Ticker

6/recent/ticker-posts

Waƙar Kidnafas

Wannan waƙa jaje ne ga waɗanda abin ya shafa tare da jan hankali ga gwamnati da sauran al'umma baki ɗaya. Muna addu'ar Allah ya kare mu da imaninmu. Amin.

WAƘAR KIDNAFAS

Abddulhamid M. Sani
(Malumman Matazu)
GSM : 08037868097

Allah da sunanka nake farawa,
Kai kay yi loto kullum yake juyawa,
Kai ne ka raya Allahu kai ka matarwa,
Ka halicci fajir sannan kayo Mumnawa,
Zan so ku ji ni ya al'umarmu mutane.

Kafin na fara na yo salati farko,
Wurinsa Manzo Shalele da aka aiko,
Duk Annabawa shi ne ya zam cikamakko,
Sannan iyalai sahabihi nai anko,
Ban ƙin na sanya nagargaru a mutane.

Yau firgici ne ya mamaye yankinmu,
Tsoro a kullum daɗo yake jama'armu,
An sace mata an sace har yaranmu,
Masu kuɗinmu an sace sarakanmu,
Abin takaicin wai gwamnatin jama'a ne.

Cikin gidanka a zo a ɗau maka mata,
Koko ɗiyanka a bi su har makaranta,
Waninmu fasinja yana kan mota,
Yau al'umarmu muna cikin firgitta,
Halin ƙasarmu na garkuwa da mutane.

Sam baabu imani wurin kidifawa,
In sunka sata wasu waya suka yowa,
Kuɗi miliyya su ce abin fansowa,
Allah tsare mu kaidinsu mun roƙawa,
Su al'umar da ke garkuwa da mutane.

Wasu cikinmu in sun yi garkuwa das su,
Nau'i da nau'i azaba suke gunsu,
Duka da yunwa su gaggalabaita su,
Har izgilanci kidifawa ke yi gunsu,
Sharri gare su 'yan garkuwa da mutane.

Daji su ɗaure ruwa ya ƙare kansu,
Sanyi na hunturu a kai na wasunsu,
Can daga baya za su kira ikhwansu,
Kuɗi a kawo koko su hallaka su,
Wayyo ni wayyo wai gwamnatin jama'a ne!

Kare suke ci ba babbaka yankinmu,
Abin takaici wai shugaba kuma ɗanmu,
Mun raina himmar da ake wurin kare mu,
Wai sulhu za ai da masu kakkashe mu!
Anya hukuma aikinta kare mutane?

Abin takaici ne ƙwarai kui duba,
Wai a hakan ne ake faɗin ci gaba,
Ƙalubale ne gare mu wannan babba,
Dukkan musifa yaye mana Wahhaba,
Duk kar ka ware har garkuwa da mutane.

Ni sha'írin nan 'yar shawarata ga ta,
Wurin hukuma ni ma gudummuwata,
Tsayin daka ku yi don kare al'ummata,
Jami'an tsaronmu ciki da maha'inta,
Ku sanya lura cikinsu kun gaggane.

Bora da mowa kul kar ku wawware su,
In kun ka gano tabbas ku hukunta su,
Wurin hukuncin kul kar ku bambanta su,
'Yar shawarata ƙin garkuwa da mutane.

A sa idanu sosai ga infomansu,
Jami'an tsaro na sirri a alkinta su,
Dama cikakka a ba su sui aikinsu,
'Yan sanda soji a ba su duk ƙarfinsu,
Don daƙilewar 'yan garkuwa da mutane.

Mu 'yan ƙasa kau gare mu shawarata,
Aikin alkhairi mu yi mu nuna a yi ta,
Har addu'o'i mu rinƙa yi gun bauta,
Kamun ƙafa na duk matsalar Allah kyauta,
Babbar musifa ta garkuwa da mutane.

Ko ƙyas bayani in mun ji kar mu rufe ta,
Mu kai rahoto ga jami'ai su bahasta,
In mun yi wannan Allahu za ya tsayatta,
Allahu amsa duk matsalar ga ta kwanta,
Babbar musifa da ta damu dukka mutane.

Ashirin da biyu "Two thousand eighteen" yin ta,
A shekarar da "Musabbabi" ma nai ta,
Wata na Maris don ba ni son in manta,
A tsakkiyar da muke cikin firgitta,
Birni da ƙauye yin garkuwa da mutane.

Ni wanda nai ta Abdulhamid Malumma,
Abba ga Hafsat ni ne Uban Fatimma,
Jihar Katsina birninmu mai alfarma,
Garin Matazu a nan kuma nake zamma,
Allah taƙaita a daina kama Mutane.

ALHAMDULILLAH

Post a Comment

0 Comments