Ticker

6/recent/ticker-posts

My Journalistic Work Sample - Zubairu Ahmad Bashir (Kasarawa)

VISION FM 92.5 MHZ SOKOTO

 

TASKAR VISION RADIO SRIPTS

PRODUCER: ZUBAIRU AHMAD BASHIR (KASARAWA)

 

17/11/2020              VFMNEWS               TASKA

CUE IN SIGNATURE TUNE

Taskar Vision kuke saurare daga nan Gidajen Rediyon Vision FM Najeriya, dake yada shirye shiryensu akan mita 92.1 a Abuja Babban Birnin tarayya da Katsina birnin Dikko, mita 92.5 a Jihohin Sokoto, Kano da Kaduna, a Birnin Kebbi kuwa a na sauraren Vision FM, akan mita 92.9, sai kuma mita 92.7 a jihar Gombe.

Zaku iya sauraren Vision FM kaitsaye a koda yaushe daga ko ina a fadin duniya, ta adireshin mu na internet wato Visionfm.ng

Hakama zaku iya bibiyarmu ta shafukanmu na Facebook, Twitter, da Instagram domin tafka muhawara akan labaran da muke wallafawa, duka a Vision FM Nigeria.

CUE IN TUNE………………………………..

Masu sauraro assalamu alaikum, barkammu da warhaka Zayyanu Ibrahim Maradun ne ke farin cikin kasancewa daku a Taskar ta yau, shirin da ke kawo muku labaran duniya har ma da rahotannin abubuwan da ke faruwa a nan Najeriya da makwabciya Jamhuriya Nijar har ma da sauran kasashen duniya.


A cikin rahotannin mu na yau zaku ji cewa:

1.          Rahotanni daga jahar Sakkwato na bayyana yau Assabar din nan ne wata mata ‘yar asalin Jamhuriya Nijar ta tsallake rijiya da baya, biyon bayan zargin wani jami’in hukumar shige da ficen Najeriya da harbinta, a birnin Sokoto.

Cue………………………………..in Wata Mata.

2.          Rashin samun tallafi daga gwamnati ya tilastawa Manoman rani a jahar Kebbi yin Kaurar-dole zuwa Makwabtan jihohi domin neman Mafita. To ko me yayi zafi haka?

Cue in………………………………….Manomi

3.          Muna kuma tafe da shirin yan siyasa na iya ruwa fidda kai a cikin taskar ta yau.

 Cue in……………………………. Iya Ruwa

Zaku ji cikon wannan dama shirin Najeriya a Makon Jiya tare da Nura Muhammad Ringim, to amma bari mu fara da jin halin da duniya ke ciki tukunna.

 

TASKA TUNE………………………………………….

   LABARAN DUNIYA

                                               

AFGHANISTAN

Akalla mutum takwas ne suka mutu yayin da fiye da 30 suka jikkata sakamakon harin rokoki da aka kai rukunin gidaje a birnin Kabul na Afghanistan.

Roka fiye da 12 aka harba daga wata mota zuwa cikin birnin, a cewar ma'aikatar harkokin cikin gida.

Ƙungiyar IS ta yankin ta ɗauki alhakin kai harin, wanda aka kai a wanni kadan kafin tattaunawa tsakanin Sakataren Harkokin Wajen Amurka Mike Pompeo da wakilan ƙungiyar Taliban.

A farkon makon nan ne gwamnatin Donald Trump ta sanar da cewa za ta janye dakaru 2,000 daga Afghanistan nan zuwa watan Janairu.

Masu sharhi da dama na ganin sojojin Afghanistan ba su da ƙarfin yin yaƙin da kansu idan sojojin ƙasashen waje suka fice.

VISION NEWS HAU

 

           BRAZIL

Masu fafutikar adawa da wariyar launin fata a kasar Brazil na zanga-zanga a gaban babban kantin Carrefour bayan ƴan sanda sun aikata ƙazamin kisa kan wani mutum baƙar-fata da ke aiki a kantin.

Lamarin dai ya faru ne a kudancin birnin Porto Alegre a daren Alhamis din data gabata, 'yan sanda sun yi amfani da ƙarfi wajen tarwatsa dubban masu zanga-zangar.

Mutumin da jami'an tsaron suka kashe ɗan shekara 40 ne mai suna Joao Alberto Silveira Freitas. Sai dai Mataimakin Shugaban Brazil, Hamilton Mourao ya alakanta kisan da rashin ƙwarewa irinta jami'an tsaro sannan ya dage kan cewa ba a nuna wariyar launin fata a kasar ta Barzil.

VISION NEWS HAU.

 

LABARUN DUNIYA KUKE SAURARO DAGA NAN VISION FM NIJERIYA.

                           

  AMURKA

Zaɓaɓɓen Shugaban kasar Amurka Joe Biden na neman kuɗin gudanar da shirye-shirye na karɓar gwamnatin ƙasar saboda shugaba Trump ya ki bayar da haɗin kai domin miƙa mulki ga tawagarsa.

Cikin wata yekuwar neman tallafi da Biden ya wallafa a shafinsa na Twitter, ana neman magoya bayansa da su tara kuɗin saboda Donald Trump ya ƙi aminta da shan kaye.

Sakon na Joe Baden ya nuna buƙatar taimako daga magoya bayansa domin iya gudanar da tsare-tsaren karbar gwamnati daga hannun shugaba Trump.

To sai dai a gefe guda kuma, Donald Trump ya sake fuskantar gagarumin koma-baya a ƙalubalantar sahihancin sakamakon zaɓen da yake yi.

'Yan majalisar Jihar Michigan na jam'iyyar Republican ta Trump sun faɗa masa cewa ba su samu wasu gamsassun bayanai da za su iya yin watsi da nasarar da Joe Biden ya samu ba a Jihar, don haka dole a jingine duk wata matsala da za ta haifar da barazana ga kasar.

VISION NEWS HAU.

Labarun duniyar kenan, yanzu kuma sai rahotanni shirye shiryen da Taskar take dauke dasu.                      

    TASKA TUNE…………………………………………

 

 

21-11-2020                  TASKA                 SOKOTO

Da sanyin safiyar Assabar din nan ne wata mata ‘yar asalin Jamhuriya Nijar ta tsallake rijiya da baya, biyon bayan wani harbin bindiga da ake zargin wani jami’in hukumar kula da shige da fice ta Najeriya ya yi mata, lamarin da ya auku a tsakiyar birnin Sokoto.

Kamar yadda zaku ji a cikin wannan rahoton da Abubakar Tauba ya aiko mana daga Sokoto, an garzaya da matar a asibitin kwararru dake Sokoto, sai dai jami’in da yayi harbin ya sha da kyar a hannun wasu fusatattun yan Najeriya da suka shedi yadda lamarin ya auku.


Ga dai rahoton da Tauban ya aiko mana daga Sokoton.

Cue in Sokoto: Start with voice of demonstrators

A gaida Tauba, sai ka dakace mu domin zaka sake dawowa cikin taskar nan gaba kadan.

Cue in Amadu Ajilo’s song…. ”Allah Wahidun Ka taimaki ‘yan Najeriya, kasarmu ta zauna lafiya baki dai”


 

21-11-2020                  TASKA                KEBBI

Idan muka leka a jihar Kebbi dake makwabtaka da sokoton kuwa, Manoman ranin jihar ne ke yin Kaurar-dole ta hanyar barin jihar zuwa Makwabtan jihohi domin neman Mafita ko mafaka.

Manoman sun ce sun dauki matakin ne saboda kasawar da suke zargin Gwamnatin jihar Kebbi ta yi wajen taimaka musu da tallafin da zai basu kwarin quiwar tsayawa a fadammunsu na gadin-gadin.

Bari mu ji halin da suke ciki a cikin wannan rahoton da Muhammad Yazeed Umar ya aiko mana daga jihar ta Kebbi.

Cue in kebbi: The farmar’s voice………………….

Muhammad yazzed Umar kenan, yanzu kuma sai shirin siyasa na wannan makon wato Iya ruwa fidda kai tare da Kabir Hassan Iyatawa.

Gareka Iyatawa.

Cue in Iya Ruwa tune……………………………..

Shirin siyasa na Iya ruwa fidda kai kenan kuka saurara tare da Kabir Hassan Iyatawa, da fatar yan siyasa da masu ra’ayin tofa albarkacin akan lamuran siyasa zasu tuntubi wakilanamu a duk lokacin da bukatar hakan ta taso.

Cue in tune.

                               

                                    BREAK

To wadannan rahotanni na zuwa muku ne daga nan gidan rediyon Vision FM Najeriya dake  Birnin tarayya Abuja sai jihohin Katsina, Kano da Kaduna, hakama ana sauraren shirin a jihohin Sokoto, Kebbi  da kuma Gombe.

Za ku iya saurarenmu kai tsaye ko karanta labaran da muke wallafawa a shafinmu na Intanet wato, visionfm.ng ko tafka muhawara a shafukanmu na sada zumunta a Vsion Fm Najeriya.

 

Taska Tune…………….…………………………..

21-11-2020                  TASKA                 SOKOTO

Madalla!

Rahotanni daga Jihar Sokoto daya daga cikin jihohin dake fama da matsalar ‘yan bindiga masu garkuwa da mutane a yankin arewa maso yammacin Najeriya na cewa, a tsakiyar makon nan ne masu garkuwa da mutane suka sako Hon. Sa’idu Gumburawa mai baiwa Gwamna Tambuwal shawara akan ayukka na musaman bayan yin garkuwa da shi na tsawon kwanaki.

Ko ya aka yi har Gumburawan ya kubuta?

Daga Sakkwato Abbakar Abbakar Taubah na da cikon rahoton.

 

Cue in…………………………… Tauba

Yanzu kuma sai ku gyara zama domin kasancewa da shirin Najeriya a makon jiya tare da Nura Muhammad Ringim!

Cue in……….. Najeria a Makon Jiya

Nura Muhammad Ringim kenan da shirinsa na Najeriya a makon jiya!

Cue in…………………………… tune

To ga baki daya da haka ne, Taskar ta yau ta kammala, a madadin Zubairu Ahmad Bashir, wanda shine ya hada muna wannan taska ta yau, sai kuma Ukashatu Bello Sakkwato, da ya kula muna da sauti ni Zayyanu Ibrahim Maradun da na gabatar, ke cewa mu kasance cikin koshin lafiya. Sai dai kada ku manta a koda yaushe kuna iya saurarenmu akan yanar gizo wato visionfmrdio.ng

 

Cue in…………………………….Taska tune.

Vision FM



Post a Comment

0 Comments