Za ka sami wanda zai tausaya wa yarinya da irin halin
da take ciki, kamar talauci ko canjin addini da sauransu, sai ya fara nemanta
ba tare da ya yi shawara da uwayensa ko abokai ba, kawai sai ta kware masa sai
ya ba da haƙuri ya yi tafiyarsa.
Zan Ƙara Aure // 09:
Ka Yaudare Ta
Baban Manar Alƙasim
Zauren Markazus Sunnah
Da za ka bi shawarata ba za ka taɓayunƙurin ƙara aure
ba sai ka tabbatar da cewa ba gudu ba ja da baya, tunda ka fara ba abinda zai
sa ka janye wannan yunƙuri, in ka yi haka ka yi daidai, zan ba da misali, wani
mutum ne ya fara neman aure gadan-gadan, sai matansa suka miƙe tsaye, ta inda
suka shiga ba tanan suke fita ba, suka sami abokansa suka marairaice musu gami
da rantsuwar cewa ba za su sake bijire masa ba, da ya ji haka sai ya janye ƙudurinsa,
tunda sun yi ladabi.
To ita wancan da ka fara nema ta riga ta gaya wa uwa
da 'yan uwa cewar kana nemanta, meye laifinta da ka dena? In ka karbi hanzarin
ta gida ka janye maganar, ita kuma wannan da ka cusa wa ƙaunarka har ta fara
son ka wani abu za ka yi ka saka mata, kudi? An ce ba sa sayen ƙauna, a taƙaice
dai ka cutar da rayuwarta sai dai Allah ya isa, daga ranar kuma ka zama
mayaudari a wurinta da duk makusancinta, wannan a babin misali na ba ka ba shi
kadai ba ne.
Za mu yi bayaninsu a rarrabe amma bari mu kawo su a
dunƙule, wani yakan yi sha'awar ƙarin aure ne idan ya ga wace ya taɓanema ta
baro gidan miji, nan da nan sai ya tuno tsohuwar soyayya ya bi ta, wani
abokansa suke zuga shi, wani damina ce ta yi kyau ya ga yabanya, wani uwayensa
ke matsa masa, wani kwalliyarta ya gani ya yi sha'awa, ko ƙoƙarinta a karatu,
ko kyakkyawar dabi'arta, wani ita matar da kanta take zawarcinsa, wani bai da
dalili kawai cusa kansa ya yi.
To duk irin waɗannan mutum zai kai kansa da zarar ya
ga abu bai kai masa ba sai ka ga ya ja da baya ya ce ba ya yi, wani ma sai dai
matar ta ga ya dauke ƙafa kawai, kwanaki wani malamin makaranta yake ba mu
labarin cewa wani mutum mai ƙima da daraja ya kawo wata yarinya, ya shigar da
ita makarantarsu, makarantar unguwar-zoma ce, ya yi alƙawarin zai dauki nauyinta
har ta gama, nan take ya fara biya, amma bai kammala ba, wani tudu wani kwari
ya sare a kan hanya, lokacin da makaranta ta dan matsa masa ya biya na zango
daya ba wanda ya sake ganinsa.
Ita kanta ta yi mamaki don ko musayar yawu ba su taɓayi
ba, kawai dauke ƙafa ya yi, ko ta buga masa waya ba ya dagawa, ta bi waɗanda
yake shiri da su amma ba wani labari, a ƙarshe ta fara fadin ya yaudare ta, don
kawai haka ta dena ganinsa kamar daukewar wutar lantarki, wani kuma shiga ƙarin
auren ya yi gadan-gadan, soyayya babu kama hannun yaro, mutane na kallo suna
sha'awa, sai da aka zo sa rana sai ya ce a je a yi gwaji, ana gwadawa sai ga
duk suna da AS, wato akwai yuwuwar samun cutar Sikila a yaran da za su samu,
sai ya ce ya haƙura.
Za ka sami wanda zai tausaya wa yarinya da irin halin
da take ciki, kamar talauci ko canjin addini da sauransu, sai ya fara nemanta
ba tare da ya yi shawara da uwayensa ko abokai ba, kawai sai ta kware masa sai
ya ba da haƙuri ya yi tafiyarsa. Gaskiya wannan yaudara ce,
wallahi wata a hannuna ta muslunta saboda wani saurayi da suka dade suna jin
mu'ujizar juna tare, yayin da ya tafi Legas, ta muslunta da zammar in ya dawo
za ta aure shi, gogan naka na dawowa ya tubure wai bai san maganar ba, ya ce
gidansu ba za su yarda ba ko 'ya'yansa da na kishiyar za su riƙa cewa kaza da
kaza.
Akwai wata ma da ta zo wurimmu bayan ta muslunta, ta
ce; mijinta yana da aure na tsawon lokaci amma ba su taɓahaihuwa ba, sai ya
musluntar da ita, ya aure ta, ta haifa masa yara biyu, daganan ya sake ta, ba
tare da lefin a zo a gani ba, dama abinda yake nema kenan yara, kuma ya samu,
ya zai yi da amincewar data yi masa oho, har maganar da muke cikinnan ta kasa
zaman aure saboda irin ƙaunar da take masa, da kuma irin dadin da ta ji a baya,
in ta tuno sai kawai ta fashe da kuka, ta yi auren ta sake fitowa.
Wani kuma ya fara neman auren ne bai tuntubi babansa
ba, lokacin da abu ya yi nisa aka ce ya fito lokacin ne ya sami babansa, shi
kuma baban ya ce bai yarda ba, yaushe ya yi ta farko da zai ce zai ƙara? Ya
bari sai ya yi gidansa na kansa ya sami jari mai ƙarfi in ya so sai ya ci gaba,
haka dai ya sami uwayen yarinya ya yi magana da su, yarinyar kuma sai daina jin
duriyarsa ta yi, a ganinsa ya gama kenan, wani ƙazantar matar ta sa ya fara
neman aure, da aka yi mata fada ta ce ta gyara, shikenan wai an daidaita sai ya
watsar da wancan.
Wani ya yi ƙudurin ne a dalilin matarsa ba ta haihuwa,
Allah cikin ikonsa, shekarar da ya fara neman wata a shekarar ta sami ciki, har
ma sun dan sami hayaniya a tsakaninsu matar ta tafi gidansu shi kuma ya ƙi zuwa
biko, da ya ji bullar maganar cikin shikenan ya watsar da maganar ƙaro aure ya
dawo da matarsa, duk dai maganar da muke yi ita ta biyun da mutum ya dasa mata ƙaunarsa
sannan ya watsar da ita me yake tunanin ya yi, yaudara?
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.