A zuciyata na ce "Bari na yi alwala na yi salla
raka'a 2 don gode wa Allah. Lokacin da na idar sai na ga ashe tare muka yi da
ita. Yayin da 'yan uwa da abokai suka watse sai na matsa kusa da ita na miƙa hannuna. Sai ta ce "Dakata Abu-Umayya."
Kundin Ma'aurata // 19: Ki Buɗe Idanunki
Baban
Manar Alƙasim
Duk girmanki da wayewarki ƙila wanda yake nemanki
ya fi ki, don mai son abinka ya fika dabara, haka muke cewa da Hausa, a cikin
shika-shikan ƙauna akwai fadi da baki, da nuna wa a aikace bayan
tabbatuwa a zuciya, tausayi dake cakude da soyayya shi yake bayyana irin yadda
kake son masoyinka, komai naka nasa ne sai in bai nuna yana so ba, wani lokaci
ma ba sai ya furta ba, in dai ka ga kamar yana so za ka iya ba shi, koda kuwa
hakan zai iya baƙanta maka rai a nan gaba, galibimmu maza mun san wannan,
mata ne dai ba su cika ganewa ba, wasu lokutan sai an kwashi ƙafafunsu suke fadaka, misali: Wata mata ta sami wani
malami take cewa "Tsakani da Allah ni ba mazinaciya ba ce, amma maigidan
da na aura tun shekara 16 da suka wuce wani abu ya faru kafin ɗaura aure"
Malamin ya tambaye ta "Kamar ya?" Ta ce
"Ana sauran 'yan kwanaki kadan a ɗaura mana aure shedan ya dan yaudare mu, gaskiya malam
mun san juna kafin aure, to ni abin yana min ciwo tsawon wannan shekarun, tunda
ba mu yi istibra'i ba shin auremmu ya dauru ko ya?" A lokacin da ka ji ana
cewa saura 'yan kwanaki a ɗaura aure shedan kan yi aiki da wannan damar don ganin ya
cimma burinsa, ke amarya ki shiga taitayinki, sha'awa wani lokacin ba ta da
linzami, ki guji duk abin da zai sa ki ki kebe da saurayinki nesa da idanun
jama'a, bar ganin kina da wayau ko wayewa, namiji da wayewarki zai yi amfani ya
cimma burinsa.
Batun ki zo dakinsa ko ku hadu a hotel wurin tattauna
kaza da kaza bai taso ba, ke tasa ce tun daga ranar da aka ɗaura aure, tunda an kusa
ya yi haƙuri kawai, kina ƙoƙari ne ki tafi masa a tsarkakkiyar uwa, don haka ya ba ki
wannan damar, duk wani ban baki da taushe murya kar ki yarda da ita, zancen
cewa ya kai sadaki gidanku don haka kin halasta masa maganar banza ce, in haka
ne kuwa to meye amfanin ɗaura auren matuƙar kai sadaki ya gama
komai, mace ba ta halasta sai ta gama cika duk rukuna ɗaura aure, kamar waliyi,
shedu sadaki da sigar ɗaura auren, tunda ba a yi wannan ba to ki bari sai an yi
tukun, namiji in yana buƙatar abu a wurin mace marairaice mata zai yi, da haka
wasu 'yammatan suke zuwa dakunansu da ciki, bayan shekaru abin ya yi ta yi musu
ciwo.
A Fahimtata
Walima akan yi ta ne don koyi da sunnan ma'aiki kuma
mutun ya nuna jin dadinsa da gode wa Allah bisa wannan abin arziƙi da ya samu, sai dai shari'a ba ta bar ta haka kara zube
ba, ta gindaya wasu sharuddai da dokoki wadanda za a bi, bai dace ba Allah ya
yi maka arziƙi a maimakon ka gode masa wajen bauta masa, sai kuma ka
juya ka saba masa kuma a daidai wannan lokacin kana neman ya yi maka albarka,
ba a roƙon Allah SW da zunubi, ko walimar an ce ka kira mutanen
kirki, ba ka rubuta a invitation kowani irin mutum ya zo ba, sannan an yi
bayanin irin abincin da ya kamata ka bayar da wadanda suka dace ka tuntube su.
Hada 'yammata da samari ana kida ana rawa gami da wasu
nau'o'i daban-daban na sabon Allah kamar shigar tsaraici da matan keyi,
gwamatsuwa da maza har zuwa alfahasha a ƙarshe, wannan yana nuna
yadda yadda kake so zuriyar ta kasance kenan a gaba, mutumin da ya yi walima
bisa koyarwar Annabi SAW yana ladar kwatanta sunna, yana kuma da ladar ciyarwa,
sannan in wani ya yi sha'awar yadda ka yi shi ma ya dauka daga wurinka ka nuna
masa alkhairi kenan kai ma kana da ladarsa, to bare kuma za ka ji mutane suna
ta zabga maka addu'o'i kamar yadda aka koyar, wasu har tsohonka sai ya sami
kasonsa, masamman in walimar ta amsa sunanta, in ba ka da halin kiran mutum 70
ko mutum 7 ka kira ka yalwata musu ya fi.
Bayan Aure
Na tsinci wani labari a littafin "Az-Zauj
Al-Mithaaliy" na Dr Ridal Nasriy p9-10, inda ya kawo cewa: wata rana Alƙali Shuraih ya sadu da Sha'abi, sai Sha'abin ya tambaye
shi lamarin gida, sai Shuraih yake cewa "Shekara 20 kenan iyalina ba su
taba yi min abin da ya baƙanta min rai ba" Sha'abiy ya ce "Kamar
ya?" Shuraih ya ce "Ranar farko da na shiga dakin amarya na ga wani
kyawun dake fisgar hankali wanda ba ko yaushe ake samun irinsa ba.
A zuciyata na ce "Bari na yi alwala na yi salla
raka'a 2 don gode wa Allah. Lokacin da na idar sai na ga ashe tare muka yi da
ita. Yayin da 'yan uwa da abokai suka watse sai na matsa kusa da ita na miƙa hannuna. Sai ta ce "Dakata Abu-Umayya." Ta yi
hamdala da salati ta ce bayan haka. "Ni baƙuwa ce a gidanka. Ban san
dabi'unka ba. Don haka karanto min abin da kake so don na riƙa yi maka, wanda ba ka so kuma na guje shi".
Ta ce "In a danginku akwai wace da ka so ka aura to
ni ma haka ne, amma abin da Allah SW ya so shi zai faru, yanzu dai ni mulkinka
ce ka yi abin da Allah SW ya amince maka, daganan ko dai ka riƙe ni da kyau ko ka rabu da ni cikin dadin rai, a wannan
maganar nake nema mana gafarar Allah gaba daya" Shuraih ya ce
"Sha'abi, sannan ne nima na yi yunƙurin yin tawa hudubar,
na yi hamdala da salatin Annabi SAW, na ce " Kin yi wata babbar magana
wace in kika tsaya a kai to kin yi sa'a, in kuma kika canja to za ta zamemin
hujja a kanki, ina son kaza da kaza da kaza, in kin ga wani abu mai kyau ki
bayyana a gani, mummuna kuma ki boye"
Ta ce "To ya maganar zuwa gaida 'yan uwana?" Na
ce "Ban son surukaina su ƙosa da ni" ta ce "Maƙwabta fa, wa kake so ya shiga gidanka waye ba ka
so?" Na ce "Gidan su wane mutanen kirki ne, su wane kuwa mutanen
banza ne, daganan ne na sami kanta, shekararmu 20 ban taba ganin abin da zai baƙanta min rai ba sai sau daya, shi ma din ni ne na dauki
alhakinta" namji in ya shiga dakin amarya wata muguwar sha'awa take
lullube shi, ita matar ta sa hankali ta nuna masa abin da ya dace.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.