Ticker

6/recent/ticker-posts

Gudummawar Turawa Wajen Samuwa Da Ginuwar Ƙa’idojin Rubuta Hausa

 Maƙalar da aka gabatar a taron ƙara wa juna sani na ƙasa da ƙasa da Sashen Harsunan Nijeriya Da Kimiyar Harshe, Jami’ar Jahar Kaduna ta shirya a kan Daidaitacciyar Hausa da Ƙa’idojin Rubutu da Fasahar Shirya Ƙamus da kuma Ƙalubalan da Suke Fuskanta a Cikin Ƙarni Na 21. Wanda aka gudanar a Zauren Lacca Na Tsangayar Fasaha da ke Jami’ar Jahar Kaduna, daga ranar 14 zuwa 17 ga watan Nuwamban shekarar 2019.    

rubutun hausa

Gudummawar Turawa Wajen Samuwa Da Ginuwar Ƙa’idojin Rubuta Hausa

Dr. Adamu rabi’u bakura

arbakura62@gmail.com

08064893336

Tsakure

            Rubutu wani salo ne na zayyana wasu alamomi a kan wani abu mai bagire da za su waƙilci Magana. Ana iya kallonsa a matsayin wani nau’i na kwaikwayon Magana wadda ake furtawa da fatar baki. Akwai waɗansu ‘yan bambance-bambance tsakaninsa da maganar fatar baka. Bambancin kuwa shi ne,  naƙaltar ƙa’idojin rubutu, rashin sanin ƙa’idar rubutu yana haifar da sauya ma’ana da rage wa matanin da aka rubuta kima. Yayin da aka tashi rubuta wata maganar fatar baki, dole ne a kula da wasu lafuzzan sautukan harshe tare da ƙoƙarin nuna su a rubuce domin sadar da saƙo mai ma’ana. Hakan ba zai tabbata ba sai ta hanyar fahimtar dokokin rubuta harshe. Rubutun Hausa, tamkar rubutun kowane  harshe ne, yana da ƙa’idoji waɗanda tilas ne mai rubutu ya kiyaye su muddun yana buƙatar isar da saƙo mai ma’ana. Fahimtar haka ya sa Turawa suka haɗu suka shata ƙa’idojin rubuta Hausa da haruffan boko. Harshen Hausa da al’ummar Hausawa sun amfana, saboda hakan ya taimaka wajen cigaban harshen Hausa da kyautatuwar martabarsa. Ba don Turawa ba, da ɗora wa boko harsashi a Hausa ya yi wuya. Turawan mishan da ‘yan leƙen asiri da ma’aikatan hukuma da ‘yan mulkin mallaka, sun taimaka wa rubutun Hausa har ya sami kansa a matsayin da yake a yau. Sanin haka ne ya sa wannan maƙala ta ƙuduri aniyar komawa fagen tarihi domin zaƙulo rawar da Turawa suka taka wajen shimfiɗa harsashen ginin ƙa’idojin rubutun Hausa, musamman hanyoyin da suka bi wajen mayyaze wasu sautukan Hausa da babu a harshen Ingilishi. Ko ba komai Hausawa sun ce, waiwaye adon tafiya.   

1.0 Gabatarwa

            Harshen Hausa ya fi kowane harshe da ke sararin wannan duniya sauƙin sarrafawa. Domin lafuzzan haruffan boko da ake rubuta Hausa da su, ba sa sauyawa kamar yadda wasu harsuna kan sauya. Misali a rubutun Hausa lafazin harafin g ba ya sauyawa, kamar yadda yakan sauya a Ingilishi, inda yakan koma lafazin /j/  kamar a Kalmar Germany. Haka kuma a harshen Hausa ba a gutsure ƙarshen kalma wajen karatu tamkar yadda yake faruwa a harshen Larabci, a inda ake rubuta BINTU a karanta shi da lafazin BINT. Irin wannan sauƙin ne ya sa Turawa suka duƙufa suka koyi harshen har suka yi ƙoƙarin shata masa ƙa’idojin rubutu domin cimma wata ɓoyayyar manufarsa. Rubutu da maganar baki sun sha bamban. Hasali ma dai rubutu wakiltar maganar baka yake yi. Don haka ne suka yi tunanin tsara wasu ƙa’idojin da za su taimaka wa masu karatu saurin fahimtar abin da aka rubuta. Fahimtar haka ne ya sa aka ƙudurin aniyar komawa cikin fagen tarihi domin lalabo irin rawar da Turawa suka taka wajen aza harsashen gina ƙa’idojin rubutun Hausar boko. Shi ya sa aka sanya wa maƙalar suna: Gudummawar Turawa Wajen Samuwa Da Ginuwar Ƙa’idojin Rubutun Hausa. Takardar ta kawo ma’anonin tubalan ginin taken maƙalar tare da bayyana nau’o’in gudummawar da Turawan suka bayar kamar : Schon da Robinson da Hanns Vischer da Bargery da R. M. East wanda ya kai gwauro ya kai mari don ganin Hausa ta sami daidaitacciyar hanyar rubutu. Kamar yadda za a gani ɗaya bayan ɗaya.   

1.1 Gudummawa

            Gudummawa kalma ce bahaushiya da ke cikin jerin sunayen jinsin mata. Ana faɗar ta da “gudunmawa” a karin harshen Sakkwatanci da na Kananci da kuma Zazzaganci, kuma akan furta ta da lafazin “gudunmuwa” a karin harshen Kananci, kamar yadda Bargery (1993:402) ya nuna. Shi kuwa Abraham (1975:337) ya nuna cewa a karin harshen Sakkwatanci ne ake faɗar ta da lafazin “gudunmowa”, wato akan sa wasalin “o” a gaɓa ta uku maimakon wasalin “u” da wasu karin harsuna ke amfani da shi. Har ila yau Ƙamusun Hausa na Jami’ar Bayero (2006:171) ya nuna ana furta gaɓa ta uku da wasalin “a” ko “o” misali gu-dum-ma-wa. Kalmar gudummawa tana ɗauke da ma’anar taimako na aiki ko kuɗi ko abinci ko sutura ko wani abu. Kuma daidai take da agaji ko ceto daga wahala kamar yadda Garba (1990:4) ya bayyana.

 

1.2 Turawa

            Ita kuma Kalmar “Turawa”, jam’i ce ta kalmar Bature ko Baturiya. Wannan kalma tana cikin jinsin suna na namiji. Turawa suna ne da ake kiran ‘yan asalin ƙasashen Yammacin duniya da ake yi wa laƙabi da Turai waɗanda ke amfani da harsunan Turanci a matsayin harshen uwa, musamman Ingilishi na ƙasar Ingila, kamar yadda Ƙamusan Hausa (2006:41) da Webster (1990:428) da Macmillan (2007:501) suka nuna.

1.3 Samuwa

            Kalmar “samuwa” kuwa tana nufin tabbatar da abu a hannun mutum ko al’umma. Ita wannan kalma an fito da ita ne daga kalmar “saamaa” wadda ke iya ɗaukar wasalin “e” ko “i” ko “o” ko “u” a gaɓar ƙarshe. Misali; saamee, saami, saamoo, saamuu, Ƙamusun Hausa  (2006:385).

            Wannan kalma ce da ke cikin jerin kalmomin da ke nuna aiki, wato fi’ili. Kuma tana ɗaukar ɗafa ƙeya, wanda hakan ya bayar da kalmar “samuwa”, wato an yi mata ƙarin “wa” a ƙarshenta.

1.4 Ginuwa

            Ginuwa kuma kalma ce da aka samar daga kalmar “gina”, mai ɗauke da ma’anar ƙaga wani abu. Ita wannan kalma tana cikin sahun kalmomi da ke nuna aiki, wato fi’ili. Haka kalmar tana iya ɗaukar wasalin “e” ko “o” ko “u”. Ita ma tana ɗaukar ɗafa-ƙeya, wanda hakan ya samar da kalmar “ginuwa”. A Hausance kalmar ƙaga na ɗauke da ma’anar ƙirƙiro ko samar da wani abu ko gano wani sabon abu kamar yadda Ƙamusun Hausa (2006:165) ya bayyana.

 

1.5 Ƙa’idoji 

            Asalin wannan Kalmar balarabiyar kalma ce da aka samo daga Kalmar Larabci, wadda Larabawa ke kira da suna ƘA’IDATUN  ana kuma taƙaita ta zuwa ƘA’IDA a harshen Larabcin. Ta hanyar taƙaitawar ce Hausawa suke amfani da Kalmar, Kalmar ƘA’IDA (Ƙaa’idaa) tana cikin jerin sunayen kalmomin Hausa jinsin mata, jam’i kuwa ya kasance ƙa’idoji  ko ƙa’idodi. Kalmar na ɗauke da ma’anoni daban-daban da suka haɗa da:

Doka – Wannan kalma na nufin umurnin hukuma, jam’i kuwa  a ce dookooki.

Iyaka – Marabar wani abu da wani abu.

Tsari – Daidaitawar abubuwa ko kuma shiryiwarsu.

Kyakkyawar ɗabi’a, kamar yadda BUK (2006:274) ya bayyana

1.6 Rubutu

            Ita wannan kalma bahaushiyar kalma ce wadda ke cikin tsarin kalmomin suna jinsin maza, jam’i kuwa shi ne rubuce-rubuce. Kalmar na ɗauke da ma’anar: Zana wasu alamomi a kan takarda ko wani abu mai bagire domin sadar da Magana wadda ɗan-adam ya fi faɗin (furta) ta da fatar baki a ji da kunne, kamar yadda Yahaya (1988:1) da Bunza (2002:1) da BUK (2006:374) suka nuna.

1.7 Ma’anar Ƙa’idajin Rabutu

            Ƙamusai da dama sun bayyana ma’anar ƙa’idar rubutu (orthography) gwargwadon fahimtarsu, kamar yadda za a gani ɗaya bayan ɗaya:

            Webster (2000: 834) ya bayyana ma’anar da cewa: Wata fasahar rubuta kalmomi ne ta amfani da haruffan da suka dace bisa daidaitaccen tsari. A ma’anarsa ta biyu kuwa, cewa ya yi:  hanya ce da ake amfani da ita wajen wakiltar sautukan lafuzzan furucin harshe a rubuce ko kuma ta hanyar buga wasu sanannun alamomi. Ba nan kawai ya tsaya ba, ya ma nuna cewa, wata hanyar nazari ce da ta danganci haruffa da rubutun kalmomin harshe.

            Yayin da Kamusan Macmillan (2007:1058) ya bayyana ma’anar da cewa: A nazarin ilimin harshe ƙa’idar rubutu na nufin wani salon tsarin rubutu ne da ake amfani da shi wajen rubuta haruffan harshe.

            Idan muka dubi yadda masana suka bayyana ma’anonin tubalan gini wannan maƙala a cikin ƙamusai da ita kanta ma’anar ƙa’idar rubutu, za a iya  cewa a dunƙule: Wata daidaitacciyar hanya ce, da aka shata domin sarrafa abjadin Hausa cikin kyakkyawan tsarin ginin kalmomin Hausa, bisa dokokin haɗa kalma da kalma  da raba su tare da ba kowane sautin furuci haƙƙinsa tamkar yadda tsarin nahawun harshen ya tanada, domin sadar da sahihiyar ma’ana a rubuce.

2.0 Tarihin Rubutu Da Gwagwarmayar Marubuta

            Tun farkon zuwan Turawa a farfajiyar Afirka ta Yamma a cikin shekarar 1773, suka soma tsintar kalmomi da zantuttukan Hausa, suka tafi da su ƙasar Turai. Sun  rubuta su ne da harruffan Romawa (boko), kamar yadda Hair (1967:32) ya nuna. A daidai wancan lokacin duk yadda kunnensu ya ji sautukan Hausar, haka nan suka rubuta su.

            Ƙasashe kamar Jamus da Ingila su ne wuraren da aka fara ƙoƙarin daidaita harruffan Romawa wajen rubuta harsunan Afirka, ciki kuwa har da harshen Hausa. Wani masanin tarihin kalmomi da ke Jamus mai suna: Lepsius, shi ne ya fara shirya wata hanyar rubutu a shekarar 1850, da aka kira: Daidaitaccen Abjadi, kamar yadda Zarruk (1980:112) da Yahya(1988:74) da Bunza (2002:32) suka zo da bayanin. Ta wannan hanyar rubutu ce, Turawan ƙasar Jamus da dama suka aiwatar da rubuce-rubucensu masu ɗimbin yawa da suka danganci harshen Hausa da adabinsa, kamar: James Frederick Schon da Prietzer da Miscich da George Reime da Westerman da sauransu.

            Yayin da aka karkato a ƙasar Ingila kuwa, akwai masana kamar irin su: Farfesa Lee, da ya yi aiki a ƙarƙashin Ƙungiyar Gano Afirka, waɗanda suka samar da wani matani da suka kira  da suna: Rubutun Afirka. Daga cikin Turawan da suka yi amfani da wannan hanyar salon rubutu babu kamar Rabinson da Bargery, tamkar yadda Hair (1967:40) ya ambata.

2.1 Gudummawar Schon

            Schon mutumin ƙasar Jamus ne, cikakken sunansa James Frederic Schon. Aikin Mishan ya kai shi Saliyo a wajejen shekarar 1840. Bai taɓa saka ƙafarsa a farfajiyar ƙasar Hausa ba. Ya koyi Hausa ne wurin Dorogu da Abega, wasu bayi da Barth ya tafi da su ƙasar Turai, kamar yadda Yahaya (1988: 124).

            Schon ya yi amfani da kusan haruffan abjadin da ake amfani da su a wannan zamani wajen rubuce-rubucensa na Hausa, in ban da ‘yan atishawa da ‘yan zoza da hamzatattu. Abjadin kuwa sun haɗa da: a, b, c, d, e, f, g, h, I, j, k, q, l, m, n, o, p, r, s, t, u, v, w, y, z.

Kasancewar kunnen Schon na Jamusanci ne, shi ya sa sautukan ‘yan atishawa kamar: c, j, ts, sh, s, z da ‘yan zuz na Hausa kamar: f,  fy,  sh,  h,  s suka gagare shi rarrabewa. Wannan ne ya haifar da hautsuna su.

Haka ya kasa tantance hamzatattun baƙaƙe, wannan ne ya wanzar da rashin haruffan ɓ,  ɗ, ƙ, da ‘y a cikin abjadinsa. Wani lokacin yakan rubuta gb a madadin b. Ya kuma kasa gane bambancin gajeren wasali da ɗauri. Wannan ne ya sa yakan rubuta baba a wani wurin kuwa ya sa babba domin ya ɗauke su tamkar abu ɗaya ne. Wani lokaci yakan rubuta dere wani zubin kuwa ya rubuta dare. A wasu wuraren kuwa ya rubuta taffi da teffi a madadin tafi, kamar yadda Newman (1974:3-4) ya nuna.

Schon ya bayar da muhimmiyar gudummawa wajen aza harsashen ginin ƙa’idojin rubutun Hausa, domin ana kyautata zaton cewa, shi ne Baturen farko da ya gabatar da jerin haruffan Hausa da yadda ake amfani da su wajen gina kalmomin Hausa, (Schon,1885:xi-xii). Hasali ma da aikinsa na Nahawun Hausa aka yi amfani wajen koyar da Turawa ɗalibai harshen Hausa a ƙasar Turai, kamar yadda Bakura (2012:211) ya kalato daga Baldin (1977:9-10).                                                                                                                            

2.2 Gudummawar Charles Henry Robinson

Robinson haifaffen garin Ingila ne. Yana ɗaya daga cikin ‘yan ƙungiyar Hausa, wadda aka kafa a shekarar 1890. Ƙungiyar ce ta ɗauki nauyin turo shi ƙasashen Afirka. Ya zauna a Libiya inda ya koyi harshen Larabci da Hausa, wannan ne ya ba shi damar naƙaltar rubutun ajamin Hausa. Wannan ne ya ba Robinson damar sanin hamzatattun baƙaƙen Hausa, ya yi ƙoƙarin rarrabe su. Ana kyautata zaton shi ne ya fara yin ɗigagga a ƙarƙashin haruffa kamar: b. da d. da kuma k. . Sai dai ba ko’ina yake yin ɗigon ba. Saboda tasirin da rubutun ajamin Hausa ya yi masa, domin su kansu masu rubutun ajamin Hausa, sukan rubuta harafin ƙan mai ruwa (ق) wani zubin su rubuta kaulasan (ك) dalilin haka ne Robinson ya rubuta karami maimakon k.arami ( ƙarami) ya kuma rubuta k.aratu maimakon karatu.

Abin tambaya a nan shi ne, daga ina Robinson ya samo wannan fasahar saka ɗigagga a ƙasan hamzatattun haruffa? Shin shi da kansa ya ƙago ko ilhami ya samu? Ko kuwa kwaikwayon fasahar ya yi?

Amsar waɗannan tambayoyi ita ce, muna sane da cewa, ya koyi harshen Hausa da Larabci a ƙasar Libiya. Ita kuwa Hausar da ya koya, ya koye ta ne daga wasu malamai ko almajirai da suka fito daga ƙasar Hausa. Wannan ne ya ba shi damar naƙaltar ajamin Hausa, ta hanyar karatu da rubutun ajamin ne ya mayyaze hamzatattun sautuka. Har ya yi ƙoƙarin kwaikwayon hanyar da Malam Shi’itu Ɗan Abdur-Ra’ufu ya yi amfani da ita a littafinsa mai suna :  JADDIL- AJIZ waƙaƙƙe na fiƙihu. Ana kyautata zaton cewa, malamin ne na farko da ya fara sanya ɗigagga a saman wasullan sama na haruffa dal (د )  da ba  (ب ) da kaulasan  ( ك ) domin su bayar da sautukan ɓ da ɗ  da kuma ƙ. Daga nan ne Rabinson ya ciranto wannan fasahar. Shi kuma sai ya sanya musu ɗigaggan a ƙasan haruffan b da d da kuma k, na haruffan Romawa waɗanda ke da muryoyin sautuka ɗaya da makamantansu na Larabci, domin su bayar da sautukan ɓ da ɗ da ƙ. Daga wannan za a iya fahimtar cewa, Robinson ya gina ƙa’idojin rubutu Hausar boko a bisa tsarin rubutun ajamin Hausa. Saboda haka ne Robinson ya gaza cim ma Schon a fagen raba kalmomin Hausa.

            Robinson ya bayar da gagarumar gudummawa a wannan haujin, musamman ida aka yi la’akari da talife-talifensa a ɓangaren Nahawu da adabin Hausa, waɗanda ya yi amfani da su wajen koyar da Turawan Mishan harshen Hausa a Jami’ar Ingila a ƙarshen ƙarni na goma sha tara (19) don su sami damar yaɗa addinin mishan a ƙasar Hausa, kamar yadda Bakura (2012:155) ya nuna. Da wannan aikin ne Turawan da suka biyo bayansa suka sami hasken kwaikwayon yadda Hausawa suka alamta sautukan muryoyin Hausa a tsarin rubutun ajamin Hausa.        

 

 

3.0 Tunanin Samar Da Sigar Abjadin Sautukan Hausa Daga Abjadin Ingilishi A Nijeriya

            Bayan samuwar makarantun boko da yaɗuwar ilimin zamani da ƙaruwar yawan ɗalibai da ke shiga makarantun a sassa daban-daban da ke farfajiyar Nijeriya Ta Arewa. Babbar matsalar da ta fara fuskantar ma’aikatar ilimi ita ce ta ƙarancin littattafan karantawa a makarantun. Wannan ne ya sa a daidai lokacin da Hanns Vischer ya tafi London hutu a shekarar 1911, ya gudanar da tarurruka da masu ruwa da tsaki wajen tafiyar da harkokin mulkin mallakar ƙasar Hausa, domin ganin an samar da littattafan karatu a Makarantar Nasarawa kafin ƙarshen hutun, saboda shiga sabuwar shekarar karatu a cikin watan Oktoba na shekarar 1911, wato bayan sallah ƙarama (Graham, 1966:83). Babbar matsalar da ya fara fuskanta, ba ta wuce ta rashin takamaiman abjadin da za su mayyaze saututtukan harshen Hausa a cikin sigar rubutun Hausar Boko ba (Graham,1966:83).

            A sakamakon fahimtar da ke akwai na cewa, abjadin Ingilishi bai ƙunshe da wasu sautukan Hausa, ya sa tun a cikin watan Afirilu na shekarar 1910, Bishop Tugwell ya bayar da shawara ga Hesketh Bell da ya ƙaddamar da wani kwamiti da zai ƙunshi mutane kamar Miller da Bargery da Vischer da H.R. Palmer da E.J. Arnett, domin su tattauna game da matsalar wasu sautukan harshen Hausa da yadda za a magance lamarin. Wannan ya sa Hesketh Bell ya yi na’am da shawarar, tare da ƙudurin jinkirta buga littafin da Hanns Vischer ya rubuta mai suna Hausa Primer , sai bayan kwamitin ya zauna, sun cimma matsaya game da sigar abjadin sautukan Hausa da za a yi amfani da su (C.M.S.,1910/(N.N.)No.37).

3.1 Gudummawar Turawan Mishan

            ‘Yan Mishan sun haɗu a Lakwaja suka gabatar da buƙatarsu ta a samar da wani tsayayyen abjadin da zai samar da wasu sautuka na  harsunan Hausa da Nufanci da Yarabanci da kuma harsunan da ke Lardin Binuwai. Harshen Hausa yana da haruffa 29, idan aka cire harafin “q“ da “x” a matsayin haruffan da suka amince a yi amfani da su wajen rubuce-rubucen adabin mishan (C.M.S., 1911/N.N.).

3.2 Gudummawar Hanns Vischer

            Hanns Vischer, shi ne mutun na farko a farfajiyar Nijeriya Ta Arewa da ya fara shata ƙa’idojin rubutun Hausar boko. Ya tsara su ne a daidai lokacin da yake riƙe da muƙamin Daraktan Ilimi a Nijeriya Ta Arewa. Ya rubuta maƙala da ya kira da suna:  Rules For Hausa Spelling, wadda aka buga a farkon shekarar 1912. Sai dai Yahaya (1988:126) ya ambaci Rules For Hausa Spelling a matsayin littafi ba maƙala ba. A tsarin abjadin Vischer an kawo haruffa 28 ne kawai, yayin da aka cire haruffan “ c” da “q” da “v” da kuma “x”.

            Visher ya nazarci matsalolin rubutun Hausa da na nahawunsa, a cikin wannan maƙalar tasa ya yi magana a kan baƙaƙe da wasulla da auren wasali kamar “ au”, da “ ai” da wakilin suna da zagi da yadda ake samar da jam’i da lokuttan aikatau. Haka ya bayyana cewa duk kalmomin Larabci da ake amfani da su a cikin harshen Hausa da suka danganci addini da shari’a za a rubuta su kamar yadda ake furta su da Hausa. Sunayen Larabci kuwa za a juya su ne kamar yadda suke. Yayin da kalmomin Ingilishi kuwa sai a fassara su zuwa Hausa (Vischer, 1912:3) da (Graham,1966:84) da (Zarruk,1980:116-7).

            Vischer, ya cancanci laƙabin Ɗanhausa, domin sautukan harshen Hausa ba su kuɓuce masa ba. Ya bayyana irin kalmomin da suka kamata a haɗa da waɗanda suka kamata a raba. Hasali ma, ba inda abjadinsa ya bambanta da na wannan zamanin sai a waɗannan muhallai:

1-      Amfani da harafin ch a madadin c misali, ya rubuta mache a madadi mace

2-      Ya kasa bambanta y da ‘y.

3-      Ya yi amfani da ɗigagga a ƙarƙashin hamzatattun baƙaƙe. misali: b.  d.  k. a madadin ɓ ɗ ƙ. Sai dai an sami saɓani a wannan Haujin, domin Yahaya (1988:126) cewa ya yi Hanns ya sauya alamar nan ta yin digo da almar yi wa harafi alamar hamza. Misali: b. a rubuta shi haka ‘b  wato ɓ , d. a rubuta ta haka: ‘d wato ɗ, yayin da k. za a rubuta shi haka: ‘k wato ƙ. Ya kuma nuna cewa da ƙa’idojin ne Bargery ya yi amfani wajen rubuta ƙamusunsa.

4-      Yakan sa ɗauri a muhallin da babu ɗauri. Misali: barra a madadin bara.

5-      Harafi r da ke ƙarshen Kalmar nasaba ko haddasau yakan saje da baƙin da ke biye da shi. Misali: rigad da a madadin rigar da, ko fitad da a madadin fitar da.

6-      Ya yi amfani da karan ɗori a sashen farko na tagwan Kalmar da ke sarrafuwa. Misali: ɗan-uwa; ‘yan-uwa. Su kuwa kalmomin da ake maimaitawa,sai a haɗe su ba za a sa musu karan ɗori ba. Misali: saƙesaƙe a madadin saƙe-saƙe.

3.3 Gudummawar George Parcy Bargery

            George Parcy Bargery ya bayar da tasa muhimmiyar gudummawa wajen kyautata ƙa’idojin rubutun Hausar Boko ta hanyar yi wa abjadin Hausa wasu gyare-gyaren da yake ganin sun dace da harshen Hausa. Daga cikin waɗannan gyare-gyaren da ya aiwatar sun haɗa da:-

-          Watsi da tagwan harafin “ ch” ya ɗauki “ C”. Sai dai ya amince da harafin “ sh” da “ ts”, a fagen ɗauri ne kawai yake amfani da “ –ssh” da “ –tts”, ba “-shsh” da “ –tsts” ba.

-          Amfani da waƙafi a gaban hamzatattun baƙaƙe a maimakon ɗigagga da ake sawa a ƙarƙashin baƙaƙen, misali: ‘b , ‘d , k’  

-          Rashin nuna alamar tsawon wasali, sai wurin da ake jin mai karatu zai ruɗe. Idan haka ya zama wajibi, sai a yi layi a saman wasalin kamar a wannan misali: “ ko ya aike ni ba na je ba.”

-          Rashin rarrabewa tsakanin ra-kaɗe da ra-buge. Ba kuma za a sa wata alama da za ta bambanta “n” ‘yar hanƙa da ‘yar hanɗa ba.

            Kusan za a iya cewa, abjadin Bargery ya fi kusanta da kuma dacewa da lafuzzan Hausa fiye da na sauran da suka gabace shi. Haka ƙa’idojinsa na raba kalmomi sun fi na sauran, kamar yadda Zarruk (1980:117-8) ya bayyana.

            Bayan wannan sahihiyar hanya da aka fara bi don ganin an samar da ingantaccen harsashen ginin ƙa’idojin rubutun Hausa, an kuma yi ƙoƙarin kafa wasu hukumomi a cikin gida da ƙasashen Turai da aka ɗora wa alhakin kyautata ƙa’idojin da kuma haɓaka shi. A ƙasashen waje hukumar da aka ɗora wa wannan aiki ita ce Hukumar Ƙasa Da Ƙasa Ta Nazarin Harsuna Da Al’adun Afirka:-

3.4 Gudummawar Hukumar Ƙasa Da Ƙasa Ta Nazarin Harsuna Da Al’adun Afirka

(International Insitute Of  African Languages And Cultures).

            Bincike ya tabbatar da kafuwar wannan hukuma a cikin watan Yuni na shekarar 1926, a ƙarƙashin jagorancin Frederick John Dealtry Lugard. Hukumar ta ƙunshi ‘yan majalisar gudanarwa mutun goma sha biyar (15). Hukumar tana tattare da ƙungiyoyi 28 da ke sha’awar nazarin al’amurran da suka danganci Afirka, da ke da wakilai a ƙasashe goma a cikin nahiyar ta Afirka, tare da ƙungiyoyin mishan daban-daban da suka haɗa da Forotastan da kuma Roman Katolika (International Institute, 1928:10).

            An kafa wannan hukuma ne domin ta samar da bayanai da suka danganci al’ummomin nahiyar Afirka. Ta bayar da shawarwari tare da tallafi ga Turawa da ke tafiyar da wasu ayyuka na musamman a wasu sassan Afirka, da kuma bayar da gudummawa a kan sha’anin binciken kimiyya da ilimin halayyar al’adun ɗan-adam da kuma ilimin harsuna.

            Hukumar ta sha alwashin danganta duk wani sakamakon binciken da aka aiwatar, da rayuwa ta haƙiƙa da ta shafi al’ummomin Afirka ta yadda binciken zai amfani jami’an mulkin mallaka da na sashen ilimi da na ɓangaren ma’aikatar lafiya da masu kula da jin daɗin walwalar al’umma da Turawa ‘yan kasuwa da ke zaune a nahiyar Afirka (Lugard, 1928:2). Domin ganin ta cimma burinta, hukumar ta samar da mujalla guda biyu, ɗaya an yi mata take: African Studies, wadda ta ƙunshi nazarce- nazarcen ƙwararru a kan wasu fannoni da suka keɓanta ga hukumar. Mujalla ta biyu kuwa an yi mata laƙabi da: African Documents, wannan mujalla ta ƙunshi ƙasidu da rubutattun matani, waɗanda aka samu a rubuce ko ta hanyar shifta daga ɗan Afirka, aka kuma fassara shi cikin harsunan ƙasar Turai. Irin waɗannan bayanai sun ƙunshi labarai da waƙoƙi da wasan kwaikwayo da kacici-kacici da karin Magana da tarihi da wasu hanyoyin gudanar da al’adu da ke ɗauke da bayanai nau’i-nau’i da suka haɗa da tsarin sarautun al’ummomi da al’adunsu da hikayar mafari da kuma uwa-uba, lamarin addini.

            Muhimmin aikin farko da hukumar ta fara sa wa a gabanta bayan da aka kafa ta shi ne, ƙoƙarin samar da daidaitaccen ƙa’idojin rubuta harsunan ƙasashen Afirka, wanda ya kwashe shekaru ba tare da haƙa ta cimma ruwa ba. Duk da haka Farfesa Westerman ya yi namijin ƙoƙarin shata wata ƙa’ida ta gaba ɗaya da ta shafi rubuta harsunan Afirka, ciki kuwa har da harshen Hausa, bayan ya sami damar ganawa da ƙwararru da dama, kamar yadda Lugard (1928) ya nuna.

            Sakamakon samuwar wannan hukumar ce  da ayyukan da ta zartar ya haifar da wanzuwar  gasar farko da  ta samar da littattafan gasa kamar:

1.      Hausa Stories                                                na H. G. B. Nuhu.

2.      Hausa Stories                                                na Malam Dodo.

3.      Zaman Dara                                      na Malam Ahamet Mettenden.

4.      Littafin Karatu Na Hausa               na Malam Bello Kagara.

5.      Takobin Gaskiya                              na Malam Nagwamatse Ɗan Alƙali Sakkwato, (Westerman, 1933:102-103). Sai dai ba a samu damar buga waɗannan littattafan ba.

3.5 Gudummawar Dr. R.M. East

            A daidai shekarar 1933, Bargery yana ƙoƙarin famar kammala ƙamusansa, yayin da Ministan Ilimi kuma Shugaban Ofishin Fassara, Dr. R. M. East yana azamar tsayar da ƙa’idojin rubutun Hausar boko. Ko da yake yana ƙudurin daidaita rubutun Ofishin Fassara da na Bargery. A Ofishin Fassara ana amfani da harafin ch, ana kuma saka wa hamzatattun haruffa ɗigagga a ƙasansu. Misalan wasu jumloli daga cikin Ladabin Chiniki a Labaru Na Da Na Yanzu :

·         Ya kamata ka d.ebe malafo ko lema.

·         In ya karb.a maka ka shiga.

·         Sai ka fara chinikin abin da ya kawo ka (1931:260).

Duk da haka sai da East ya bayar da umurnin yin amfani da ƙa’idar rubutun Bargery tamkar

Yadda yake, kamar yadda Zarruk (1980: 118) ya zo da bayani.

            Kasancewar Gwamnatin Jahar Arewa ta naɗa kwamiti tun a cikin shekarar 1932, wanda ya share kusan shekaru biyar yana kai da komawa kafin ya cimma matsayar yi wa haruffan b da d da k kugiya ko lanƙwasa a samansu maimakon ɗigaggan da ake yi a ƙasan haruffan. Domin ganin an cimma gurin da ya sa aka naɗa kwamitin, takanas sai Dr. East wanda yake ɗaya daga cikin ‘yan kwamitin, ya tafi Birnin Berlin da ke ƙasar Jamus, ya tattauna da Shugaban Cibiyar Nazarin Harsuna Da Al’adun Ƙasashen Afirka, a inda suka kai ga matsayar da a rinƙa rubuta ƙugiya a kan haruffan b domin samar da sautin ɓ, haka harafin d domin samar da sautin ɗ, da kuma harafin k domin samar da sautin ƙ.

            Yayin da East ya dawo, sai ya sanar da Gwamnatin Jahar Arewa, aka aminta tare da bayar da sanarwar amincewa da waɗannan alamun sautukan Hausa, a Mujallar Gwamnatin Nijeriya (Nigeria Gazett, Government Notice, No.396, ta 24 ga watan Maris na shekarar 1938, kamar yadda Yahaya (1988:127) ya zo da bayanin. Binciken Yahaya (1988:127) ya nuna cewa, R.C. Abraham ne farkon wanda ya fara amfani da waɗannan sababbin alamomin sautukan haruffan wajen rubuta ƙamusansa mai Suna: Dictionary of the Hausa Language wanda London University Press suka buga a cikin shekarar 1946.

3.6 Gudummawar Gwamnatin Nijeriya Ta Arewa

            Duk da kasancewar akwai ƙa’idojin rubuta Hausa da Gwamnati ta aminta a yi amfani da su, amma akan samu bambace-bambance wajen yadda wasu ke rubuta Hausa, musamman a fagen haɗa wasu kalmomi da raba su. Ga kuma kullun safiya harshen sai daɗa bunƙasa yake ta hanyar sababbin kalmomin Turanci da ke shiga cikin harshen Hausa ba kama hannun yaro. Don a hanzarta shawo kan waɗannan matsalolin da ke barazana ga rubutun Hausar boko, sai wani ɗan Majalisar Wakilai ta Jahar Arewa da ke Kaduna, da ke wakiltar Lardin Bauchi mai suna Malam Bawa Bulkacuwa, ya gabatar da shawarar cewa, “ya kamata a ba Mai Girma Gwamna shawarar a kafa wata hukuma da za a kira: Hukumar Harshen Hausa.

            Sakamakon wannan buƙata ce da Malam Bawa Bulkacuwa ya gabatar a zauren Majalisar Wakilai da ke Kaduna na kafa Hukumar Harshen Hausa domin a daidaita ƙa’idojin rubuta harshen Hausa, sai gwamnatin ta karɓi kiran, ta kuma kafa hukumar da aka kira da suna: “Hausa Language Board” wato Hukumar Harshen Hausa, a shekarar 1955 domin daidaita ƙa’idojin rubutun Hausa. Hukumar ta yi ƙoƙarin tace kalmomin da harshen Hausa ya aro daga wasu harsuna kamar Larabci da Turanci. Ta kuma gudanar da wasu ayyukan da suka taimaka wajen kyautatuwar rubutun harshen Hausa.

            Hukumar ta ɗauki ma’aikata da dama, shahararru daga cikinsu sun haɗa da: Alhaji Isa Kaita da Alhaji Aliyu Makaman Bida da Alhaji Tukur Sarkin Yawuri da Alhaji Abubakar Imam da Mr. C. Sanderson da Alhaji Abubakar Dokaji da Alhaji Abdulmalik Mani da Malam Maigari Yusuf da Mr. J. W. Court a matsayin sakataren hukumar.

            Daga cikin ayyukan da hukumar ta aiwatar sun haɗa da:

1.      Tabbatar da littafin ƙa’idojin rubutun Hausa mai suna: Rules For Hausa Spelling, tare da yi masa wasu gyare-gyaren da suka suka shafi haɗa kalmomi da raba su. Misali: a riƙa raba lamirin mutum da na lokaci kamar a irin waɗannan jumlolin:

·         Abin da su ke so      ba        Abin da suke so ba

·         Sa’ar da ya ke zuwa                        ba        Sa’ar da yake zuwa ba.

Kalmomi irin su saboda da kalmomin jama’u irin su koyaushe da kowane da ko’ina  sun raba su kamar haka:

·         Ko yaushe                 ba                    koyaushe                  ba

·         Ko wane                    ba                    kowane                      ba

·         Ko ina                                    ba                    ko’ina                         ba

·         Sabo da                     ba                    saboda                                   ba

Haka sun zartar da hukuncin haruffa za su daina sajewa a cikin kalmomi irin waɗannan:

·         duk da haka             ba                    dud da haka             ba

·         ya fitar da mu                       ba                    ya fitad da mu                      ba                                

kamar yadda Kirk-Green (1964:194) ya nuna. An ma buga gyare-gyaren da hukumar ta aiwatar game da ƙa’idojin rubuta Hausa a Mujallar Gwamnatin Jahar Arewa, wato Northern Nigeria Gazette, Northern Reginal Notice No.31 ta ranar 22 ga watan Janairu, shekarar 1957, kamar yadda Yahaya (1988:129) ya bayyana.

2.      An cimma matsayar yin amfani da wasu kalmomin bayanin nahawun Hausa kamar:

·         Ismi    ya koma         suna

·         Fi’ili    ya koma         abin da za a yi

3.      An tsara littafi wanda ya ƙunshi jerin kalmomin da harshen Hausa ya ara fiye da ɗari biyu da hamsin (250) waɗanda aka kira da suna Alphabetical List of Words Impoted into Hausa. Kamfanin ɗab’i mai suna: Baraka Press ta buga a shekarar 1958, kamar yadda Yahaya (1988:129) ya nuna.

4.      An tsara littafin keɓaɓɓun kalmomin Hausa, da aka kira da suna Glosseries of Technical Terms. Wannan littafin yana ɗauke da kalmomi dubu ɗaya da ɗari ɗaya (1100) da suka danganci keɓaɓɓun kalmomin da ake amfani da su a sassan ma’aikatu daban-daban.

Wannan ba ƙaramar gudummawa ba ce ga harshen Hausa da su kansu al’ummar Hausa.

Domin  irin wannan rawar da Turawa suka taka ta taimaka gaya wajen taskace tarihi da fasahohin magabatanmu tare da ƙara wa harshen Hausa ƙima a idon duniya, har al’ummomi daban-daban sun duƙufa a fagen nazarinsa.

4.0 Kammalawa

            Daga waɗannan bayanai za a fahinci cewa, Turawa sun shata ƙa’idojin rubuta Hausar boko ne, domin ƙoƙarin samar da wasu alamomin da za a rinƙa sa wa harruffan Romawa don su wakilci muryoyin harshen Hausa. Saboda Hausa tana da sautukan da babu irin su a harshen ƙasashen Turai. Haka sun yi ƙoƙarin samar da hanyoyin da za a riƙa haɗa harruffa ana gina kalmomi da jumlolin Hausa da yadda za a riƙa rarrabewa tsakanin kalma da kalma da hanyoyi da za a nuna wa mai karatu wurin tashi ko tsayawa ko iƙirari ko tambaya da sauransu. Abin kula a nan shi ne, sun aiwatar da haka ne domin wasu manufofi nasu. Duk da haka sakamakon aikin ya haifar da bunƙasar harshen Hausa, musamman idan aka yi la’akari da ayyukan da Turawa suka yi kamar: Hanns Vischer da G.P.Bargery da R.M. East da R.C. Abraham da sauransu. Wannan takarda ta gano tushen inda Robinson ya samo fasahar yi wa hamzatattun haruffa ɗigagga, wato daga aiki Malam Shi’itu Ɗan Abdur-Ra’uf na Birnin Zariya. Bayan shuɗewar Turawan Mulkin Mallaka, an samu wasu masana daga cikin Hausawa da ma masu sha’awar harshen Hausa da suka ba da tasu gudummawa ta hanyar ɗorawa daga inda Turawan suka tsaya. Masanan ne suka daɗa daidaita ƙa’idojin rubutun Hausar book tare da inganta shi, duk kuwa da irin matsalolin da harshen ya rinƙa fuskanta a hannun ‘yan ƙasa, bayan gushewar Turawan Mulkin Mallaka. A sakamakon irin yadda aka yi masa riƙon sakainar kashi, ta hanyar hana koyar da Hausa a makarantun furamare da ke faɗin Arewacin Nijeriya. Akwai buƙatar a ba da himma wajen binciken tsofaffin ayyukan magabatanmu da ke jibge a wuraren adana kayan tarihi domin fito da fasahohin magabatanmu.

Manazarta

Tuntuɓi mai takarda

Post a Comment

0 Comments