Abubuwan
da suka bayyana a irin wannan matakan da ake ɗauka su ne ake kira kishi. In dai haka ne to ba dole
ne ya bayyana ga namiji ba. Sau ɗaya
na ga wani mutum da matarsa take koyarwa a wata makarantar firamare wanda suka kwashe
shekaru da dama suna tare, sai dai duk daɗewar nan suna ɗan samun wasu 'yan matsaloli
a tsakaninsu. In kuma
an samu ɗin wani abokin
aikinta ne yake shiga tsakaninsu, domin mijin har...
Kundin
Ma'aurata - 11: Abin da Kowa Yake Gani
Baban Manar Alƙasim
Zauren
Markazus Sunnah
Suna
maganar dalilan dake sanya mace hauka ne a lokacin da kishi ya taso mata, sai
suka ce: Mace kan miƙa
kanta ne kacokan ga namijin da zarar zuciyarta ta natsu da shi, wannan mutumin
shi zai yi jagorancin rayuwarta gaba daya, ta yi hukuncin rayuwa da shi daga
duniya har lahira, sai ya zamo yana da wani matsayi na yarda wanda ko
mahaifinta bai samun irinsa, don akwai maganganun da in ba mijin ba ba za ta taba
yi da wani ba, ita kenan, amma shi namijin da mace ta nuna tana ƙaunarsa kuma bai yi wani
kokwanto ba wurin yarda da ci gaba da soyayya da ita ƙila don ya hango wani abu ne
da ya burge shi wanda ido zai iya gani, shi ya sa in wasu abubuwa daga baya sun
taso zai iya rabuwa da ita cikin sauƙi
ba tare da cutuwar zuciya sosai kamar macen ba, don tun farko bai ba da
zuciyarsa gaba daya ba, gaskiya wannan nazari ne kawai.
Mace
in namiji ya nuna ƙaunarta
takan dan dakata ta lugwigwita maganar tukun na dan wani lokaci, ta sanya
lamarin a cikin mizani ta gani anya wannan ba zai ci amanata ba? Matsalar kuma
ba wasu hanyoyi take da su na gano cewa ba zai ci amanar tata ba sama da
mu'amalarta da shi, wai tanan ne za ta fahimce shi, in ma uwarta ta nemi jin
wasu 'yan abubuwa na sirri a tsakaninsu ba dole ne ta gaya mata ba, saboda tana
ganin cewa wannan abu ne da ya shafi rayuwarta.
To
in aka sami akasi sai ya yi mata mummunan tasiri, ya hana ta kwanciyar hankali,
ta riƙa
ganin kanta tsirara a gaban mutane, ta tuna irin maganganun da aka gaya mata na
ta bi da lura amma ta watsar, sai ta ji cewa a shirye take ta yi komai don
rayuwarta ta riga ta lalace, to namiji a irin wannan matsayin ba kowa ba ne,
duk lafazin da ba ka taba zato ba za ta ambato shi, ba ta damu da abin da zai
biyo baya ba, wadanda za su iya magance lamarin su ne uwayenta, yadda za su
jawo ta a jiki, su dauke hankalinta wajen nuna ƙaunarsu gareta gami da fada
mata maganganu masu dadi, wadanda za su mantar da ita halin da ta shiga.
Sai
dai kuma uwaye ba su cika yin hakan a irin wannan lokacin ba, kodai don barinta
ta dandani abin da ta janyo da hannunta, ko kuma saurarawa har lamarin ya dan
yi sauƙi,
ita kuwa a daidai wannan lokacin za ta fara neman mafita, wata za ta yanke
hukuncin cin mutuncin mijin ne ta kowace hanya, albashi duk abin da zai faru ya
faru, wata kuma sai ta daura kaifukan gaba daya a kan wace za a auro, ta ga
cewa ita ce take nema ta ƙwace
mata jin dadinta don haka sai dai Allah ya raba su, za ta fuskance ta da duk
abin da take da shi.
Abubuwan
da suka bayyana a irin wannan matakan da ake ɗauka su ne ake kira kishi. In dai haka ne to ba dole
ne ya bayyana ga namiji ba. Sau ɗaya
na ga wani mutum da matarsa take koyarwa a wata makarantar firamare wanda suka kwashe
shekaru da dama suna tare, sai dai duk daɗewar nan suna ɗan samun wasu 'yan matsaloli
a tsakaninsu. In kuma
an samu ɗin wani abokin
aikinta ne yake shiga tsakaninsu, domin mijin har makarantar yake biyo ta, da
wannan sai abokin aikin ya zama cikakken alƙalin da su biyun duka suka
yarda da shi, don yakan kebe da kowa ya gaya masa laifinsa, ya kuma ja
hankalinsa, ya gaya masa maganganu masu dadi yadda zai haƙura ya ci gaba da zama da
masoyinsa cikin kwanciyar hankali.
To
bayan wasu shekaru sai zaman ya gagara gaba daya, har dai aka haƙura da auren kowa ya kama
gabansa, amma abin da zai daure kai shi ne, alƙalin da yake shiga tsakani
kuma shi ne ya fito a matsayin manemi, da bincike ya yi nisa an gano cewa
tsohuwar matarsa ce ta nuna ƙaunar
abokin aikin nata a sakamakon irin ban bakin da yake mata, da irin ƙoƙarin da yake yi na ganin sun
zauna lafiya, tanan ne ƙaunarsa
ta kurdada zuciyarta, wancen auren na ƙarewa
kuma ta ga ba wanda ya dace ta zauna da shi in ba abokin aikin ba, shi kuma
tsohon mijin ya maka su a kotu kan cewa bai tarda ba, yana ganin dan
tsakiyannan shi ne ya fitar masa da mata don ya sami damar aure masa ita.
A
ƙarshe
dai ya fadi a gaban alƙali
cewa bai damu ba kowa ya aure ta amma ba wannan dan tsakiyan ba, shi kuwa
abokin aiki tunda ya ga mata fara sal kyakkyawa wace bai taba zaton zai iya
neman irinta ba ta nuna tana son shi sai kawai ya miƙa wuya, a dalilin rashin
samun abin da zai hana shi nemanta, alƙalima
ya tambayi tsohon mijin in shi ne ya rabu da matar ya ce "I", ya sake
tambayarsa in yana da haƙƙin
sai ya yarda da mutum kafin tsohuwar matar tasa ta aure shi, ya ce
"A'a" daganan aka watsar da ƙarar
saboda rashin hujjar yinta.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.