Ticker

6/recent/ticker-posts

Kukan Kurciya



Wannan waƙa na ɗaya daga cikin jerin waƙoƙin da “Fasihi Usman Mai Riga Jega” ya rubuta. Usman matashi ne da Allah ya zuba wa basirar gudanar da abubuwa daban-daban. Ciki har da baiwar rubuta waƙoƙi masu matuƙar ilimantarwa da faɗakarwa. Yana zaune a garin Jega da ke jahar Kebbi a Nijeriya.

Usman Mai Riga Jega
07067998315
Mairigajega@gmail.com
Kukan Kurciya

1- To ya sarkina ka bani sa'a,
    Akan waƙar ga da za ni ƙago.

2- Kullum salatina wurin Ma'aki,
    Ɗan Abdallah gun mu shi ne jigo.

3- Duk ko wanda ke zagin Sahabbai,
    Ranar mutuwarsa ransa za a fisgo.

4- Dubi yaro mai Abin mamaki ne,
    Don wata rana shi ne ke zama Ango.

5- Kai! Yaro wallahi miƙe ka bar fashi,
   tabbas ai haushi na gun uwar Raggo.

6- Lallai mai son ka shi ne ke ta begenka,
    Domin shi so na can cikin ɓargo.

7- Kun san fa Amarya dole ta yo ƙunci,
   Matuƙar yau aka ce babu ran Ango.

8- Tabbas abin mamaki yana da yawa,
    Yau mai nama ya zagi mai mango.

9- Ai kun san kurin wada na banza ne,
   Dubi shi ma ya san ba ya kai dogo.

10- To Matuƙar ko in za a yo layya,
      An faɗa an fi so kowa ya sai Raago.

Post a Comment

0 Comments