Wannan waƙa na ɗaya daga cikin jerin waƙoƙin da “Fasihi Usman Mai Riga Jega” ya rubuta. Usman matashi
ne da Allah ya zuba wa basirar gudanar da abubuwa daban-daban. Ciki har da
baiwar rubuta waƙoƙi masu matuƙar ilimantarwa da faɗakarwa. Yana zaune a garin Jega da ke jahar Kebbi a
Nijeriya.
Usman Mai Riga Jega
07067998315
Mairigajega@gmail.com
Magada Annabawa
1- Rabbana kareni a cikin dare,
Ko da rana kar in sha
wuya.
2- To bani iko ya sarkina gwani,
Don ban da kamarka a duniya.
3- Yau zan yi waƙata yar Zamani,
Domin abin da ke cikin
zuciya.
4- Salatin Manzona ni shi
na riƙe,
Koda yaushe da shi nake godiya.
5- Alihi da sahabbai ai suna biye,
Dukkansu ina son su a zuciya.
6- Malammai waƙar nan fa ta ku ce,
To sai ku karɓa ban da
hayaniya.
7- Kar ku damu yanzu zan bayyana,
Tunda wasu sai sun yo tambaya.
8- To malammai ai ku ne ginshiƙai,
Tunda An ce ku ne Magada Anbiya.
9- Duniyar ga da ku ake yi lallai ko'ina,
Kar ku yarda ku ɗau son
zuciya.
10- Kar ku yarda zuga ta kifar da ku,
Kunga ƙarshe a sakaku a hawuya.
11- Da'awa ita ma sai ku yo da kyau,
Harshenku please sai ku tausaya.
12- Ku ne ke cewa ai tuni Allah ya faɗa,
Kar a same ku cikin wai kun antaya.
13- Masu zaginku kuma ku yi Haƙuri,
Don kun kasance a tsaka mai wuya.
14- To fa ai Allah ne ya Aza muku shi,
Kar ku bar shaiɗan zai
muku dariya.
15- Kun san wasu sam ba su da hankali,
Ba illimi sannan ba sa yin tambaya.
16- Kai kar ku zam masu yin jiji da kai,
Don Allah fa baya son mai fariya.
17- To wanda duk ke zagin mallamai,
Ai don aƙida ne ko
kuma ƙungiya.
18- Laifin wani sam baya shafar wani,
Ayar Alƙur'ani ku
je ku mu bibiya.
19- Wasu aikinsu ƙazafi ga mallamai,
Kai musamman ma social
midiya.
20- San da duk malami yai kwalliya,
Sai su ce kai Malam ya
cika fariya.
21- Matuƙar Ko Malam na da Arziki,
Sai suce lallai da Alamar
tambaya.
22- To in har Malam Motoci gareshi,
Sai su ce wai Malami ake wa
jiniya?
23- Malami in da'awa ya je a ƙasar waje,
Garesu Malam ba ya zama
Najeriya.
24- Su ce ba ya saye kuma bai saisuwa,
Kuɗinmu da
su yake ta sharholiya.
25- To in ko Malam ya yo musu raddi,
Sai su ce ai an yi dubunka
a Duniya.
26- Na ga Malam an zagai a gidansa,
Wallah zagin kuma mai taɓa zuciya.
27- Waƙata Ban cire kowa a cikinta ba,
Amma kuskurena ku yo min
yafiya.
28- Wallahi falalar ilimi kam tai yawa,
Banda ilimi ballaima ku yi
tambaya.
29- To ashe neman ilimi lallai da ƙyar,
Duk wanda ke so sai ya yo juriya.
30- Wanda duk ka gan shi fa
da illimi,
Rayuwarsa ta baya je ka yi
tambaya.
31- Don Allah Mallammai ku yi hankali,
Wallahi Ku ji tsoron wannan Duniya.
32- Na san komai zan faɗi ai kun sani,
Haka yassa ni zan ɗan tsaya.
33- Gafara nake nema gun Sarki gwani,
To ya Allah ka gyara muna
zuciya.
34- Usman Mai Riga sunan mai batun,
Jega can nake gun mai
Tambaya.
35- Ma sha Allah tammat waƙa ta cika,
Ai da iyawar Sarkin nan mai
kariya.
0 Comments
Rubuta tsokaci.