Ticker

6/recent/ticker-posts

Ginuwar Kagaggun Labaran Kallon Da Bahaushe ke Yi Wa Wasu Kabilu

 Akwai masu ganin bai kamata a kira Hausawa da suna ƙabila ba, sai dai a ce, su taro ne na ƙabilu daban-daban da suka cuɗanya da juna, kuma suka taru suna magana da harshe ɗaya. Ita kanta kalmar Hausa a wurin Bahaushe tana nufin harshe. Saboda akan ji y ace: “ ban ji wannan Hausar ba”. Wato bai gane wannan yare ke nan. Ko kuma ya ce: “ ya ji wata Hausa”. Wato ya ji ana magana da wani harshe, ko gwalangwanto.

mutane a cikin duhu

Ginuwar Ƙagaggun Labaran Kallon Da Bahaushe ke Yi Wa Wasu Ƙabilu

Dr. Adamu rabi’u bakura

arbakura62@gmail.com

08064893336

1.0 Tsakure

            Ana iya kallon kalmar Hausa a matsayin suna na harshe, kuma masu wannan harshe su ake kira Hausawa. Su al’ummar Hausawa ba su ɗauki kansu ƙabila ba, don kuwa a gurin su duk wanda ba Bahaushe ba ne, shi suke kira ƙabila, ko kuma bagware, tamkar yadda Larabawa suka ɗauki duk wanda ba Balarabe ba a matsayin Ba’ajame (Baubawa). Masana da dama sun bayyana Ƙabila da cewa: “ Al’umma ce mai asali ɗaya da yare ɗaya da kamannu (ƙirar jiki) kusan ɗaya da al’adun gargajiya iri ɗaya da ra’ayin zaman duniya (falsafa) ɗaya, da sauran irinsu. Kuma lallai ne cikin wannan al’umma kowa yana da’awar shi ɗan ƙabilar ne (Adamu, 19787) da (Adamu, 1997) da (Aamu,2011) da (Kwakwachi,2010).

            Akwai masu ganin bai kamata a kira Hausawa da suna ƙabila ba, sai dai a ce, su taro ne na ƙabilu daban-daban da suka cuɗanya da juna, kuma suka taru suna magana da harshe ɗaya. Ita kanta kalmar Hausa a wurin Bahaushe tana nufin harshe. Saboda akan ji y ace: “ ban ji wannan Hausar ba”. Wato bai gane wannan yare ke nan. Ko kuma ya ce: “ ya ji wata Hausa”. Wato ya ji ana magana da wani harshe, ko gwalangwanto.

            Sau da yawa akan sami ɗan haifaffen ƙasar Hausa, a tambaye shi ƙabilarsa, zai ce shi Bafillace ne ko Babarbare ko Banufe, amma bai san ko zo-in-kashe ka ba. Haka ana samun wasu jisin mutane zaune tare da wasu ƙabilun da ba sa jin Hausa, waɗanda harshen ƙabilun ya yi tasiri gare su, bas a jin Hausa, amma duk da haka suna da’awr  su Hausawa ne. Misali, Abakwa Riga na Wukari da Takum na Lafiya. Wannan kan faru ne a sakamakon cuɗanya da auratayya.

            Wannan maƙala ta ƙuduri aniyar gabatar da ƙwarya-ƙwaryar bayanai game da yadda Bahaushe ya ƙaga labaran raha game da wasu ƙabilu da zama tare ya haɗa shi da su. Ya gina labarin ne a sakamakon fahimtar wasu daga cikin halayen ƙabilun. Sai dai muƙalar za ta taƙaita ne kawai a kan al’ummomi kamar Fulani, Buzaye, Nupawa, Yarbawa da Inyamurai tare da bayar da haske game da sanadin haɗuwar Hausawa da su.

2.0  Gabatarwa:

            Mafi yawan Hausawa musulmi ne, waɗanda yawancin al’adunsu sun dogara ne a kan yadda Musulunci ya yi tanadi. Sai dai ɗan abin da ba a rasa na daga al’adun gargajiya, musammman ta haujen Maguzawa. Ta fuskar mu’amala da iyaye ko dangi ko abokai ko shugabanni ko maƙwabta ko wanin waɗannan, yawanci ana gudanar da su ne kamar yadda addini ya tanada.

            A sakamakon irin tasirin da addinin Musulunci ya yi a rayuwar Bahaushe Musulmi, shi ya wanzar da zaman lumana a tsakaninsa da sauran jinsin ƙabilu da zaman tare ya haɗa su. Sakamakon wannan zama ne, har Bahaushe ya sami damar fahimtar halayen ƙabilun, musamman na wauta, son abin duniya, rowa, ƙazanta da sauransu. Fahimtar irin waɗannan halayyar mutane shi ya bayar da damar samar da labarai da suka dace da halayen ƙabilun, ya riƙa bayarwa da niyyar tsokana don a yi dariya.

3.0 Haɗuwar Hausawa Da Fulani :

            Fulani, mutanen Fula ne, suna zaune a ƙas ashe kamar Mali daSenegal. Fulani nau’i biyu ne, Fulanin daji ( Bararoji) da Fulanin Soro. Fulanin daji su ke kiwon shanu. Suna yawo daga wannan wuri zuwa wancan domin neman makiyaya da rowan sha saboda dabbobinsu. Su kuwa Fulanin Soro rukuni - rukuni ne da suka haɗa da: Torankawa da Sulluɓawa da Jahunawa da sauransu. Ana kyautata zaton sun fara zuwa ƙasar Hausa zamanin Sarkin Kano Yakubu wanda ya yi mulki a tsakanin shekarar 1452-1463 (Ibrahim, 1970:103). Fulanin daji a koyaushe suna cikin jeji, babban abin da ke haɗa su da Hausawa shi ne kasuwanci, wato cinikin mai da nono ko shanu da kanwa da gishiri da sauransu.

            Fulanin Soro kuwa suna zaune cikin garuruwa suna karatu da karantarwa. Daga cikin sun e aka sami Malam Musa Jakollo kakan Shehu Usman Ɗanfodiyo wanda ya zauna a Birnin Ƙonni da ke cikin ƙasar Gobir a wancan zamani (Ibrahim,1970) da (T/ Mafara,1999) da ( Wazirin Sakkwato). An sami muhimmiyar alaƙa tsakanin Hausawa da Fulani bayan kammala jahadin Shehu Usman Ɗanfodiyo, wanda ya yi sanadin mayar da ragamar mulkin ƙasar Hausa a hannun Fulani har zuwa farkon ƙarni na ishirin lokacin da Turawa suka ƙwace mulki daga hannun Fulani. Irin wannan zama na masu riƙe da mulki da waɗanda aka ƙwace wa mulki, ya wanzar da kusanta ta ƙud-da-ƙud da hulɗa tsakanin Bahaushe da Bafillatani da ta haifar da raini a tsakaninsu. Kuma ita ta ba Bahaushe damar fahimtar halayen Bafillatani musamman wajen wauta da rashi wayewar kansa, har ma yake ganin Bafillatani a matsayin sakarai maras wayon zaman duniya. A kan haka ne Bahaushe ya gina labarai don ya nuna wautar bafillatani kamar haka:

3.1 Ƙagaggen Labari Game Da Fulani

            Wai wani Bafillatani ne, rowan sama ya dake shi, ga sanyi, ga dare.

            Sai ya zo ya sami mafaka. Ya tarar an hura wuta, ana gasa gyaɗa. Da

            Gyaɗa ta gasu, aka ba Ɗanfulani ya ci sai y ace, “Mhm”! Aka ce, “yaya

            dai Ɗanfulani?” Sai ya ce “ Ai mu oya, wallahi ko lahira wuta muka zaɓa

            da kwandon gyaɗa”.

4.0 Haɗuwar Hausawa Da Buzaye

            Azbinawa suna zaune tare da Bugaje (Buzaye) a bakin saharar yashi arewa da ƙasar Hausa. Buzaye kuwa asalinsu bayin azbinawa ne (Ibrahim, 1970). Dukkansu suna Magana da harshe ɗaya ne, suna da al’ada iri ɗaya. Suna ado da baƙaƙen tufafi ba ka raba su da naɗa rawani a kowane lokaci

            Azbinawa da Buzaye sun fara cuɗanya da Hausawa tun kusan lokacin da aka kafa ƙas ashen Hausa bakwai. An ce shekarar da su Bagauda suka sara Kano tare da manya-manyan gonaki, kasancewar wurin sabo ga kuma taki mai yawa, sai Allah ya ba su amfanin gona mai yawa. Da shekara ta zagayo sai aka yi yunwa mai tsanani wadda ta shafi kusan dukkan sassan ƙasashen Hausa har ma da ƙasar Azbin. Wannan yunwa ta haifar da kwararar mutane zuwa Kano, don su sami abinci. Cikin mutanen da suka yi ƙaura zuwa Kano har da Azbinawa da Buzaye (Ibrahim, 1970).

            Da aka sami ƙoshi da yalwar abinci a ko’ina, sai yawancin al’ummomin da suka zo Kano, suka koma ƙasashensu, amma su Buzaye sai suka ƙI bin Azbinawa suka yi zaman su a Kura ta ƙasar Kano (Ibrahim, 1970). Kasancewar Buzaye gwanin ƙira da rinin baƙaƙen tufafi, sai  suka duƙufa ga sana’arsu. Wannan ya ‘yan’uwansu suka rinƙa zuwa Kano suna sayen baƙaƙen tufafi, ta haka ciniki ya yi yauƙi har Hausawa suka tsunduma cikin safarar, suna kai hajar baƙaƙen tufafi ƙasar Azbin.

            Babbar hanyar nan ta ciniki ta da, wadda ta tashi daga bakin kogin Bahar Rum ta ratsa ta hamadar yashi ta zarce zuwa ƙas ashen Hausa, ta ƙara kawo cuɗanyar Hausawa da Buzaye, domin hanyar ta ratsa garin Azbinawa. An yi amfani da ita wajen fataucin bayi da wasu kayayyakin ƙasar Turai zuwa ƙasar Hausa. An ci gaba da amfani da hanyar har bayan zuwan Turawa, musamman daga kudanci sahara zuwa ƙas ashen Hausa, wajen cinikin gishirin mangul da manda da kanwa da dabbobi. Buzaye su ne madugun wannan tafiya. Idan sun sayar da kayansu sai su sayi baƙaƙen tufafi da goro su tafi da su ƙasarsu (1970).

            Sakamakon wannan daɗaɗɗiyar mu’amala tsakanin Hausawa da Azbinawa da Buzaye ta ba Bahaushe sararin fahimtar ɗabi’ar Buzu ta tsananin son kuɗI, don haka ne matansu kan tafi suna bin mutane suna cewa: “ Muna bara muna kitso muna karuwa”. Wato a            nan ida           n sadaka ta samu ko kitso suna so, in kuma akwai mai buƙatar su a shirye suke. Ta la’akari da wannan ne ya sa Bahaushe ya tsara labari don ya nuna irin yadda yake kallon Buzu.

4.1 Ƙagaggen Labari Game Da Buzu

            “Wai wani Buzu ne cikinsa na ciwo, shi kuma yana sayar da kanwa, sai aka

            Ce, a nemo kanwa a jiƙa masa, sai ya ce a je cikin kindinsa a saka sisin kwabo

            a ɗauko kanwar a jiƙamasa”.

Ba nan kaɗai ta tsaya ba, domin Bahaushe na kallon Buzaye a matsayin mutane marasa hankali, ga su da tsananin wauta.

5.0 Haɗuwar Nupawa Da Hausawa

            Ƙasar Nupe tana gefen Kogin Kwara da ke kan hanyar da Hausawa kan bi wajen zuwa fataucin goro a ƙasar Yarbawa. Hasali ma an sami mu’amalar cinikayya a tsakanin Nupawa da Hausawa. Hausawa kan sawo irin manyan rigunan nan da Nupawa ke ɗinkawa masu aiki da ake kira girken Nupe da kwakwata waɗanda suke da farin jinni a wajen Hausawa, musamman attajirai da sarakuna, ga kuma kayan ƙarau da manja da suke samarwa. Irin waɗannan sana’o’i da Nupawa suka ƙware, sun wanzar da kyakkyawar mu’amala a tsakanin su da Hausawa (Tukur,1978), tun kafin zuwan Turawa.

            Sakamakon jahadin Shehu, wani muhimmin ne wajen ƙara kawo cuɗanyar Hausawa da Nupawa. Shi ne ma sanadin zamansu a ƙarƙashin daula ɗaya, domin mafi yawan su musulmi ne( 1978). Sakamakon wannan cuɗayyar har an sami ƙulluwar auratayya a tsakanin Nupawa da Hausawa. A daidai shekarar 1807-1833 Sarkin Katsina Ummarun Dallaje ya auri Banupiya wadda ta haifa masa ‘ya’ya kamar yadda (Tukur, 1991)  ya nuna. Ana kyautata zaton irin wannan dangantaka ta ɗan namiji da ɗan mace ita ta wanzar da samuwar labaran raha a tsakanin Hausawa da Nupawa. Misali Bahaushe ya yi nazari ya gane cewa, Banupe mutun ne mai maƙo, sai ya samara da labarin dakon Banufiya.

5.1 Ƙagaggen Labari Game Da Nupawa

            “Wai Banufiya ce ta ɗora wa ɗandako kaya mai nauyi ya kai mata gida. Ya

            Kai kayan da ƙyar. Da aka sauke, sai t ace da shi ya shiga rumfarta. A cikin

            Rumfar ya shiga ɗaki. A cikin ɗakin (uwar ɗakan) ya duba ƙarƙashin gado

            Akwai tukunya. Cikin tukunyar akwai gwangwani, a cikinsa akwai ƙunshi

            Leda ya ɗauko ya duba zai tarar da ƙullin tsumma, ya kwance zai ga kwabo,

            ya ɗauki ɗari ladan dakonsa”.

Ganin wannan wahalar da zai sake sha wajen neman ladan dakon, sai ɗandakon ya ce ya yafe. Idan muka dubi wannan labari za a fahimci an gina shi ne a kan fahimtar da ke akwai ta mutsiltsila da tsananin matsolancin Banufe.

 

 

6.0 Haɗuwar Hausawa Da Yarbawa 

            Ƙasar Yarbawa tana kudu maso yamma da Kogin Kwara. Cinikin goro shi ne farkon abin day a haifar da cuɗanya tsakanin Hausawa da Yarbawa. Hausawa al’umma ce mai sha’awar cin goro, matansu kuma suna cin hannun ruwa (goro mai yauƙi), wanda ba a samun su sai a ƙasar Yarbawa. Wannan ne ya sa Hausawa tafiya ƙasar Yarbawa domin fataucin goro a ƙasa da  kuma jakuna. Sun kira waɗannan ƙasashe da suna “Gonja”. Wannan suna bai keɓanta a kan ƙas ashen Yarbawa ba, har ya haɗa da ƙas ashen Ghana, domin suna tafiya can wajen safarar goro.

            Jahadin Shehu ya ƙara kawo cuɗanyatsakanin Hausawa da Yarbawa. Shi ne sanadin zaman ƙasar Ilori da wasu sassan ƙas ashen Yarbawa a ƙarƙashin daula ɗaya tare da Hausawa(Ibrahim,1970). Irin wannan zaman tare ya ci gaba da wanzuwa har zuwa kafuwar mulkin mallakar Turawan Ingila. Kafa mulkin mallaka ya ƙara haɗe ƙas ashen Yarbawa suka kasance a ƙarƙashin ƙasa ɗaya da suna Nijeriya, wanda hakan ya ƙara haɓaka mu’amala tsakanin Hausawa da Yarbawa. Irin wannan shaƙuwa ta tsawon lokaci ta ba Bahaushe dama fahimtar halaye da ɗabi’un Yarbawa. Shi ya sa Bahaushe ke kallon Bayarbe da wasu halaye da suka danganci tsattsauran ra’ayi da tsumulmula game da kuɗI ko dukiya. Wannan ya ba Bahaushe tsara labari domin ya shammaci Bayarbe a kan halayensa da ya sani game da dukiya.

6.1 Ƙagaggen Labari Game Da Bayarbe

            “ Wai wani Bayarbe ne mai suna Baba Alabi, ya yi adashi tare da Hausawa.

            Sai Bahaushe ya karɓi kwasar farko. Ana cikin haka sai kwasa ta zo ga Baba

            Alabi. Da ya zo karɓar kuɗinsa, sai ya taras da wanda ya ɗauki kwasar farko

            ya mutu. Kowa ya ba shi zubi saura na mamaci, sai aka gaya masa cewa, ya

            mutu. Daga nan Baba Alabi, ya ce kai! Wannan “ Filan ni”. Wai a nan yana

            nufin bai tashi mutuwa ba sai da ya karɓI kuɗin mutane? Don haka shi bai yarda

            ba.”

7.0 Haɗuwar Ibo ( Inyamuri) da Bahaushe

            Zuwan Turawan Mulkin Mallaka da tabbatar kafuwar mulkinsu na ɗaya daga cikin sanadin cuɗayyar Hausawa da Ibo. Haka samuwar hanyoyin sufuri kamar titunan matoci da layukan jirgin ƙasa da ta taso daga Legas ta zarce zuwa Kano mai tsawon mil 704 wadda aka kammala a shekarar 1911. Ita ma hanyar jirgin ƙasa da ta taso daga Port Harcourt zuwa Kano mai tsawon mil 600 da aka sami kammalawa a 1926 ta taka muhimmiyar rawa wajen zama sinadarin haɗuwar Bahaushe da Ibo (Crowder, 1968). Hasali ma hanyoyin sun haɗa babbar cibiyar kasuwancin ƙasar Hausa da sauran sassan manyan garuruwan da ke cikin Nijeriya. Irin waɗannan hanyoyi sun taimaka matuƙa wajen cuɗayyar Hausawa da wasu ƙabilu, musamman ƙabilar Ibo da suka taso daga garuruwa kamar Legas da Enugu da Ibadan suka zauna a wurare kamar Kano da Zariya da Jos da Gusau da Sakkwato domin neman riba ta hanyar kasuwanci (Osaghae, 1994). Ta wannan mu’amala ce Bahaushe ya fahimci cewa, baa bin da ya fi ƙyama a rayuwarsa irin kuturu, sai ya ƙirƙiro labarin hammer Inyamiri.

7.1 Ƙagaggen Labari Game Da Inyamiri 

            “ Wai wani inyamiri ne yana tsaye bai san cewa, wani kuturu mai zubar

            mugunya na tsaye a bayansa ba. Sai Inyamiri ya yi hamma ba tare da ya

            sa hannu ya rufe bakinsa ba. Ganin haka sai kuturu ya cusa dugun hannunsa

            a bakin Inyamiri, y ace, “shege, kafiri, ba salati ba rufe baki”. Sai Inyamiri

            ya rufe baki da dungun kuturu. Ba a Ankara ba sai Inyamiri ya faɗI somamme,

            aka yayyafa masa ruwa”.            

             

             8.0 Kammalawa:

            Allah Ya yi wa ɗan Adam baiwa da basiri da tunani ta yadda zai iya ƙwanƙwance abubuwa ta kowace fuska ya same su. Wanna ne ya ba shi damar bayyana ra’ayinsa game da duk wani abu da yake kusa da shi. Ba Bahaushe ne kaɗai ke da wannan sifa ba. Kowace al’umma ma akwai yadda take kallon wata al’umma da zaman tare y agama su, da yadda suka suka fahimci juna, fahimta mai kyau ko maras kyau ko da kuwa iyaye ne, sai daikunya ko tsoro ko wani abu ya hana a bayyana. A sakamakon haka ne aka kalato ire-iren labaran da Bahaushe ya ƙaga a kan al’ummomi daban-daban da suka haɗa da: Fulani da Buzaye da Nupawa da Yarbawa daga ƙarshe aka cika da Inyamiri(Ibo). Sai dai idan aka nazarci irin waɗannan labaran barkwanci za tarar akwai birbishin kishi a mafi yawan su. Wasun su an ƙaga su ne domin a huce haushe. Misali, barkwancin da ke wanzuwa a tsakanin Bahaushe (kaɗo/ haɓe), an aiwatar da shi ne a sakamakon haushin da Bahaushe ke ji na zafin Fulani sun ƙwace masa mulkin ƙasarsa ta haihuwa. Shi ma sai ya samara da irin waɗannan labarai domin ya muzanta Fulani. Haka lamarin zai kasance idan aka zurfafa bincike a kan labaran da aka gina game da sauran ƙabilu.

 

MANAZARTA

Tuntuɓi mai takarda

Post a Comment

1 Comments

ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.