Kundin Binciken Neman Digirin Farko (B.A Hausa) Wanda Aka Gabatar A Sashen Harsuna Da Al’adu, Jami’ar Tarayya Gusau.
Ingausar
Yarbawa Da Hausawa A Garin
Gusau, Jihar Zamfara (6)
NA
ADAMU SANI
BABI NA BIYAR
KAMMALAWA
5.0 SHIMFIƊA
Da sunan
Allah mai rahama mai jinƙai, wanda ya
baiwa ɗan-Adam
fasahar karatu da rubutu, tare da bayar da dammar yin wannan aikin. Allah mun
gode ma, tsira da amincin Allah su tabbata ga Manzonmu Annabi Muhammad (S.A.W)
tare da iyalansa da sahabbansa har zuwa ranar ƙarshe.
Wannan babin
shi ne babi na ƙarshe a wannan aiki, yana ɗauke da
abubuwa kamar haka; Taƙaitawa, da hasashen
bincike, haka kuma akwai ta’arifin wasu kalmomi. Bugu da ƙari daga ƙarshe
akwai naɗewa.
5.1 TAƘAITAWA
A wannan
bagire za a taƙaita aikin ne gaba ɗaya ta hanyar
haskaka ababen da aka binciko da kuma sakamakon binciken, da kuma kammalawar
aikin. Wannan bicike ya ƙunshi babi
biyar, za mu bayyana abin da kowane babi ya tattauna a taƙice kamar
haka:
Babi na ɗaya an
tattauna abubuwa kamar; dalilin gudanar da bincike, da muhallin bincike. Haka
kuma an bayyana hanyoyin gudanar da bincike. Bugu da ƙari, an
bayyana muhimmancin bincike kamar samar da abubuwan karatu, bayan waɗannan an
bayyana matsalolin da aka fuskanta lokacin gudanar da binciken kamar ƙin
bada haɗin kai daga
wasu Yarbawa da sauransu.
A babi na
biyu an waiwayi wasu ayuka na magabata da aka gabatar a kan ingausa da kuma
wasu masu alaƙa da ita. Daga bugaggun littattafai, da muƙalu,
da kuma kundin bincike.
Babi na uku kuwa mai taken “Gusau ta Sambo”, an
tattauna abubuwa da dama daga ciki akwai; Taƙaitaccen
tarihin Gusau, an waiwayi kafuwar garin Gusau a shekarar (1806) da kuma zaman
sa babban birnin jihar Zamfara a shekarar (1996). Haka kuma an bayyana yanayin
garin, da kuma waɗanda suka
fara zama a garin, bugu da ƙari an
bayyana tattalin arzikin mutanen garin kamar noma da sauran wasu sana’o’i.
Haka kuma an
bayyana addinin mutanen garin shi ne musulunci, amma sanadiyar zuwan baƙi
an samu addinin masihiyya (Kiristanci) da mabiya addinin gargajiya. Bayan waɗannan an
bayyana zuwan Yarbawa garin tun a (1920) da wasu lokuta mabambanta. Kuma an
bayyana mu’amularsu da Hausawan Gusau tare da bayyana tasirin harshe da al’adun
mutanen Gusau ga Yarbawa, kamar auratayya, sakatufafin Hausawa da Sauransu.
Babi na huɗu mai taken
Ingausa an bayyana ma’anar harshe daga masana daban –daban, kuma an kalli
harshen Hausa da Hausawa, tare da duban abokan zaman su Yarbawa da harshensu.
Bugu da ƙari an bayyana ma’anar ingausa daga masana
daban- daban, tare da kawo dalilan da ke haifar da ingausa kamar zaɓen kalmomi da
sauransu. Haka an kawo amfani da illolin ingausa ga harshe. Bayan waɗannan an
bayyana sakamakon binciken ta hanyar kawo misalign wasu jumlolin ingausar
Yarbanci da Hausa cikin jadawali.
Babi na biyar
mai taken “taƙaitawa” ya tattauna abubuwa kamar taƙaitawa,
hasashen bincike, da ta’arifin wasu kalmomi da kuma naɗewa a ƙarshe.
5.2 HASASHEN
BINCIKE
An yanke
shawarar gudanar da wannan bincike mai taken “Ingausar Yarbawa da Hausawa a
garin Gusau” a matsayin wani hasashe na fitowa da tasirin da harshen Hausa ya
yi ga Yarbawan garin Gusau, tare da aza batun a faifan nazarin harshe domin
samar da abubuwan dubawa ga ɗalibai ‘yan’uwa da ma’abota bincike a
kan harshe.
Haka kuma ana
hasashen wannan bincike zai iya zama ƙofa ga masu
nazarin harshe, inda za a iya kallon ingausar a wasu harsuna da ba Hausa da
Yarbanci ba, ko kuma Hausa da Yarbanci a wata siga da ba wannan ba. Kamar ingausar
Yarbanci a cikin waƙoƙin
Hausa na zamani da sauransu.
5.3 TA’ARIFIN
WASU KALMOMI
Ta’arifi
ararriyar kalma ce daga harshen Larabci, wadda take nufin fito da ma’anar abu.
A wannan bagiren za a fito da ma’anar wasu kalmomi ne na Yarbanci da aka yi amfani
da su a cikin sakamakon binciken. Za a bayyana su a cikin jadawali kamar haka:
S/N |
YRB |
HAU |
1.
|
Bami |
Bani |
2.
|
Gbe |
Ɗauki
|
3.
|
Mode |
Na zo |
4.
|
Mofe |
Ina so |
5.
|
Tuntun |
Sabo |
6.
|
Mi |
Ni |
7.
|
Ni |
Shi/kai |
8.
|
Wo |
Kallo |
9.
|
Oni |
Ba ka da |
10.
|
Aso |
Tufafi |
11.
|
Odi |
Sai |
12.
|
Oro |
Magana |
13.
|
Omo |
Wannan/wancan
|
14.
|
Adugbo |
Shiya/Unguwa
|
15.
|
Obe |
Miya |
16.
|
Monlo |
Zan je |
17.
|
Iyawo |
Amarya |
18.
|
Arewa |
Kyakkyawa
(Mace) |
19.
|
Yami |
Aro mini |
20.
|
Jade |
Fita |
21.
|
Funmi |
Bani/ Sayo |
22.
|
Oti |
Giya |
23.
|
Moje |
Na ci |
24.
|
Olulufemi |
Abin ƙaunata |
25.
|
Kosi |
Babu |
26.
|
Tori |
Saboda |
27.
|
Ana |
Jiya |
28.
|
Omoge/Omidan |
‘Yanmata |
29.
|
Dara-Lakunrin
|
Kyakkyawa
(Namiji) |
30.
|
Age |
Buta |
31.
|
Ose |
Sabulu |
32.
|
Eko |
Kunu |
33.
|
Omitutu |
Ƙanƙara |
34.
|
Funfun |
Fari |
35.
|
Elubo |
Gari |
36.
|
Amun |
Tulu |
37.
|
Ife |
Kofi |
38.
|
Kanga |
Rijiya |
39.
|
Oba |
Sarki |
40.
|
Oluko |
Aji |
41.
|
Gba |
Karɓa/ansa |
5.4 NAƊEWA
Daga ƙarshe
za a ƙara jaddada godiya ga Allah (SWA) da ya bada
ikon kamala wannan aikin, da fatar zai zama wata muhimmiyar gudummuwa a fagen
ilimi wadda da ba a samu ba.
Wannan babin
kammalawa ce ta aikin da aka gudanar a kan ingausar Yarbawa da Hausawa a garin
Gusau. Babin ya yi bayani a kan abubuwa kamar; Shimfiɗa, da taƙaitawa
game da aiki da aka gudanar, haka kuma an bayyana hasashen binciken, bugu da ƙari
da ta’arifin wasu kalmomin Yarbanci zuwa Hausa, daga ƙarshe da naɗewar aikin
baki ɗaya.
MANAZARTA
Tuntuɓi Amsoshi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.