai taken:

Gwaron giwa kullun yana halin yabo,

Alhaji LumunMusa ciyaman zarumi.

          Ita ma wannan waƙar ba a bar ta a baya ba domin akwai zambo a cikinta kamar inda yake cewa:

Jagora: Ƙasar Gwadabawa,

            Mu mun yi babban arziki,

            Don mun ije kunkuru mai idanu tsatstsaye.

Yara:   Kai bari ɗan tulluƙi ba a yi komai da kai.

 

A wani ɗan waƙa yake cewa:

 

Jagora: Wane an kashe shi sai ya tcira man tcegumi

             Mai babban gaba mi gami na ni da kai?

Yara:    Ka isko ni gida ka ce za ka tungatci da ni.

 

          A waɗannan ɗiyan waƙar Ɗanba’u ya yi wa ɗan takara da Musa Lumu ya kasuwa zambo ta hanyar halitta da Allah ya yi masa inda ya siffanta halittarsa da kunkuru tare da bayyana yadda idanunsa suke da kuma yanayin ƙirar jikinsa wato ɗan tulluƙi kuma mai babban gaba tare da ambatar an ije shi da an kashe shi, tare da bayyana wani saɓani da ya faru tsakaninsu inda yake cewa ka isko ni gida ka ce za ka tungatsi da ni. Bayan kammala ɗan waƙar sai Ɗanba’u ya ce: “Ba ka faɗa da Musa Lumu shi da yak kashe ka sai Ɗanba’u da am macce.”

Haka kuma a wani ɗan waƙa suke cewa:

Yaro: Haji Ɗanba’u akwai tambaya ta ni da kai,

          Yaran Musa akwai tambayata ni da ku,

          Maroƙan Musa akwai tambayata ni da ku,

          Shin don Allah ina mai hwaɗin sai ya bugan?

          Wani ɗan kutuɓi baƙi mai idanun raguna,

          To na zage ka,

Yara/jagora: Komai kakai man sai ka yi,

Jagora: Wane yau na zage ka,

Yara:    Komai kakai man sai ka yi.

          A wannan ɗan waƙar sun yi wa wani mutum wanda saɓanin siyasa ya haɗa su zambo ta hanyar bayyana abin da ya faru tsakaninsu tare da kawo hoton sifarsa wato kutuɓi baƙi mai idanun raguna ta yadda kowa zai fahimce shi, sannan daga ƙarshe kai tsaye suka ce sun zage shi komai zai yi ya yi.

A waƙar Sardaunan Hamma’ali Malami Maigandi mai taken:

Sardaunan Hamma’ali zaki

Malami Maigandi bi da arna,

A wannan waƙar ita ma Ɗanba’u ya yi zambo a cikinta kamar inda yake cewa:

Jagora: Hamma’ali na tafi yawo,

            Ga wani nai muna kurin banza,

            Ya ce shi aka wa Sardauna,

            Sai nac ce kauce da nesa,

Yara:   Kusun kusumi ba ya kyau da sarki.

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa wani mutum wanda ya yi neman sarautar Sardaunan Hamma’ali bai samu ba. zambo ta hanyar halittarsa wato siffar jikinsa inda ya kira shi da kusun kusumi ba ya kyau da sarki. Da ya kai ƙarshen ɗan waƙar sai ya ce ana sarki babu kyau babu kyawun kama?        

A wani ɗan waƙar yana cewa:

Jagora: Cikin ‘yan sarki na Hamma’ali,

            Akwai wani sata yakai da rana

            Shi wannan ya zame muzuru,

Yara:   Yan kaji bai bari su girma.

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa wani ɗan sarkin Hamma’ali wanda a masarautar shi ne kawai bai goyon bayan Sardauna. Shi ne Ɗanba’u ke yi masa zambo ta hanyar ƙirƙiro sata ya laƙa masa domin a wulaƙanta shi a ci zarafinsa tare da baƙanta masa rai da siffanta shi da muzuru. Duk ɗan sarkin da ke jiran sarauta aka kira shi ɓarawo ai an nakasa shi. A nan kusan ‘yan Hamma’ali duk sun san ɗan sarkin da ake nufi.

A waƙar Alhaji Aliyu Magatakarda Wamakko mai taken:

Maganin wargi ɗan Garba,

Aliyu Sabon gwamnan Sakkwato,

Ba a kai ma reni ko kusa.

Wannan waƙar ita ma akwai zambo a cikinta. A cikin wasu ɗiyan waƙa kamar haka:

Jagora: Su wane sun ci amana Allah,

            Yanzu amana ta kama su,

            Sun yi gidaje gadan-gadan,

            Gahwa gidaje daidai jin daɗi,

Yara:    Ba a da dama zaunawa ciki.

          A wannan ɗan waƙa Ɗanba’u ya yi wa wasu manyan ‘yan siyasa da suka faɗi zaɓe a jahar Sakkwato, suka kasa zama garin zambo ta hanyar bayyana manya-manyan gidaje da suka yi amma ba su iya zama garin saboda baƙin ciki da kuma tsoron kada a yi musu wani abu. Waɗannan ‘yan siyasa a jahar Sakkwato sanannu ne.

A wani ɗan waƙa yake cewa:

Jagora: Wane giyam mulki ta ɗibai,

             Hay ya je Gada ya sha wallah,

             Ya ce ko hullatai ya aje ƙasag ga,

             Sai tai gwamna Sakkwato.

Yara:    Mai bundigar iskan ga talo-talo,

             Bana ya hau dokin rantsuwa.

          A wannan ɗan waƙar Ɗanba’u ya yi wa wani mai mulki zambo ta hanyar wata halayyarsa, ta rantsuwa da kuma wani jawabi da ya yi a garin Gada wurin kamfe inda yake cewa duk wanda ya tsaisuwa takara gwamna sai ya ci zaɓe. Shi ne yake danganta maganarsa da bindigar iska wato maganar banza kuma ya kira shi talo-talo kuma ya hau dokin rantsuwa.

3.7 Naɗewa

          A wannan babi an yi bayani a kan zambo tun daga asalin kalmar da ma’anarta da ire-iren zambo daga ra’ayoyin masana da manazarta daban-daban, tare da kawo dalilan da ke sa a yi shi. haka kuma an bayyana muhimmancin ko amfanin da ake samu ta hanyarsa. Daga ƙarshe an kawo sharhin zambo a cikin wasu waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanba’u Gidan Buwai ta hanyar fitowa da abubuwan da masana da manazarta suka bayyana a matsayin zambo. Haka kuma an nazarci wasu waƙoƙinsa da ke ɗauke da zambo aka kawo misalai a wurare daban-daban.

Post a Comment

0 Comments