Shi
ya sa abokan aikinta suke girmamata suna kiranta da malama. Ban san yadda suka haɗu da malamin ba amma dai
soyayya ta bayyana a tsakaninsu, kuma kowa ya ji daɗin wannan aure. Abin da zai ba ka mamaki
malamin bai yarda ta...
Kundin
Ma'aurata - 16: Neman Kusanci a Fahimta
Baban Manar Alƙasim
Zauren
Markazus Sunnah
Daya
daga cikin abubuwan da muke fama da su a yau tsakaninmmu da abokan zamammu har
da kuskuren da muke yi a wurin zabe, domin za ka sami mutum wayayye dan boko
mazaunin birni, in ya ƙyalla
ido ya hango wata bafulatanar riga, jar fata, sai ya sha alwashin ko nawa zai
kashe sai ya aure ta, zai kashe ɗin ya
kuma auro tan, amma ba dole ne a sami komai daidai ba, don shi ya yi Kudu ne
ita ta yi Arewa, duk abubuwan da yake so a yi masa ba ta san su ba bare ta sa
himmar yi masa, zai yi mata bayanin ga yadda za ta yi a rana guda, ita kuma
wayewa karatun shekaru ce da take shiga a hankali, in ba ta yi masa abin da
yake so ba sai ya kama fada, yau da kullum sai ta fara maida masa, in ba a yi
sa'a ba sai lamarin ya ƙi
ƙarko.
Wata
da aka auro ta ba shakka an kashe kudi a kanta, koda yake tun farko an canfe su
da cewa ba sa zaman aure, amma abin da na karanta a kanta, mutumin yana da mata
tun asali, zancen iya kwalliya, tsafta, gyaran kai kamar tsuke da sauransu suna
da alaƙa
da wayewa, kuma sirri ne na mace, ba kowace mace ce za ta tsaya tana yi wa
kishiyarta bayanin cewa ga abin da maigidansu yake so don haka ta yi masa ba,
balle uwa uba sirrin dafa abinci da abin-ci, abubuwan suna da yawa, don in ka
tabo bangaren tsafta dama makaranta ce guda mai zaman kanta.
Wato
dai duk abubuwan da mutumin yake buƙata
ba ta iya yi masa, a ƙarshe
ya fara yi mata fada yana cewa ta sa ido mana ta riƙa kallon abokiyar zamanta,
su mata wannan ƙasƙanci ne da raini, sannan
sirrorinsu in ba su suka fada ba ba idon da zai iya kallo maka, a ƙarshe dai ya saki amaryar
tasa bayan ta haifa masa yaro kyakkyawa, ban san me ya sa ba, don kyawun da ya
aure ta don shi har yanzu akwai shi.
Dayan
kuwa malami ne, da yake sauka gidan wani mai hali a duk lokacin da ya zo wa'azi
garin, matar Alhajin tana da wata ƙanwa
da ta yi karatun digirinta na farko a dayan jami'o'immu, kuma ma'aikaciyar
asibiti ce, ƙira
ta halitta gami da jin dadin rayuwa duk sun bayyana mata, takan yi kwanaki tana
aikin dare kafin ta komo na rana, ba ta cika tsoron maza ba don tun tana
nursery school tare da maza ta yi har jami'a, yanzu kuma yanayin aikin nata dai
tana tare da mazan ne, har ma a wurin aiki, akwana tare a tashi tare, sai dai
duk da wannan mace ce mai kamun kai da son ibada.
Shi
ya sa abokan aikinta suke girmamata suna kiranta da malama. Ban san yadda suka haɗu da malamin ba amma dai
soyayya ta bayyana a tsakaninsu, kuma kowa ya ji daɗin wannan aure. Abin da zai ba ka mamaki
malamin bai yarda ta ci gaba da aikinta ba matuƙar tana matarsa saboda abin
da ya kira da zubewar ƙimarsa,
ya yi mata alƙawarin
daukar duk nauyinta, ita kuma ta yarda, saboda ƙaunarsa tana zucuyarta,
masamman kwadayin abin da ta gani tare da shi na ilimi, shuhura da tsoron
Allah, abin da take sha'awa kenan a rayuwarta.
Bayan
aure da wasu yara ƙanana
da ta samu rigingimun dake tsakaninsu tun da jimawa suka fara ƙamari, domin shi ba mai
zaman gida ba ne, yakan hada wata ba shi a gari, ga kuma matansa a garuruwa
daban-daban, ga wa'azuzzuka wasu har a jahohi masu nisa, bai da lokacin zama da
iyalin bare su yi maganar karatu ko wasu abubuwan, yanayin wayewarta da
karatunta ko kusa ba su yi kusa da halin da ta sami kanta a ciki ba, a ƙarshe duk ƙoƙarin da uwayen suka yi na
ganin an zauna lafiya bai yuwu ba, dole aka haƙure wa juna.
Na
ce: Da a ce ya kalli rayuwarta tun farko da yadda ta taso koda za a sami
matsala za ta zo da dan sauƙi,
ita ma za ta shiga fagen nasa ne na yi wa mata wa'azi, da halartar tarurrukan
imani na mata, ga makarantun islamiyu ga na gwamnati da suke da alaƙa da abin da ta karanta waɗannan
ma kawai sun ishe ta, rashin duba wannandin ya sa auren ya ƙi dorewa, ta yi ta zarginsa
da rashin ba ta haƙƙinta,
abubuwan ma da bai dace wani ya sani ba duk ta fada saboda bacin rai, aure dai
ya lalace, ma'auratan kuma duk ransu a bace, shi maigidan yana jinjina wa irin
kyautatawar da yake wa matar amma sam ba ta ni, ita kuma ta lissafo abubuwa da
dama da irin rayuwarta da aikinta da ƙawayenta
da duk ta rabu da su a dalilinsa amma kullum cikin baƙin ciki, abin dai ba dadi
wai mahaukaci ya ci kashi.
Ita
kuwa wannan baiwar Allan kowa yana yaba mata kamunkai da shigar mutunci, ga ta
da hardar Ƙur'ani,
ta gama sakandarenta kenan tana burin shiga jami'a, ita ma ta ce pharmacy take
son ta karanta, fara ce ƙal
amma ba kowa ya sani ba don ba inda ake kallo a jikinta, ban sami cikakken
bayanin yadda ta hadu da mijinta ba bare yadda aka yi auren, amma kullum cikin
fada suke, ta nemi ya sake ta ya ƙi,
tana zarginsa da yin sakaci da addini shi kuma yana cewa tana yi masa wasa da
gida, sannan bai yarda da koyarwar da take son yi ba, kuma ba ita za ta tsara
masa rayuwarsa ba, a taƙaice
dai babu kusancin fahimta a tsakanin duk waɗannan
ukun, ina ganin shi ne masabbabin samun tasgaro a auren.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.