Kundin Binciken Neman Digirin Farko (B.A Hausa) Wanda Aka Gabatar A Sashen Harsuna Da Al’adu, Jami’ar Tarayya Gusau.
Kwalliyar
Matan Garin Gusau (1)
NA
ƊAYYABA
MUSTAPHA IBRAHIM
SADAUKARWA
Na sadaukar
da wannan aiki nawa ga mahaifiyata Hajiya Maimunatu Aliyu, Allah ya jiƙanta
da rahama, sai kuma mahaifina Alhaji Mustapha Ibrahim, da kuma yayata Hajiya
Hadiza Mustapha Ibrahim waɗanda da taimakonsu ne cikin yardar
ubangiji aka fara wannan karatu lafiya kuma aka gama lafiya. Allah ya saka da
mafificin alheri.
TSAKURE
Wannan kundi yana ƙunshe da bayanai akan Kwalliyar Mata a Garin Gusau, da ire-irenta da nau’o’inta da amfaninta, da kuma yanda mata ƙanana ke yin kwalliya da ‘yan mata da zawarawa, da kuma matan aure. Daga ƙarshe, an bayar da shawarwari a kan yadda za a bunƙasa Kwalliya. Akwai kammalawa da kuma manazarta.
GODIYA
Ina fara
jaddada godiyata ga Allah (S.W.T) mai rahama mai jinƙai. Tsira da
amincin Allah su tabbata ga Annabi Muhammad (S.A.W) da sahabbansa da zuri’arsa
da dukkan wanda ya bi tafarkinsa har zuwa ranar sakamako.
Bayan haka,
ina miƙa godiya da jinjina zuwa ga mahaifiyata
Hajiya Maimunatu da Mahaifina Alhaji Almustapha Ibrahim a bisa jajircewarta
domin ta ga na kammala wannan karatu, kuma na gode da irin addu’o’in da take yi
mini ba dare ba rana. Allah ya saka mata da mafificin alkhairi, ya sanya
Al-Janna Firdausi ta kasance makoma a gareta.
Bayan haka,
sai godiya da jinjina zuwa ga yayyena da kuma ƙannena a bisa
gudunmawarsu ta fuskoki daban-daban, tun daga addu’o’i, shawarwari da kuma
kayan aiki daga cikinsu akwai; Aunty Hadiza, Aunty Hannatu, Yaya Babawo, Aunty
A’isha, Aunty Halima da kuma kanene Attahir, da kuma Maimunatu da Fatima, da
Sani, Rabiatu da kuma Hafsatu, duk Allah ya saka masu da mafificin alkhairi.
Godiya ta
musamman ga malamai na musamman na sashenmu, dangane da gudummawar da suka bani
da kuma shawarwari. Haka kuma ina miƙa godiyata ta
musamman ga Malamai kamar su; Prof. Aliyu Muhammad Bunza, Prof. M.T Yakawada,
Prof. Balarabe, Malam Rabi’u A. Ɗangulbi da malam
Isah S. Fada da malam Musa Abdullahi da Dr. Nazir Abbas da Dr. Tahir da Dr.
Fadama da Dr. S. Gulbi da sauransu. Allah ya saka da mafificin alheri.
Bayan haka,
ina miƙa godiya da jinjina ga malamina kuma wanda ya
duba wannan aiki Malam Musa Abdullahi bisa ɗorani a kan
hanya da kuma haƙuri da ya yi da ni lokacin gudanar da wannan
aiki. Allah ya saka da alheri.
Bayan haka
ina miƙa godiya ta ga mutanen da aka yi hira da su a
lokacin gudanar da wannan aiki, musamman yadda suke ba da lokacinsu sannan kuma
suna da karamci, daga cikinsu akwai; Malama Halimatu, Malama Hurriya Mai
Kwalliya da dai sauransu.
Haka kuma,
ina miƙa godiyata zuwa ga abokan karatuna dangane da
taimakon da su yi mini ta fuskoki daban-daban, nagode da kulawarku, Aunty
Amina, Abubakar Hassan, Abdulrashid S. Fawa, Ahmad M. Kabir, Abdulrahman Bala
(ABG), Aliyu S. Ibrahim, Bashir Isiyaku, Mustapha Sa’idu, Hassan Galadima, Nura
S. Kwatarkwashi, Hizbullahi Ɗanlami.
Haka kuma
akwai godiya zuwa ga abokaina na musmaman waɗanda ba zan
manta da su ba, kamar irin su; Safiyya Ahmad, Wasila Sani, Rahila Aliyu da
Zainab Sani
A ƙarshe
ina miƙa godiya ta musamman ga Faisal Musa bisa ga
addu’arshi da kuma jajircewa wurin hakar karatuna na gode, Allah ya saka da
mafificin alheri.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.