Sau ɗaya na taɓa ganin namijin da ko zaman gidan ba ya yuwuwa masa a
dalilin matar. Mabuƙaciya ce ta inna-naha, kuma ba ruwanta da dare ko safe. Da ma yaranta suna
da iyaka a gidan. Sam ba ta bari su kusanci turakar mahaifin...
Zan Qara Aure // 22: Idan ta yi Maka Kaɗan
Baban Manar Alƙasim
Zauren
Markazus Sunnah
Yadda
Allah SW ya halicce mu da sifofi daban-daban, ya karkasa buƙatumu ya ba wa kowa nasa, haka ma lafiyar jiki kowa da
irin tasa, gwargwadon ƙarfin halin mutum da himmarsa ke sanyawa ya ƙara aure, wani ya yi biyu wani uku, amma ba wai don ya
sami abin duniya ba, domin in wadata ce ke sanya mutum ya ƙara ba shakka masu kuɗi ne ya kamata su fi kowa tara yawan mata, abin mamaki
sun fi kowa auren mata guda-guda, idan ka bincika da kyau za ka taras cewa
tabbas ba su da buƙatar ƙarin auren ne.
Shi
kuwa mutumin karkara yana motsa jiki, ko ba aikin gona ba na sana'a zai taka a ƙafa zuwa duk inda yake so, sannan komai zai ci za ka
taras abince ne nagartacce mai ƙara kuzari da lafiya, ga shi yana motsa jiki koda wani
lokaci, bai yawan ta'amuli da abincin gwangwani wanda aka cika shi da sinadarai
barkatai, dole ne in ya ci ya ƙoshi ya buƙaci shimfidarsa, ba
kamar mutanen maraya da sanyin AC, firinji ko zaƙi ya yi musu illa ba,
kar ka yi mamaki in ba su buƙaci ƙarin aure ba.
A
daidai wannan gabar muna ƙoƙari ne mu nuna cewa buƙatar namiji da shimfida
babban dalili ne da zai sa ya buƙaci ƙarin aure, wani mata biyu wani fiye, ina da masaniya da
wasu abubuwa guda uku waɗanda dukansu a kusa da ni suka faru, kai da jin
labarurrukan ka san zama da mace dayan akwai matsala, na farko a kotun ƙauyenmu na tsinci labarin, sannan ina ƙarami ban gane sahihin abinda ya faru ba sai da na girma.
Wato
mace ce ta kawo mijinta ƙara kotu kan cewa yana zaga ta fiye da goma a kowace
rana, ita kuma a dabi'arta ba za ta iya daukar hakan ba, alƙali ya shigo tsakiya yana rarrashi da ban-baki kamar
yadda mijin ya nema, a zama na uku aka yanke
hukuncin cewa zai riƙa zagawa sau shida ne kacal a rana, mijin na ta roƙo har yana kuka a ƙara ya kai 8, ka ji abu
kamar wasan kwaikwayo, aka ce ya ƙara aure, ya ce ba macen
da za ta zauna da shi, gaskiya kusan hakan ne in dai ba ya yi dace da irinsa ne
ba.
Na biyu
kuma a Sudan ya faru, da yake wasu ƙasashen na Larabawa ko
don kaciyar da ake wa mata ne da suke rede mata gabanta yadda ba za su buƙaci namiji ba oho.
Bisa
nazari da wahala auren mutum biyu ya yi ƙarko, wato mai nacewa
shimfida kowani lokaci da wanda bai iya ba wa shimfidar haƙƙinta, wanda duk mace ɗaya ta yi masa ƙaranci, to auren mata 4
babban riga-kafi ne na samun zama lafiya, duk ƙamari dai matansa ne,
sannan in ya kwana biyu a gida ɗaya sai ya kwana 6 kafin ya sake dawowa, ka ga ƙila a daidaita, su kansu matan in suka ga ba dama da
kansu za su nemi ya koma wani gidan.
Sau ɗaya na taɓa ganin namijin da ko
zaman gidan ba ya yuwuwa masa a dalilin matar. Mabuƙaciya ce ta inna-naha, kuma ba ruwanta da dare ko safe. Da
ma yaranta suna da iyaka a gidan. Sam ba ta bari su kusanci turakar mahaifin. A
irin wannan hali shi ma dole ya ƙara aure don ya sami
wurin hutawa, bai yuwawa a ce kai da gidanka amma zamansa ya gagare ka, in ya
ce zai ƙara aure tabbas zai yi fama da uwargidar amma ba wata
mafita in ba hakan ba.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.