Akwai
kuma wata Balarabiyar ƙasar
Lebanon inda na ga
hirarta a talabijin ɗin ƙasar ita da wani baƙin fatan ƙasar Ghana. Ita ma ya je karatu ne
ajinsu guda. Ya je bai
iya Larabci irin nasu ba amma yana fus'ha, wato gamagarin Larabci wanda shi ne
karɓaɓɓe a tsakaninsu. Ta ce wannan shi ne babban
dalilin da ya sa...
Kundin
Ma'aurata - 15: Ƙwarya
ta bi Ƙwarya
Baban Manar Alƙasim
Zauren
Markazus Sunnah
Na
jima ina da wannan fahimtar, a gaskiya na gwada sosai kuma na ga amfaninsa, na
sa ido a rayuwar wasu da dama don na yi karatu, kuma na fahimci abubuwa da
dama, sai dai ba ina ƙoƙarin cewa saurayi ya auri
budurwa ko bazawari ya auri bazawara ne ba, sha'awa wace ake mata laƙabi da soyayya ana samunta a
ko'ina, kuma tsakanin kowa, tare da bambancin aƙida ta siyasa ko addini,
hali na dabi'a ko dukiya, mulki na sarauta ko aikin gwamnati, matsayi na wurin aiki ko rayuwa, wayewa ta
ilimi ko ta duniya, bambancin shekaru ta bangaren mace ko namiji da dai
sauransu.
Yawancin
maza in suka mace a ƙaunar
macen ba sa rabewa tsakanin soyayya ta gaskiya da sha'awar kasantuwa da mutum
don dadin bakinsa da salon iya magana, mace a rayuwarta abin da take buƙata kenan a wurin namiji
kamar yadda muka karanta a baya, in ta sami wani namiji ya iya kalamai masu
dadi za ta ƙaunace
shi ba tare da ta duba ko shi waye ba, nazarin ya yi daidai da rayuwarta ko bai
yi ba wannan ba lissafinta ba ne, don in ka tambaye ta "Don me kike ƙaunarsa?" Da wahala ta
iya ba ka katamaiman dalili guda daya, magana ce kawai mai dadi.
Na
taba ganin wata Baturiyar ƙasar
Sweden da ta auri wani baƙi
dan ƙasar
Sudan, ana hira da ita a talabijin ɗin
Sudan din, mai gabatarwar ta tambaye ta "Don me kika aure shi tare da
bambacin rayuwa kika canja addini, yare, ƙasa, abinci, sutura, kika
bar gari mai mugun sanyi kika dawo gari mai mugun zafi?" Na so na ji
bayanin da za ta yi masamman kasancewata mai nazari ta fuskar rayuwar dan adam,
ƙila
na tsinci wani abin da ban sani ba, koda yake in kana neman bankaura ka sami
Bature ka gama.
Da
bude bakinta ta ce ba ta da wani dalili, ta ce "Kawai dai mun yi karatu
tare kuma ajinmu guda, shi mutum ne mai yawan barkwanci da son ba'a, to launin
fatarsa ya fita da na kowa don haka hankulan mutane suna yawan komowa kansa, ni
ban taba sha'awar zama tare da shi ba, amma in ya zo ta wurina nakan tsaya na
saurare shi, da haka dai da yake gidansa yana kusa da namu har muka saba, ni
ban san lokacin da ya shiga raina ba, ban ma sani ba wa ya fara neman wani a
cikimmu, a ƙarshe
dai mun fahimci juna kuma ga ni a Sudan".
Matar
ta iya baro ƙasarta
ta tare da shi a Sudan, ta haifa masa 'ya'ya 6, amma ta ce gidansu ba wace ta
haifi 'ya'ya ƙasa
da 12, kuma ita ma in Allah ya sa za ta haife su a shirye take, ta ba ni
sha'awa masamman yadda na gan ta musulma, kuma na ga ba ta da wata niyya ta
komawa ƙasarta,
a maganarta ma sai ta kwashe shekaru kafin ta je gida, in ta je ɗin
ma dan lokaci kadan sai ta dawo wurin mijinta, wannan kam zama ya yi dadi, sai
dai bambancin launin fata ne, ƙasa,
addini, yanayi, cima, sutura da rayuwa, ban san bambancin hali irin na dukiya
ba, don in dan Sudan zai je karatu ƙasar
Sweden akwai yuwuwar kasancewarsa mai arziƙi, ita kuma a ƙasarta ba dole ba ne,
kasancewar tana zuwa Sweden ta dawo ka ga akwai hali.
Akwai
kuma wata Balarabiyar ƙasar
Lebanon inda na ga
hirarta a talabijin ɗin ƙasar ita da wani baƙin fatan ƙasar Ghana. Ita ma ya je karatu ne
ajinsu guda. Ya je bai
iya Larabci irin nasu ba amma yana fus'ha, wato gamagarin Larabci wanda shi ne
karɓaɓɓe a tsakaninsu. Ta ce wannan shi ne babban
dalilin da ya sa ƙaunarsa
ta kurdada zuciyarta ba tare da ta sani ba, har dai a ƙarshe suka yi aure, koda
yake a iya hirar ba a ambato dadewar da suka yi tare ba, bare a yi maganar ko
takan je Ghana ɗin ko
ba ta zuwa, ba a yi kuma maganar sun sami zuri'a tare ko har yanzu suna nema
ba, sai dai an nuno yadda ta riƙe
shi tamau, sannan maganganunta da motsinta duk suna nuna irin tsabar ƙaunar da take nuna masa.
Shi
ma an nuno cewa ta fara ƙoƙarin koyon harshensa wato
Hausa, shi Bahaushen Ghana ne, kayan jikinsa yana nuna cewa ɗiyan
masu hali ne, koda yake waɗannan
Larabawan mun sani suna da ƙyamar
baƙin
fata, amma in kana da hali ba matsala, za su iya aurenka kuma su zauna da kai a
duk inda kake son ka rayu da su, sai dai dole ka riƙa tunawa cewa tana da 'yan
uwa, kuma ita kamar gona ce dole ka riƙa
ban ruwa daga lokaci zuwa lokaci, in ba haka ba kuwa in wata rana ta je ganin
gida auren ya ƙare
kenan, yaranka ma dole ka haƙura
ka bar mata, ko kuma ku yi ta shari'a, koda yake in za a yi adalci ba dukansu
haka suke ba.
Sai
dai na ga aurarrakin da aka yi tsakanin 'yan Nigeria da fararen buzayen Nijer,
na ji irin koke-koken da aka riƙa
yi wadanda suka so su yi kama da auren diyoyin fulani a yau, haka na zauna da
wadanda suka auri Shuwa, su kam ba wani kuka sama da bambancin zamantakewa ta
wurin me za a ci, kuma ya za a dafa shi, almuhim, wannan ba zai zama hujja a
wurin talaka ya ƙyalla
ido kan ɗiyar masu kudi ya
kafe kuma sai ya aure ta ba, banda auren akwai rayuwa kamar me za a ci? Me za a
sanya a matsayin sutura? Wace iriyar mota za a hau? Wani gida za a zauna? Wa
zai yi hidimar gida da dai sauransu.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.