My Journalistic Work Sample - Zubairu Ahmad Bashir (Kasarawa)
VISION FM 92.5 MHZ SOKOTO
TASKAR VISION RADIO SRIPTS
PRODUCER: ZUBAIRU AHMAD BASHIR (KASARAWA)
17/11/2020 VFMNEWS TASKA
CUE IN SIGNATURE TUNE
Taskar Vision kuke saurare daga nan Gidajen Rediyon Vision FM Najeriya, dake yada shirye shiryensu akan mita 92.1 a Abuja Babban Birnin tarayya da Katsina birnin Dikko, mita 92.5 a Jihohin Sokoto, Kano da Kaduna, a Birnin Kebbi kuwa a na sauraren Vision FM, akan mita 92.9, sai kuma mita 92.7 a jihar Gombe.
Zaku iya sauraren Vision FM kaitsaye a koda yaushe daga ko ina a
fadin duniya, ta adireshin mu na internet wato Visionfm.ng
Hakama zaku iya bibiyarmu ta shafukanmu na Facebook, Twitter, da
Instagram domin tafka muhawara akan labaran da muke wallafawa, duka a Vision FM
Nigeria.
CUE IN TUNE………………………………..
Masu sauraro assalamu alaikum, barkammu da warhaka Zayyanu
Ibrahim Maradun ne ke farin cikin kasancewa daku a Taskar ta yau,
shirin da ke kawo muku labaran duniya har ma da rahotannin abubuwan da ke
faruwa a nan Najeriya da makwabciya Jamhuriya Nijar har ma da sauran kasashen
duniya.
A cikin rahotannin mu na yau zaku ji cewa:
1. Rahotanni daga jahar Sakkwato na bayyana yau
Assabar din nan ne wata mata ‘yar asalin Jamhuriya Nijar ta tsallake rijiya da
baya, biyon bayan zargin wani jami’in hukumar shige da ficen Najeriya da
harbinta, a birnin Sokoto.
Cue………………………………..in Wata Mata.
2. Rashin samun tallafi daga gwamnati ya tilastawa Manoman
rani a jahar Kebbi yin Kaurar-dole zuwa Makwabtan jihohi domin neman Mafita. To ko me yayi zafi haka?
Cue in………………………………….Manomi
3. Muna kuma tafe da shirin
yan siyasa na iya ruwa fidda kai a cikin taskar ta yau.
Cue in……………………………. Iya Ruwa
Zaku ji cikon wannan dama shirin Najeriya a Makon Jiya tare
da Nura Muhammad Ringim, to amma bari mu fara da jin halin da
duniya ke ciki tukunna.
TASKA TUNE………………………………………….
LABARAN DUNIYA
AFGHANISTAN
Akalla mutum takwas ne suka mutu yayin da fiye da 30 suka jikkata
sakamakon harin rokoki da aka kai rukunin gidaje a birnin Kabul na Afghanistan.
Roka fiye da 12 aka harba daga wata mota zuwa cikin birnin, a
cewar ma'aikatar harkokin cikin gida.
Ƙungiyar IS ta yankin ta ɗauki alhakin kai harin, wanda aka kai a
wanni kadan kafin tattaunawa tsakanin Sakataren Harkokin Wajen Amurka Mike
Pompeo da wakilan ƙungiyar Taliban.
A farkon makon nan ne gwamnatin Donald Trump
ta sanar da cewa za ta janye dakaru 2,000 daga Afghanistan nan zuwa watan
Janairu.
Masu sharhi da dama na ganin sojojin
Afghanistan ba su da ƙarfin yin yaƙin da kansu idan sojojin ƙasashen waje suka
fice.
VISION NEWS HAU
BRAZIL
Masu fafutikar adawa da wariyar launin fata a
kasar Brazil na zanga-zanga a gaban babban kantin Carrefour bayan ƴan sanda sun
aikata ƙazamin kisa kan wani mutum baƙar-fata da ke aiki a kantin.
Lamarin dai ya faru ne a kudancin birnin
Porto Alegre a daren Alhamis din data gabata, 'yan sanda sun yi amfani da ƙarfi
wajen tarwatsa dubban masu zanga-zangar.
Mutumin da jami'an tsaron suka kashe ɗan
shekara 40 ne mai suna Joao Alberto Silveira Freitas. Sai dai Mataimakin
Shugaban Brazil, Hamilton Mourao ya alakanta kisan da rashin ƙwarewa irinta
jami'an tsaro sannan ya dage kan cewa ba a nuna wariyar launin fata a kasar ta
Barzil.
VISION NEWS HAU.
LABARUN DUNIYA KUKE SAURARO DAGA NAN VISION FM NIJERIYA.
AMURKA
Zaɓaɓɓen Shugaban kasar Amurka Joe Biden na
neman kuɗin gudanar da shirye-shirye na karɓar gwamnatin ƙasar saboda shugaba
Trump ya ki bayar da haɗin kai domin miƙa mulki ga tawagarsa.
Cikin wata yekuwar neman tallafi da Biden ya
wallafa a shafinsa na Twitter, ana neman magoya bayansa da su tara kuɗin saboda
Donald Trump ya ƙi aminta da shan kaye.
Sakon na Joe Baden ya nuna buƙatar taimako
daga magoya bayansa domin iya gudanar da tsare-tsaren karbar gwamnati daga
hannun shugaba Trump.
To sai dai a gefe guda kuma, Donald Trump ya sake fuskantar
gagarumin koma-baya a ƙalubalantar sahihancin sakamakon zaɓen da yake yi.
'Yan majalisar Jihar Michigan na jam'iyyar Republican ta Trump sun
faɗa masa cewa ba su samu wasu gamsassun bayanai da za su iya yin watsi da
nasarar da Joe Biden ya samu ba a Jihar, don haka dole a jingine duk wata
matsala da za ta haifar da barazana ga kasar.
VISION NEWS HAU.
Labarun duniyar kenan, yanzu kuma sai rahotanni shirye shiryen da
Taskar take dauke dasu.
TASKA
TUNE…………………………………………
21-11-2020 TASKA SOKOTO
Da sanyin safiyar Assabar din nan ne wata mata ‘yar asalin
Jamhuriya Nijar ta tsallake rijiya da baya, biyon bayan wani harbin bindiga da
ake zargin wani jami’in hukumar kula da shige da fice ta Najeriya ya yi mata,
lamarin da ya auku a tsakiyar birnin Sokoto.
Kamar yadda zaku ji a cikin wannan rahoton da Abubakar Tauba ya
aiko mana daga Sokoto, an garzaya da matar a asibitin kwararru dake Sokoto, sai
dai jami’in da yayi harbin ya sha da kyar a hannun wasu fusatattun yan Najeriya
da suka shedi yadda lamarin ya auku.
Ga dai rahoton da Tauban ya aiko mana daga Sokoton.
Cue in Sokoto: Start with voice of demonstrators
A gaida Tauba, sai ka dakace mu domin zaka sake dawowa cikin
taskar nan gaba kadan.
Cue in Amadu Ajilo’s song…. ”Allah Wahidun Ka taimaki ‘yan
Najeriya, kasarmu ta zauna lafiya baki dai”
21-11-2020 TASKA KEBBI
Idan muka leka a jihar Kebbi dake makwabtaka da sokoton kuwa,
Manoman ranin jihar ne ke yin Kaurar-dole ta hanyar barin jihar zuwa Makwabtan
jihohi domin neman Mafita ko mafaka.
Manoman sun ce sun dauki matakin ne saboda kasawar da suke zargin
Gwamnatin jihar Kebbi ta yi wajen taimaka musu da tallafin da zai basu kwarin
quiwar tsayawa a fadammunsu na gadin-gadin.
Bari mu ji halin da suke ciki a cikin wannan rahoton da Muhammad
Yazeed Umar ya aiko mana daga jihar ta Kebbi.
Cue in kebbi: The farmar’s voice………………….
Muhammad yazzed Umar kenan, yanzu kuma sai shirin
siyasa na wannan makon wato Iya ruwa fidda kai tare da Kabir
Hassan Iyatawa.
Gareka Iyatawa.
Cue in Iya Ruwa tune……………………………..
Shirin siyasa na Iya ruwa fidda kai kenan kuka
saurara tare da Kabir Hassan Iyatawa, da fatar yan siyasa da masu
ra’ayin tofa albarkacin akan lamuran siyasa zasu tuntubi wakilanamu a duk
lokacin da bukatar hakan ta taso.
Cue in tune.
BREAK
To wadannan rahotanni na zuwa muku ne daga nan gidan rediyon
Vision FM Najeriya dake Birnin tarayya Abuja sai jihohin Katsina, Kano da
Kaduna, hakama ana sauraren shirin a jihohin Sokoto, Kebbi da kuma Gombe.
Za ku iya saurarenmu kai tsaye ko karanta labaran da muke
wallafawa a shafinmu na Intanet wato, visionfm.ng ko tafka muhawara a
shafukanmu na sada zumunta a Vsion Fm Najeriya.
Taska Tune…………….…………………………..
21-11-2020 TASKA SOKOTO
Madalla!
Rahotanni daga Jihar Sokoto daya daga cikin jihohin dake fama da
matsalar ‘yan bindiga masu garkuwa da mutane a yankin arewa maso yammacin
Najeriya na cewa, a tsakiyar makon nan ne masu garkuwa da mutane suka sako Hon.
Sa’idu Gumburawa mai baiwa Gwamna Tambuwal shawara akan ayukka na musaman bayan
yin garkuwa da shi na tsawon kwanaki.
Ko ya aka yi har Gumburawan ya kubuta?
Daga Sakkwato Abbakar Abbakar Taubah na da cikon rahoton.
Cue in…………………………… Tauba
Yanzu kuma sai ku gyara zama domin kasancewa da shirin Najeriya a
makon jiya tare da Nura Muhammad Ringim!
Cue in……….. Najeria a Makon Jiya
Nura Muhammad Ringim kenan da shirinsa na Najeriya a makon jiya!
Cue in…………………………… tune
To ga baki daya da haka ne, Taskar ta yau ta kammala, a
madadin Zubairu Ahmad Bashir, wanda shine ya hada muna wannan
taska ta yau, sai kuma Ukashatu Bello Sakkwato, da ya kula muna da sauti ni
Zayyanu Ibrahim Maradun da na gabatar, ke cewa mu kasance cikin koshin lafiya.
Sai dai kada ku manta a koda yaushe kuna iya saurarenmu akan yanar gizo
wato visionfmrdio.ng
Cue in…………………………….Taska tune.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.