Kundin Binciken Neman Digirin Farko (B.A Hausa) Wanda Aka Gabatar A Sashen Harsuna Da Al’adu Jami’ar Tarayya Gusau.
Taubasantakar
Bazamfare Da Badakkare (1)
NA
ABDULRAHMAN
BALA
SADAUKARWA
Na sadaukar
da wannan aiki ga mahaifina Alh. Bala Garba B.G Tsafe da fatar Allah saka masa
da alkhairi, da kuma mahaifiyata Hajiya Zulfa’u Sani Tambaya Tsafe da kuma
kakana Alh. Sani Tambaya Tsafe da Sauran ‘yan uwa da abokan arziki.
GODIYA
Godiya ta
tabbata ga Allah mai kowa mai komai da ya ba ni ikon kammala wannan bincike
cikin nasara, tare da yabo ga fiyayyen halitta Annabi Muhammad (S.A.W), tsira
da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa da Sahabbansa, da kuma
mabiyansa har zuwa ranar ƙarshe.
Ina godiya
tare da girmamawa ga Malamina Malam Aliyu Rabi’u Ɗangulbi wanda
ya taimaka matuƙa wajen gudanar da gyare-gyare na wannan
bincike da ba da shawarwari da kuma haƙuri tare da
ba da gudummuwa ta ɓangoriri mabambanta, Allah ya saka masa da
mafificin alkhairi amin.
Haka kuma ina
miƙa godiya ga shugaban sashe Farfesa Aliyu
Muhammad Bunza, Dr. Nazir Abbas Ibrahim, da sauran Malaman Sashe kamar Farfesa
Balarabe Abdullahi, Farfesa Muhammad Lawal Amin, Farfesa Magaji Tsoho Yakawada,
da Malam Musa Abdullahi da Malam Isah S. Fada da sauransu, da fatar Allah ya saka
musu da alkhairi.
Daga ƙarshe
ina miƙa godiya ga Nasiru Hassan, da Ahmad Muhammad
Kabir, da Bashar Isyaka, da Aliyu S Ibrahim, da Mustapha Sa’idu, da Abubakar
Hassan, da Nura Sani, da Hisbullah Ɗanlami, da
Amina Abubakar, da Ɗayyaba Mustapha, da
Hassan Galadima, da kuma Abdulrashid S/Pawa.
Har wa yau
ina mika godiya ta musamman ga Abbati Muhammad da ya buga wannan aiki cikin
na’ura mai ƙwaƙwalwa har ya
zuwa kammala wannan bincike. Shi ma Allah ya saka masa da alheri, amen.
0 Comments
Rubuta tsokaci.