Ticker

6/recent/ticker-posts

Alƙalami



Wannan waƙa na ɗaya daga cikin jerin waƙoƙin da “Fasihi Usman Mai Riga Jega” ya rubuta. Usman matashi ne da Allah ya zuba wa basirar gudanar da abubuwa daban-daban. Ciki har da baiwar rubuta waƙoƙi masu matuƙar ilimantarwa da faɗakarwa. Yana zaune a garin Jega da ke jahar Kebbi a Nijeriya.

Usman Mai Riga Jega
07067998315
Mairigajega@gmail.com

ALƘALAMI

1- Farko ni sai na kira gwanina,
    Allah sarki mai biyan buƙatu.

2- Roƙonka na ke yi dare da rana,
    Ka ban baiwar da zan wadatu.

3- To zan yi salatina wurin ma'aki,
     Muhammadu Abban su Bintu.

4-  Alihi da sahabbansa suna raina,
    Da duk wanda ya bisu za ya ƴantu.

5-  Ku zo ku ji yau ga sabon bayani
     Wanda na tsara kan abin rubutu.

6-   Matuƙar dai yanzu ana karatu,
     To ashe dai tilas ne a yo rubutu.

7- kunsan ai Alƙalami iri-iri ne,
   Amma ai kowane yana rubutu.

8-  Alƙalami amfaninsa fa ba iyaka,
    Domin ta silarsa ne na fahimtu.

9- In har ko kwalba ce uwar turare,
     To ashe Alƙalami ne uban karatu.

10-  Sam ba a zuwa gona in ba fatanya,
       Makaranta ko a je da abin rubutu.

11- Mu kam Shi ne zamu ƙanƙamewa,
     To meye amfanin kiɗan na shantu.

12- Kai! Jahillci shi ne ke ta yaudararmu,
      wallahi rashin ilimi ke sa a cutu.

13- Kai! Tabbas Alƙalami abin yabo ne,
      Lambu gun ka kowa ya ke ta hutu.

14- Ku duba ko zamani na manzomu,
      To ko lokacin ma ai na ji ana rubutu.

15- Dubi san da duk wahayi ya sauka,
       Anan lokacin wasu na yin rubutu.

16- To wanda ba ya yi ya ba mu hanya,
       Ni yanzu ma za ni fara yin rubutu.

17- Wanda ya riƙeshi ai  ba ya kunya,
      Tabbas zai ɗaukaka cikin halittu.

18-  Wayyo! Ni yau wai mi za ni cewa,
        Ni ina tausan wanda bai rubutu.

19- Kai kowane yare na duniyar nan,
     Idan kun bincika suna yin rubutu.

20- Samun Alƙalami mun yi murna,
     Don ga shi muna ta yin rubutu.

21- Ya Yan'uwa ni ina kiranku,
     Ku san darajar abin rubutu.

22- Ni Usman Mai Riga ake kirana,
     Garin Jega na ke kar ku zautu.

23- Waƙar nan to zan tsaya nan,
      Na gaida Alƙalami abin rubutu.

24- Godiya gun sarkinmu Allah,
     Wanda shi ne ya yi duk Hallitu.

Post a Comment

0 Comments