Sai
na kasa gane me mata suka fahimta game da aure? Masamman ma Hausa/Fulani, shi
ya sa wasu ƙabilun
ba sa yarda su auri Bahaushe saboda yawan saki.
Su kuma mazan suna cewa "In kana son ka ga ladabi da iya
riƙe
miji ka auri ƙabila!"
A ina matsalar take? Fulani kuma ka zagaya kotunammu duk su ne, sun je rigimar
aure. Waɗannan...
Kundin
Ma'aurata - 20: Matsayin Maigidanki
Baban Manar Alƙasim
Zauren
Markazus Sunnah
Da
yake ba ni da ilimin hadisi wanda zan iya tantance ingatacce da mai rauni sai
na taƙarƙare a hadisan da Nasiruddeen
Al-Albaniy kawai ya fitar a As-Saheeh Al-Jami', na san ba ni ba ko mai karatu
zai sami natsuwa saboda sanin wannan malamin da kuma ƙoƙarinsa a wannan fanni, ya
kawo hadisai masu dama da suka yi magana kan matsayin maigida, akwai wanda
Annabi SAW yake cewa "Ki duba matsayinki a wurinsa, don kuwa shi ne aljannarki
da wutarki" As-Saheeh Al-Jami' 1509, wannan yana nuna matsayin maigida ne
a wurin mace, kai ma malam ka zabo wace kake ganin za ta karanta wannan ko in
ka karanta mata za ta fahimta, kar ka bi hasken fata ko ƙarancin shekaru ko wayewa
irin ta zamani, da yawammu anan muke yin kuskure.
.
Wata
rana matar wani malamina ta zo ta same ni wai gardama suke yi, maigidanta ya ce
mata: In ya nemi ya sadu da ita ta ƙi
mala'iku za su yi ta tsine mata har ta wayi gari, ta ce "Na san ƙarya yake, buƙatarsa kawai yake so ya
biya, na gaya wa ƙawata
amma ta ce da gaske ne wai mu zo mu tambaye ka" na yi kasaƙe ina tunani, in har za ta ƙaryata malamina ta ina ni za
ta gasgata ni? To amma a ƙarshe
ta yarda din, sai nake cewa a zuciyata "Da mai ilimi ce sai dai ya bude
mata wurin ta karanta" gaskiya ban ga laifinta ba, don in bai auro ta ba
ba za ta rufe kanta ta zo a matsayin iyalinsa ba, wannan matar malam kenan ina
ga sauran matan da ba ruwansu da karatun addini, ba su ma san haƙƙoƙin mazan a kansu ba?
.
Abin
fa da Annabi SAW yake cewa "Da zan iya sa wani ya yi wa wanin Allah
sujada, da na ce wa mace ta yi wa mijinta, na rantse da wanda ran Muhammad yake
hannunsa, mace ba za ta iya ba da haƙƙin
Ubangijinta ba sai ta ba da na maigidanta, da zai neme ta lokacin tana kan
gwiwa ba za ta hana shi ba" As-Silsilatus Saheeha 1203, wannan isa matuƙa kenan wajen kwatance, Al-Ƙatb a Larabce dan surdi ne da
matan Larabawa suke hawa in za su haihu, shi ne ya kwatanta da haka, kamar dai
mu muce wance tana kan gwiwa, wannan fa maganar Annabi SAW ce, in ba mai addini
ba wa za ta kiyaye maka buƙatunka?
Shi ya sa Annabi SAW ya ba ka shawarar ka neme ta.
.
Da
yawa matan yanzu ji suke yi kamar komai suka yi maka kyautatawa ce kawai amma
ba dole ba ne, ba sa ji a jikinsu, na ji wata tana yi wa maigidanta wanki da
guda sai daya a cikinsu ta ce "Allah ya kiyaye! Ai wallahi ko nawa ba da
hannuna zan wanke ba bare na wani ƙato,
uwayena ba su kawo ni don na yi wa wani bauta ba, mu a gidammu ko wanke-wanke
ba ma yi bare wata uwar wai wankin kayan miji!" A lokacin wata mai fatawa
a cikinsu ta ce "An ce fa hatta dafa abincinnan ba dole ba ne, taimakonsu
kawai muke yi" abin mamaki duk sun san wannan hadisin ni ne kawai ban taba
ji ba.
.
A
ko yaushe mutum zai yi aure ya riƙa
duba sashe da sashe, misali in mace ta zama kamar wancan ta saman ina za ka sa
rai da cewa za ta ziyarci mahaifiyarka har ta taya ta wani aiki kamar wankin
kayan ko dafa abinci? Na taba koyarwa a wata makaranta ta Ingila dake nan Sudan
mai suna "City & Gilts" sai na sanya wa daliban darasi a ranar
Lahadi, nan ne wata cikinsu take cewa "Gaskiya duk Lahadi nakan wuni a
gidan surukata ne, ni nake yi mata duk aikace-aijacen ranar da ma wankin
suturunta na makon, don haka ba zan sami damar zuwa ba" a kanta na canja
ranar saboda matsayin uwar miji da ta ba shi mahimmanci.
.
In
kai kanka a matsayin maigidan ba a kula da matsalolinka ba ya kake tsammanin
mahaifiyarka? Wallahi ina karantarwa a gida Nigeria na ce a kawo cikakkun
jumloli, wata da ta zo ba da nata misalin sai ta ce "Uwar mijina ta rasu!"
Na dan gigita, amma sai na shanye na tambaye ta "Da gaske ne?" Sai ta
ce "A'a misali ne ta ba ni" zan zo magana kan wannan gabar amma mu ma
in za mu yi aure ya dace mu tantance wace ta dace mu zauna da ita, mace mai ƙyuya zai yi wahala ka same
ta ta iya soyayya, don abin ba a baki kawai yake ba, in ba a aikata ba na bakin
ba zai yi amfani ba, ta ya daga ganin mace ka ce ka mutu mata?
.
A
kan haƙƙin
maigida Annabi SAW ya ce "Bai halasta mutum ya yi wa wani sujada ba, da ya
halasta da na ce wa mace ta yi wa mijinta don girman haƙƙinsa a wuyarta, na rantse da
wanda raina yake hannunsa, da a ce daga ƙafarsa har madugarsa gyambo
ne mai fitar da ruwa mai wari, ta zo tana lashe shi da harshenta ba ta gama
biyansa haƙƙoƙinsa ba" As-Saheeh
Al-Jami' 7725, ni wallahi na ga wace ta auri namiji don ta yi jinyarsa, na ga
wadanda suka rabu da mazan don ba su da lafiya, ba wai rashin lafiya na jima'i
ba rashin lafiyar jiki, na ga wace tana gidan amma ba abin da ya hada ta da
maigidan wai ba shi da lafiya.
.
Sai
na kasa gane me mata suka fahimta game da aure? Masamman ma Hausa/Fulani, shi
ya sa wasu ƙabilun
ba sa yarda su auri Bahaushe saboda yawan saki.
Su kuma mazan suna cewa "In kana son ka ga ladabi da iya
riƙe
miji ka auri ƙabila!"
A ina matsalar take? Fulani kuma ka zagaya kotunammu duk su ne, sun je rigimar
aure. Waɗannan
abubuwa ne da muka san su, tsakanimmu da matammu kowa sukar juna yake, don me
ba za mu gyara ba? Mu rage karanta babobin saki mu koma na zamantakewa, na ga
mata wadanda ake ce musu malamai, abin da suke yi da mazajensu da kiyoshinsu ko
kare aka ba shi ba zai ci ba, mu ma ɗin
ga matannan kullum kuka, anya ba a wurin zabi ake samun kuskure ba kuwa?
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.