Ticker

6/recent/ticker-posts

Magada Annabawa



Wannan waƙa na ɗaya daga cikin jerin waƙoƙin da “Fasihi Usman Mai Riga Jega” ya rubuta. Usman matashi ne da Allah ya zuba wa basirar gudanar da abubuwa daban-daban. Ciki har da baiwar rubuta waƙoƙi masu matuƙar ilimantarwa da faɗakarwa. Yana zaune a garin Jega da ke jahar Kebbi a Nijeriya.

Usman Mai Riga Jega
07067998315
Mairigajega@gmail.com
Magada Annabawa

1- Rabbana kareni a cikin dare,
  Ko da rana kar in sha wuya.

2- To bani iko ya sarkina gwani,
Don ban da kamarka a duniya.

3- Yau zan yi waƙata yar Zamani,
 Domin abin da ke cikin zuciya.

4-  Salatin Manzona ni shi na riƙe,
 Koda yaushe da shi nake godiya.

5- Alihi da sahabbai ai suna biye,
Dukkansu ina son su a zuciya.

6- Malammai waƙar nan fa ta ku ce,
To sai ku karɓa ban da hayaniya.

7- Kar ku damu yanzu zan bayyana,
Tunda wasu sai sun yo tambaya.

8- To malammai ai ku ne ginshiƙai,
Tunda An ce ku ne Magada Anbiya.

9- Duniyar ga da ku ake yi lallai ko'ina,
Kar ku yarda ku ɗau son zuciya.

10- Kar ku yarda zuga ta kifar da ku,
Kunga ƙarshe a sakaku a hawuya.

11- Da'awa ita ma sai ku yo da kyau,
Harshenku please sai ku tausaya.

12- Ku ne ke cewa ai tuni Allah ya faɗa,
Kar a same ku cikin wai kun antaya.

13- Masu zaginku kuma ku yi Haƙuri,
Don kun kasance a tsaka mai wuya.

14- To fa ai Allah ne ya Aza muku shi,
Kar ku bar shaiɗan zai muku dariya.

15- Kun san wasu sam ba su da hankali,
Ba illimi sannan ba sa yin tambaya.

16- Kai kar ku zam masu yin jiji da kai,
Don Allah fa baya son mai fariya.

17- To wanda duk ke zagin mallamai,
 Ai don aƙida ne ko kuma ƙungiya.

18- Laifin wani sam baya shafar wani,
 Ayar Alƙur'ani ku je ku mu bibiya.

19- Wasu aikinsu ƙazafi ga mallamai,
 Kai musamman ma social midiya.

20- San da duk malami yai kwalliya,
  Sai su ce kai Malam ya cika fariya.

21- Matuƙar Ko Malam na da Arziki,
 Sai suce lallai da Alamar tambaya.

22- To in har Malam Motoci gareshi,
 Sai su ce wai Malami ake wa jiniya?

23- Malami in da'awa ya je a ƙasar waje,
 Garesu Malam ba ya zama Najeriya.

24- Su ce ba ya saye kuma bai saisuwa,
Kuɗinmu da su yake ta sharholiya.

25- To in ko Malam ya yo musu raddi,
 Sai su ce ai an yi dubunka a Duniya.

26- Na ga Malam an zagai a gidansa,
 Wallah zagin kuma mai taɓa zuciya.

27- Waƙata Ban cire kowa a cikinta ba,
 Amma kuskurena ku yo min yafiya.

28- Wallahi falalar ilimi kam tai yawa,
 Banda ilimi ballaima ku yi tambaya.

29- To ashe neman ilimi lallai da ƙyar,
Duk wanda ke so sai ya yo juriya.

30-  Wanda duk ka gan shi fa da illimi,
 Rayuwarsa ta baya je ka yi tambaya.

31- Don Allah Mallammai ku yi hankali,
Wallahi Ku ji tsoron wannan Duniya.

32- Na san komai zan faɗi ai kun sani,
Haka yassa ni zan ɗan tsaya.

33- Gafara nake nema gun Sarki gwani,
 To ya Allah ka gyara muna zuciya.

34- Usman Mai Riga sunan mai batun,
 Jega can nake gun mai Tambaya.

35- Ma sha Allah tammat waƙa ta cika,
 Ai da iyawar Sarkin nan mai kariya.

Post a Comment

0 Comments