In dai ka raba su kowa da gidanta, wannan ba ta san
abinda wancan take ciki ba, to ka huta...
Zan Ƙara Aure // 15: Ta Ishe Ni
Baban Manar Alƙasim
Zauren
Markazus Sunnah
Da yawa mata na da rauni a wannan bangaren, koda yake ba
dukansu ba ne, na ji wace aka ce ta taimaki maigidanta wajen ƙara aure, na ga wace ta kawo wa maigidan zanƙaleliyar mata ta ce ya aura, na ga wace ta rabu da mijin
a kan ya ce zai ƙara aure, na ga wace ta kashe kanta a dalilin ƙara auren, wata mijin ta kashe saboda ya ce zai ƙara wata matar, na ga hoton wace ta hallaka shi gaba ɗaya duk dai a dalilin ya
ce zai yi aure, babu wanda ba ya faruwa, mata kala-kala ne kamar yadda muke daban-daban,
sai dai wasu sun fi wasu.
Akwai matan da ba sa son kishiya ko misƙala zarratin amma kuma sam ba sa kyautata wa mijin. Wallahi
na ga wanda gidansa ke gagararsa zama saboda tsabar fitina, dole sai dai ya
komo waje ya zauna, duk ya yi firgigi ya lalace a dalilinta, da bakinsa na ji
yana cewa in ya bar gidan hankalinsa a kwance amma da ya dawo da fargaba zai
shiga gidan, abin mamaki wallahi ya haife ta, ka ga da girma ne ƙarfi, da damisa ba ta kar raƙumin dawa ba, amma ba anan take ba, wai an danne bodari a
ka.
Wani sa'in namiji yana da buƙatar kwanciyar hankali, kuma inda zai iya samu kenan a
gidansa, da ya dawo ga murmushi fuskannan na annuri kamar wata a daren 15, ƙanshi ko ta ko'ina, sai dai ya ci abinci mai rai da motsi
ya kwanta, in ba yara a gidan ma ya bi tsawon shinfidarsa a ƙarshe ya yi barci har da munshari, to in ya zama cewa
masifar daga gida take tashi, kenan babu inda mutum zai sa kansa, rana zafi
inuwa ƙuna, in yana da dan abin hannunsa sai ya nemi magani
kafin a tura masa hawan jini yana da dan sauran ƙuruciyarsa.
Ba wani abu ne maganin ba kamar ya sami wani gidan inda
zai riƙa fakewa ana mantar da shi duniya da abinda ke cikinta,
wanda ya yi niyyar ƙara aure a bisa wannan dalilin, kuma ya haɗa amaryar da
masifaffiyar matarsa to fa ya yi kisar macijin mata ne, an kashe ba a sare kan
ba, don wuri guda dai zai komo, yana gidan ko ba shi bala'in dai yananan, amma
in ya raba su, to zai sami kwana biyu cikin kwanciyar hankali da kyakkyawar
natsuwa, wani abinda bai taɓa gani ba na ladabi da biyayya da sanin ƙimarsa da daraja duk zai gani.
Duk bala'in mace da ka ƙara aure za ka ji ta
fara saukowa "Wai don Allah me nake ma?" Gaya mata ko ba ta bari duka
ba za ta rage, abincinka zai gyaru, dadinsa zai dawo, cefanenka zai ragu, za ka
riƙa cin abinci a kan kari, ƙananan ayyuka duk za a
yi ma, har bashi sai a ba ka. Zancen shimfida ba daga ƙafa ba gajiya. Yanzu kusan komai kana da damar da za ka
sa a yi ko ka hana. Hatta 'yan uwanka za su sami sassauci ba kamar da ba. In dai
ka raba su kowa da gidanta, wannan ba ta san abinda wancan take ciki ba, to ka
huta.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.