Kundin Binciken Neman Digirin Farko (B.A Hausa) Wanda Aka Gabatar A Sashen Harsuna Da Al’adu Jami’ar Tarayya Gusau.
Taubasantakar
Bazamfare Da Badakkare (2)
NA
ABDULRAHMAN
BALA
BABI NA ƊAYA
SHINFIƊA
1.0 GABATARWA
Ƙasar
Hausa wuri ne inda jama’ar Hausawa suke zaune, kuma tana shimfiɗe ne a
Arewacin Nijeriya da kudancin Jamhuriyyar Nijar. (Adam 1978). Harshen Hausa shi
ne mazauna wannan yankin na asali, da shi suke amfani wajen tafiyar da
harkokinsu na yau da kullum. Kamar hulɗoɗin kasuwanci
da na auratayya da sauran al’amurran rayuwa.
Hausawa suna
kewaye da maƙwabta daban-daban waɗanda ba
Hausawa ba da kuma suke da nasu Harshe da al’adunsu da suke gudanar da
harkokinsu. Amma mafi yawan lokacin sukan cuɗanya da
Hausawa domin yin wasu hulɗoɗi. Wannan ne
kan haifar da shaƙuwa da fahimtar juna har wani lokaci
auratayya ta kasance tsakaninsu. A nan ne sukan koyi harshen Hausa da kuma
al’adunsu.
Hausawa dai
kamar yadda aka san su, mutane ne masu yaƙini ga duk
abin da suka sa a gabansu da sauƙin kai, sannan
an san su da rashin nuna wariya ko ƙyama ga kowa
da kowa. Hakan ya sa suka shiga cikin mabambantan al’ummomi su yi mamaya sosai
ga abokan hulɗoɗinsu da ba
Hausawaba. (Idris: 1946).
Hausawa sun
bai wa harshensu da al’adunsu muhimmanci matuƙa, addininsu
kaɗai sukan
fifita a kan harshensu da al’adunsu.
Zamfarawa
mutane ne kuma Hausawa, ma’ana su ma wani yanki ne na wata al’umma daga cikin ƙasar
Hausa. Kuma ba su da wani harshen da yafi harshen Hausa, a wurinsu. Domin da
shi suke sadarwa, da kasuwanci da sauran hulɗoɗinsu da
sauran ƙabilu daban-daban.
Zamfarawa suna
maƙwabtaka da al’ummomi daban – daban waɗanda ba
Hausawa ba. Daga cikinsu, akwai Fulani, Barebari, da kuma dakkarawa. Sai dai a
nan za mu yi bayani ne a kan wata ‘yar alaƙa da ke
tsakanin Zamfarawa da Dakkarawa, wato “TAUBASANTAKAR BAZAMFARE DA BADAKKARE.
Dakkarawa dai
kamar yadda aka sani wata al’umma ce waɗanda suke ba Hausawa
ba. Ma’ana suna da nasu harshe da suke sadarwa da shi, kuma suke gudanar da
al’amurran rayuwarsuta yau-da-kullum. Waɗannan mutane a halin
yanzu suna zaune ne a cikin jihar Kebbi a ƙaramar
hukumar mulkin Zuru. Sai dai nan gaba kaɗan a cikin wannan
bincike za mu gano asalinsu, da kuma wurin da suka fara zama, kafin su kasance
a inda suke a yau.
Dakkarawa
kamar yadda muka yi bayani a baya, su ma suna cikin maƙwabtan
Zamfarawa, kuma suna tafiyar da hulɗoɗinsu da dama
tare da Zamfarawa. Hasali ma sun cuɗanya sosai da Zamfarawa har ta kasance
waɗansu,
(Dakarkarin) sukan baro wurin zamansu na gado su dawo ƙasar Zamfara
su zauna domin gudanar da sana’o’insu. Ko kuma a sanadiyar wani dalili sai wasu
su yi ƙaura zuwa Zamfara, haka kuma auratayya kan
kasance a tsakaninsu da Zamfarwa. Dalilin haka ta sanya wasu al’adu da ɗabi’un waɗannan
al’ummomi suka cuɗanya dana
juna. Sai dai na Zamfarawa su suka fi rinjaye domin kuwa wasu daga cikin Dakarkarin
sukan bar nasu ne su ɗauki na Hausawa, kamar aure, Dakarkaru sun
bar al’adarsu ta noma kafin ka auri mace, inda suka ɗauki ta
Hausawa kawai sadaki ake biya ba sai an yi noma ba.
Shi wannan
bincike ya yi ƙoƙari ne ya
binciko yadda taubasantaka ta samo asali ko tushe a tsakanin Bazamfare da
Badakkare (Zamfarawa da Dakkarawa), ta yadda za a fito da komai fili, ta hanyar
bayyana duk wata hanya da taubasantakar ta afku a tsakanin waɗannan
al’ummomi guda biyu. Haka kuma wannan bincike zai bai wa manazarta dammar
dubawa tare da aunawa don tabbatar da duk wani hasashe da aka yi a kan wani abu
da wataƙila zamani ne ya kawo shi, ta yadda har
wannan taubasantaka ta yi tasiri a tsakanin Bazamfare da Badakkare.
1.1 MANUFAR
BINCIKE
Wannan
bincike na nufin nazarin dalilan da suka haddasa taubasantakar da ke tsakanin
waɗannan
al’ummomi guda biyu, wato Zamfarawa da Dakarkari.
Hausa na cewa
“ruwa ba ya tsami banza” ko kuma su ce “Ba banza ba kuɗa kabin
walki”. Ma’ana ba haka ƙaddam, al’ummomi suke
zama taubasan juna ba, a a dole sai da wasu dalilai ko faruwar wani abu a
tsakanin waɗannan
jinsunan al’ummomin guda biyu, sannan a samu taubasantakar a tsakaninsu.
Wannan
bincike ya ɗauki aniyar
yin nitso a cikin waɗannan al’ummomi domin yin farautar gano
asalin taubasantakar da ke tsakaninsu. Don haka aikin zai dubi wasu muhimman
abubuwa, kamar asalin kowace al’umma a cikinsu da alaƙar da ke
tsakaninsu. Sai kuma asalin taubasantakarsu, wato inda ta samo asali. Sannan a
kawo cikakken bayanin tasirin taubasantakar Bazamfare da Badakkare ga raya
al’adun Hausawa da harshensu.
Daga nan sai
binciken ya samar da abubuwan amfani kamar su shawarwarin da ke wanzar da haɗin kan ƙasa,
wato a tsakanin ƙabilu daban-daban na Najeriya.
1.2 DALILIN
BINCIKE
Dalilin
gudanar da wannan bincike shi ne, domin mu gano ko mu zaƙulo asalin
yadda Bazamfare da Badakkare suka zama taubasan juna, wato musan asalinta da
kuma dalili ko dalilan da suka haifar da taubasantakar. Domin kuwa ita
taubasantakar tana matuƙar yin tasiri a
tsakanin al’ummomin da suke taubasan juna. Saboda duk irin yadda taubashi yake
cikin tsananin baƙin ciki, ko damuwa ko yake cikin yanayin
fushi da zarar yaga taubashinsa dole ya yi ƙoƙarin
ɓoye wannan
yanayin da yake ciki, tare da sakin fuska don taƙaita zolayar
da za ya yi mashi.
Haka zalika
taubasantaka tana ƙara ɗanƙon
zumunci a tsakanin taubasai, da kuma cusa musu soyayyar juna. Don haka yana da
kyau matuƙa jama’a su fahimci taubasantakar da ke
tsakanin waɗannan
al’ummomi guda biyu.
Wannan yana
daga cikin dalilan da suka sa na yi tunanen aiwatar da aikin binciken domin
jama’a su fahimci yadda Zamfarawa suka zama taubasan Dakarkari.
1.3
FARFAJIYAR BINCIKE
Wannan
bincike zai taƙaita ne a kan taubasantakar da ke tsakanin
Zamfarawa da Dakarkari. Ma’ana dai za a kalli al’ummar Dakarkari tun daga inda
suka samo asali tun fil’azal da kuma yadda suka haɗu da
zamfarawa, ta fuskar zamantakewa da junansu.
Haka kuma
suma maƙwabbtansu Zamfarawa, za a dubi nasu asalin da
kuma gano irin abubuwan da suka yi tasiri ko suka faru a tsakaninsu da
taubasansu, ko ince maƙwabtansu (Dakarkari),
da kuma zaƙulo abin da da ya haifar da taubasantakar da
ke tsakaninsu. Sannan kuma musan yanayin ko yadda ƙasar Zamfara
take tun wancan lokacin har zuwa yau.
Lokacin da
wannan bincike zai ɗauka shi ne mafi a’ala domin a wannan tsakani
ne ingantattun bayanai kan samu ko dai a rubuce ko ta hanyar samun wani mutum
wanda ya san tarihin abubuwa ko ma wanda yak e da haƙiƙanin
yadda al’amarin yake faruwa a ƙasar Zuru.
Misali yankin wasagu da Fakai waɗanda suke wurare ne da Dakarkari suka
mamaye ko suke zaune. Wato a nan ne ake tsammanin a sami cikakken tarihin
Dakarkari domin aiki da shi. Daga nan kuma sai a fito da asali ko dalilin yadda
taubasantaka ta samu a tsakanin Bazamfare da Badakkare.
Haka kuma su
ma maƙwabtansu, wato Zamfarawa za a iya samun
tarihinsu a rubuce ko kuma a sami wani mutum masanin tarihi sosai, musamman
wanda yake zaune a ƙasar Bukkuyum ta
cikin ƙaramar hukumar mulki ta Bukkuyum a jihar
Zamfara. Ko kuma a samu mutumin da ya san tarihin abubuwan da suka wakana,
wanda ya ke zaune a ƙasar Zurmi, ta jihar
Zamfara. A haka ne za a iya samun damar sanin asalin taubasantakar da ke
tsakaninsu.
Dalilin da ya
sa na kawo ƙasar Bukkuyum da Zurmi na Jihar Zamfara, shi
ne, wasu masana ko ince manazarta, suna ganin cewa can ne asalin Dakkarawa ya
fito. Binciken zai taƙaita a waɗannan yankuna
na jihar Kebbi da Zamfara domin a nan ne waɗannan
al’ummomi suke zaune.
1.4 HANYOYIN
GUDANAR DA BINCIKE
Domin ganin
haƙa ta cimma ruwa, wato mu ga cewa wannan
bincike ya tabbata, kuma da ganin cewa ya samu karɓuwa a wurin
manazarta ko makaranta, za a yi amfani ne da wasu dabaru don gudanar da wannan
bincike har a ga an tabatar da cewa, an kammalashi.
Da farko dai
za a duba bugaggun littattafai da mutane da dama suka rubuta masu alaƙa
da aikin. Sannan za a nemi kundayen bincike na neman digirin farko wato (B.A)
da na biyu (MA) da kuma na uku (PhD) don a sami nasarar kammalawa wannan
bincike cikin sauƙi.
A lokacin da
ake gudanar da wannan bincike, za a ƙara himma
wajen halartar ɗakunan karatu
daban-daban, na jami’o’i da na kwalejojin ilimi da makamantansu.
Haka zalika
da mujallu da takardun da aka gabatar na ƙara wa juna
sani a tarurukan ƙarawa juna sani daban-daban da suka shafi
tarihi da al’adu na al’ummomi, musamman Hausawa. Haka kuma za a kai ziyara wasu
garuruwa da ake sa ran can ne asalin wurin da ƙabilun
Zamfarawa da Dakarkari suka fara zama ko ɗaya daga cikin ƙabilun
suka fara zama, domin ana sa ran cewa ba za a rasa waɗansu alamomi
ko waɗansu mutane
waɗanda suka yi
zamani tare da su ba. Idan har aka samu irin waɗannan mutanen
to za a yi fira da su don a sami wasu muhimman bayanai, waɗanda za su
iya zama ginshiƙai na tattara bayanai a wannan bincike.
Biyar waɗannan hanyoyi
da na zayyana a baya, wajen gudanar da wannan bincike, za su taimaka matuƙar
gaske wajen kafa hujjoji gamsassu, waɗanda za su taimaka
don binciken ya samu karɓuwa a wurin manazarta da masana
tarihi.
1.5
MUHIMMANCIN BINCIKE
Duk wani abu
da ake bincike ko ake gudanar da bincike a kansa, to tabbas wannan abun yana da
matuƙar muhimmanci. Domin kuwa ana yin bincike ne
don a gano, ko don a zaƙulo wani abu da ba a
san shi ba. Kuma ana da buƙatar a san
shi, domin muhimmancinsa ko tasirinsa ga al’umma.
Shi ma wannan
bincike da ake gudanarwa, yana da irin nashi muhimmanci ga al’umma, musamman ɗaliban ilimi,
dalilina na faɗar haka shi
ne, muddin aka samu damar kammala wannan bincike, kuma aka cimma abin da ake
so, to ina sa ran binciken zai iya zama wata yar fitilar haskawa ga duk wani ɗalibin ilimi
da zai gudanar da bincikensa a wani fanni mai alaƙa da wannan
aiki ko makusancin wannan fanni.
Wannan
bincike yana da muhimmancin gaske, kuma zai taimaka sosai wajen sanin asalin
tarihin waɗannan
al’ummomi guda biyu wato Zamfarawa da Dakkarawa dangane da abin da ya shafi
taubasantakar da ke tsakaninsu.
Yana da kyau
a ce an san muhimmancin kalmar taubasantaka, da kuma irin abubuwan da ta ƙunsa
ba wai dole sai wannan taubasantakar da ke tsakanin waɗannan ƙabilun
guda biyu (Bazamfare da Badakkare) ba.
Saboda haka
wannan bincike ya ɗauri aniyar yin nitso a cikin waɗannan
al’ummomi guda biyu domin ya gano waɗansu abubuwa masu muhimmanci waɗanda ya
kamata a ce an sansu, kuma an san asalinsu da abin da ya assasa alaƙarsu
kamar irin tarihinsu da yadda alaƙa ta ƙullu
a tsakaninsu. Haka kuma da sanin abin da shi ne musabbabin yin wannan bincike,
wato “Taubasantakar da ke tsakanin Bazamfare da Badakkare.
1.6 HUJJAR
CIGABA DA BINCIKE
Hujjar cigaba
da gudanar da wannan bincike shi ne domin zaƙulo asali ko
tarihin yadda taubasantakar Bazamfare da Badakkare ta samo asali da kuma sanin
silar abin da ya haifar da taubasantakar a tsakanin waɗannan
al’ummmi guda biyu (2) (wato Zamfarawa da Dakkarawa). Dole sai an bi ta hanyar
yin amfani da tarihin waɗannan al’ummomi ne guda biyu, sannan
za a iya gano tushe ko asalin yadda taubasantakar ta samu a tsakaninsu. Saboda
shi tarihi wani muhimmin abu ne wanda yake ƙunshe da
abubuwa mabambanta game da al’ummomi tun daga asalinsu da yadda suke gudanar da
rayuwarsu da bukukuwansu, da suturarsu. Hakan zai tabbatar mana da cewa duk
wata al’umma ta duniya wadda ta isa, kuma ta ke ji da kanta, to idan aka
bincika za a ci karo da tarihinta, ya sami canje-canje daga nan zuwa can.
Zamfarawa da
Dakarkari ba a ɓoye suke ba a
wannan ƙasa tamu Nijeriya, amma rubuce-rubuce a kan
waɗannan
al’ummomi guda biyu ba su yawaita ba sosai kamar yadda ya kamata. Wannan shi ne
hujjar da ya sa zan cigaba da wannan bincike. Saboda a ɗan wannan
tsakanin ne in gantattun bayanai za su samu. Wato za a samu bayanan ne ko dai a
rubuce ko kuma ta hanyar samun wani mutum wanda ya san tarihin abubuwa ko ma a
samu mutumin da ya san haƙiƙanin
yadda al’amura suka faru a ƙasar Zamfara
da Kebbi; misalin yankin Bukuyum da Zurmi, nan ne ake sa ran asalin Zamfarawa
waɗanda suka zauna
tare da Dakarkari suka fito, sannan sai a samu wani wanda yake da haƙiƙanin
tarihin al’amarin da ya faru a ƙasar Zuru.
Misali, yankin Wasagu da fakai domin wurare ne da Dakarkari suka mamaye. Don
haka waɗannan wurare
da aka ambata ake tsammani a sami cikakken tarihin waɗannn
al’ummomi guda biyu, wato Zamfarawa da Dakkarawa. Daga nan kuma sai a taɓo inda
taubasantakar ta su ta samo asali, tare da gano ko sanin abin da ya haifar da
ita. Babbar hujjar da ya sa za a yi aiki tuƙuru wajen
sanin ko gano tarihin kowace al’umma a cikin waɗannan al’ummomi
guda biyu, shi ne, saboda kasancewarsu al’ummomi ne masu matuƙar
muhimmanci a tarihin ƙasar Hausa. Don haka
yana da kyau matuƙa jama’a su fahimci ko su san tarihinsu da
kuma abin da ya haifar da taubasantaka a tsakaninsu. Kamar yadda aka san waɗansu abubuwa
dangane da sauran al’ummomi irinsu yarbawa da al’ummar Ibo da Fulani da sauran
ire-irensu. Saboda haka wannan bincike zai mayar da hankalinsa wajen fito da
asalin taubasantaka dake tsakaninsu.
1.7 BITAR
AYYUKKAN DA SUKA GABATA
Gano ko binciko
ko bayyana wani abu da ke tsakanin al’umma daban-daban ba wani sabon abu ba ne
domin masana da manazarta da dama sun daɗe suna aiwatar da
ayyuka wajen binciko wani abu da suke son tabbatarwa akan wasu al’ummomi.
Masana da
dama sun yi rubuce-rubuce masu yawa a kan kowace al’umma, daga cikin waɗannan
al’ummomi guda biyu (Zamfarawa da Dakkarawa); misali. Adam (1978) “Asalin
Dakarawa da Dukkawa iri ɗaya ne da na al’ummar muryam”, saboda
suna ganin cewa al’ummomin Dakarawa da Dukkawa sun faru ne a lokacin da waɗansu suka yi ƙaura
daga ƙasar Hausa, suka zauna a wani wuri da babu
kowa, a tsakanin Yawuri da Zamfara, suka rasa harshensu na Hausa suka ƙirƙiri
wani sabon harshen da hanyoyin gudanar da rayuwarsu.
Shi kuma
Robins (1967) cewa ya yi a kan tarihin dangantakar harsuna ko ƙabilu
da suke ‘yan tushe ɗaya da marubutan turai suka yi, ya fara ne
daga Dante (1265 – 1321).
Mainasara S.
(2001) Bautar Magiro a Zamfara; daga ciki akwai inda ya ɗan yi tsokaci
a kan Zamfarawan asali ya ce “Zamfarawan Asali sun fito ne daga Dutsi a ƙaramar
hukumar mulki ta Zurmi, kuma su ‘ya’ya ne ga Dakka (mai yawon farauta). Don
haka Dakka mahaifi ne ga Zamfarawa.”
Shi ma Umar
Muhammad (2010), ya yi rubutu ko bincike a kan “Tau basantakar wamakko da Yabo,”
a kundin digirinsa na farko (BA), in da ya bayyana waɗansu muhimman
dalilan da suke haifar da taubasantaka a tsakanin al’ummomi, ya ce: Daga cikin
abubuwan da suke haifar da taubasantaka akwai, zumunci. Misali a samu wa da ƙanwa
‘yan ɗaki ɗaya, idan suka
yi aure suka haifi ‘ya’ya, to ya’yan nan nasu za su zama taubasan juna saboda
kasancewar su ‘yan wa da ‘yan ƙanwa. Irin
wannan taubasantaka al’ada ta haifar da ita.
Ya ƙara
da cewa akwai wasa ta taubasantaka tsakani jika da kaka. Irin wannan wasan ba a
cikin gida kawai take tsayawa ba, wani lokaci takan zama silar haɗa al’ummomi
su zama taubasan juna.
Abdullahi M.
(2002) ya yi aiki a kan tasirin magungunan Gargajiya na Hausa a kan na
Dakarkarin ƙasar Zuru, ya yi taƙaitaccen
bayani a kan Dakarkarin kasar Zuru. Ya ce “anihin Dakarkarin ƙasar
Zuru hijira suka yo daga ƙasar Katsina,
har ana kiransu da wani suna “Mutanen Riɓah” dalilin kiransu
da wannan suna shi ne, lokacin da suka baro Katsina, sun zauna ne a wani gari
ko ƙauye mai suna Ribe, a arewacin Zamfara. Don
haka ba a rasa wata alaƙa tsakaninsu da
Zamfarawa.
Muhammad
(1982) a cikin wata takarda da ya gabatar a jami’ar Bayero da ke Kano, ya yi
magana a kan “Haɗuwar
Dakarkari da Hausawa,” ya ce Huɗɗar kasuwanci ita ce ta haɗa alaƙa
tsakanin Dakarkari da Hausawa, musamman Katsina da Zamfara da ƙasar
NUPE. Ya ƙara da cewa, Katsinawan Laka sun fara zama a
kongon wasagu daga nan suka zarce zuwa Wasagu kai tsaye.
Su kuma P.G.
da Harris (1938) sun ce “Zamfarawan Dutsi a gundumar Zurmi ‘yan uwan Dakarkari
ne, su kuma Dakarkarin jikoki ne ga Dakka, wato mai yawon farautar nan da aka
faɗi a ƙasar
Bukuyum.
Bugaji
(1985); cewa ya yi “Asalin Dakarkari ya fito ne daga ƙasar
Bukkuyum.” Inda ya ƙara da cewa, a wancan
lokacin Dabai daji ne, wanda ya ke cike da itatuwa da kuma namun daji. To sai
mafarauta suka fara zuwa suna shiga don yin farauta. Lokacin da wannan mutumin
ya zauna sai wurin ya zama gari. Bugaje ya cigaba da cewa, har zuwa farkon ƙarni
na goma sha tara, sarkin Bukuyum shi ke naɗa hakimi da
Dabai wanda daga baya aka fi sani da suna marafan Dalai (Kasancewar asalinsu
Bukkuyum ne).
Haris (1938)
ya ce su Dakarkari sukan yi wa yaransu maza tsage bayan wata uku da haihuwa,
mata kuma shekara huɗu. Amma ko a cikin Hausawa, wani lokaci sai
bayan mutum ya girma ne akan yi masa tsaga. Amma an fi yin haka lokacin da
mutum yake jinjiri domin ya fi sauƙi, kuma an
tabbatar ya fi saurin warkewa.
Idrisu (1946)
ya ce “akwai auratayya a tsakanin Zamfarawa da Dakarkari tun kafin zuwan
Turawan mulkin mallaka, har ma daga cikin iyalan Sarkin Zuru da na Dabai akwai
Hausawa. Ya yi wannan bayani ne a wurin taron ƙara ma juna
sani a jami’ar Usmanu Ɗanfodio da ke Sokoto.
Nadama G.
(1986) ya yi aiki a kan “yanayin ƙasar Zamfara”
a kundin neman digirinsa na uku (Ph.D) a jami’ar Ahmadu Bello Zaria, ya ce “ƙasar
Zamfara ƙasa ce mai faɗin gaske,,
wadda take ƙunshe da al’ummomi daban-daban gami da
dajujjuka da kuma tsaunuka, ga kuma itatuwa iri iri a cikinta. Sannan kuma ƙasar
Zamfara tana da gulabe, kuma ƙasa ce mai daɗin noma, ya
cigaba da cewa ƙasar Zamfara tana maƙwabtaka da
garuruwa mabambanta misali Sokoto da Katsina da Kabi da sauran su.
Sani (1986)
“Dakarkari sun haɗu da
Zamfarawa tun lokacin da Zamfarawa ba Hausa ce harshensu ba, wanda suke amfani
da shi na asali. Ya ci gaba da cewa sun sami harshen Hausa ne a matsayin
harshen kasuwanci domin kasancewar Zamfara cibiyar kasuwanci ce kafin jihadin
Shehu Usmanu Ɗanfodiyo a ƙarni na goma
sha tara a ƙasar Hausa.
Gujiya, M.
(1987) ya ce “Ƙidayar jama’a da aka yi a can baya a ƙasar
nan ta nuna cewa, Dakarkari (wato Lele) sun fi yawa a wuraren da suka kama tun
daga peni da senchi zuwa garin zuru har Dabai da Wasagu. Amma garin wasagu ba
ya ciki. Ya cigaba da cewa” daga arewa zuwa kudu, ana samun Dakarkari tun daga
kyabo har zuwa Tadurga da bedi”.
Sakaba (1988)
“Farko zuwan maganar Alh. A ƙasar
Dakarkari a Zuru an fara ɗora tubalin Kira ga al’umma da su
shiga addinin Kirista tun shekarar 1925. Kafin wannan lokacin Dakarkari ba su
da wani addini sai ‘yan tsafe - tsafe.
Kabiru (1988)
“Tarihin ƙasar Zamfara da albarkatunta a kundin neman
digirin farko a jami’ar Usmanuu Ɗanfodiyo da
ke Sokoto.” Ya ce, “ƙasar Zamfara ƙasa
ce mai ɗimbin tarihi,
ga kuma tarin albarkatun ƙasa a
cikinta. Haka kuma ƙasa ce mai hulɗar kasuwanci
da ƙabilu daban-daban misali tarihi ya nuna cewa
Zamfarawa sun yi huɗɗar kasuwanci da ƙabilar
Dakarkari tun kafin ƙasar Zamfara ta samu
‘yancin kanta na zama (jaha).
Isma’ila
(1989) “Sana’o’in Zamfarawa jiya da yau, a cikin wannan bincike da ya yi, ya yi
ɗan tsokaci a
kan asalin Zamfarawa, inda ya ce “asalin Zamfara sun fito ne daga ƙasar
Bukuyum, kuma suna da alaƙa mai ƙarfi
tsakaninsu da Dakarkari. Domin bincike ya nuna cewa asalin Zamfarawa kakanni ne
ga Dakarkarin asali, domin tarihi ya nuna cewa jikan “Dakka” ne asalin
Dakarkari”.
Haruna (2002)
“Tasirin al’adun Hausawa aan na Dakarari” a kundin neman digiri na biyu (MA) a
jami’ar Bayaro da ke Kano. “Ya yi bayani sosai kan ƙabilar
Dakarkari mazauna ƙasar Zuru, kamar
yadda ya ce “Mafi yawan Dakarkari mazauna ƙasar Zuru,
masu tsawo (Dogaye) ne waɗanda ba su faye ƙiba ba. Suna
da babban kai da haƙora masu kaifi da
tsini. Ya cigaba da cewa mafi yawancin Dakarkarin manya da ƙanana,
maza da matansu ba su da ƙyuya ko
kasawa ga dukkan al’amura. Sannan ya ce; “Dakarkari musamman mazauna ƙauyuka
mutane ne marasa tsafta ga jiki da kuma ta gidaje. Ba su da girman kai mutane
ne masu ladabi da biyayya.
Ni kuma a
wannan aiki nawa, zan yi shi ne a kan taubasantakar da ke tsakanin Bazamfare da
Badakkare, domin kamar yadda bayanan masana tarihi suka gabata, ya nuna cewa
taubasantakar da ke tsakanin waɗannan jinsuna guda biyu ta fi rinjaye
ne a kan jikoki da kakanni (jika da kaka) ma’ana Zamfarawa su ne kakannin
Dakarkari, kamar yadda nan gaba za a tabbatar da hakan a cikin wnanan bincike.
1.8 NAƊEWA
Babban abin
buri ga kowane bincike shi ne samun nasara, haka nike fata in ga cewa na samu
nasarar kammala wannan bincike, duk da cewa, yanzu aka fara sa hannu. Amma
Hausawa sun ce “sannu – sannu kwana nesa.
Binciken ya ƙunshi
babi biyar ne waɗanda a
cikinsu ne manufofin gudanar da aikin suka fito har “haƙa ta cimma ruwa.”
Wannan Babi shi ne na farko da ya ƙunshi bayanan
ayyukan da suka gabata, bayan an kawo kyakkyawar shimfiɗa don gudanar
da aikin, sai hujjar cigaba da bincike da bayanan muhimmancin bincike. Sai
farfajiyar bincike da kuma dalilin bincike.
Haka kuma da manufar bincike da hanyoyin bincike, waɗannan su ne
abubuwan da aka tattauna a wannan babi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.