Wannan waƙa na ɗaya daga cikin jerin waƙoƙin da “Fasihi Usman Mai Riga Jega” ya rubuta. Usman matashi
ne da Allah ya zuba wa basirar gudanar da abubuwa daban-daban. Ciki har da
baiwar rubuta waƙoƙi masu matuƙar ilimantarwa da faɗakarwa. Yana zaune a garin Jega da ke jahar Kebbi a
Nijeriya.
Usman Mai Riga Jega
07067998315
Mairigajega@gmail.com
Kukan Kurciya
1- To ya sarkina ka bani sa'a,
Akan waƙar ga da
za ni ƙago.
2- Kullum salatina wurin Ma'aki,
Ɗan
Abdallah gun mu shi ne jigo.
3- Duk ko wanda ke zagin Sahabbai,
Ranar mutuwarsa ransa za
a fisgo.
4- Dubi yaro mai Abin mamaki ne,
Don wata rana shi ne ke
zama Ango.
5- Kai! Yaro wallahi miƙe ka bar fashi,
tabbas ai haushi na gun
uwar Raggo.
6- Lallai mai son ka shi ne ke ta begenka,
Domin shi so na can
cikin ɓargo.
7- Kun san fa Amarya dole ta yo ƙunci,
Matuƙar yau
aka ce babu ran Ango.
8- Tabbas abin mamaki yana da yawa,
Yau mai nama ya zagi mai
mango.
9- Ai kun san kurin wada na banza ne,
Dubi shi ma ya san ba ya
kai dogo.
10- To Matuƙar ko in za a yo layya,
An faɗa an fi so kowa ya sai
Raago.
0 Comments
Rubuta tsokaci.