Na taɓazama da 'yan ƙasar Ethiopia, ni ne ma wakilin
angon, ɗan Nigeria ne, ya musluntar da ita ya aure
ta. Soyayya ba kama hannun yaro.
Kullum tana jikinsa. Ba
ta yarda ta yi nesa da shi. Kai
ko titi za a tsallaka ba za ta yarda ya tsallaka ya bar ta ba, sai dai su tafi
tare.
Zan Ƙara Aure // 08: Kafin
Ka Fara Tunanin
Baban Manar Alƙasim
Zauren Markazus Sunnah
Auren fari abu ne mai sauƙi, haka ma in mutum ya rasa
matarsa a dalilin rasuwa ko rabuwa, duka dai zai zauna da mace guda ne, in za
ka iya ba ta haƙƙoƙinta na ci da ciyarwa kamar yadda ake fadi a dunƙule, kuma
ka ba ta sutura da matsuguni shikenan ka gama komai, sabanin a ce akwai wata
matar da za ka ƙaro, galibinmu maza ba mu san wannan ba, gaskiya ga namiji mai
son ƙara aure ba kawai in yana da abincin da zai ba su da sutura da za su saka, da matsuguni shikenan ya gama komai ba.
Dole sai yana da zarafin da zai iya daidaita su a
zauna lafiya, da yawan maza na ƙara aure bayan ba su da ƙudurar da za su iya
daidaita zamantakewar matansu, masamman waɗanda fitinar ta farkon ta sa ya yi tunanin ƙarin auren, rarrabuwar
kan mata kan haifar da rugujewar gida gaba daya, ya bata tarbiyyar yaran, a
sami tabkekiyar baraka tsakanin maigida da 'yan uwansa masamman uwayensa, in ba
a yi dace ba matan duk su shiga bokaye, in har hakan ta faru, to 'ya'yanka sai
a hankali, sai dai a nemi kariyar Allah kawai amma an riga an yi nisa.
Wata rana na ji wasu mata suna hira kan wani gida
yadda maigidan ya kasa riƙe gidansa, nan da nan wata a cikinsu take cewa
"Ragon maza ne wallahi, da a ce maigidammu ne wallahi kulle ƙofar zai yi
ya yi mana dukan tsiya, tabbas da gaske ne, don an taɓacewa ta yi wani abinda
bai so ba ya mare ta, ta zage shi, yana miƙewa ta bazama cikin daki ta leƙo ta
taga tana cewa in ya san ya isa ya shigo ya tabe ta, ta hada da cewa "Ban
yafe ba mugu kawai Allah zai saka min marin da ka yi min, kuma wallahi ba ka
daki banza ba, a jikin yaranka zan rama ai za su dawo makaranta!".
Irin waɗannan matan kamar zuma ce, shanta sai da wuta,
in ya yi lagwas gidan sai ya gagare shi, wallahi akwai matan da suka shafe
shekara 15 ba wace ta taɓataka dakin wata, koda mutuwa aka yi bare haihuwa,
hadin-kan yara kuma kai ka sani, kenan samun abinda za ka ba matan ba shi ne
kadai ba, dole ka tabbatar kana da ƙarfin zuciyar da za ka iya tafiyar da
gidanka, ka zaunar da su lafiya, in babu to ka kalli abinda tashin hankalin zai
haifar.
Na zauna da wasu 'yan ƙasar Somalia in da suke mamakin
yadda mutum yake ƙara aure kuma ya bar sabuwar matar a gari guda, har ya ce ya
ji ana yin haka a Nigeria, na ce tabbas hakan na faruwa na ja bakina, ya ce
wallahi a ƙasarsu sai wata ta kashe wata, abinda ya zo raina mu a Nigeria ai
kusan a daki daya ma zan ce, don wasu matan sukan hadu a ne falo ne, wato
"two bedroom flat" akwai masu madafa daya, ban-daki daya, komai tare
suke yi in ba uwar-daka da kowa ke da nata daban ba.
Na taɓajin wata Bamisriya a BBC Arabic tana hira da Nuruddeen Zurgiy da
jin muryarta za ta kai shekara 48-53, take cewa amaryarta ba ta san ta ba , ba
su taɓahaduwa da juna ba, kuma ba ta fatar Allah ya hada su, da ya tambaye ta
dalili sai ta ce "Gaskiya ni kyakkyawa ce! In muka hadu dole ta ji zafin
hakan a zuciyarta!" Na yi dariya na ce to an gaya mata cewa kishiyar tata
mummuna ce ko tsabar yarda da kai ce? Sannan ya maigidansu zai hada kan
'ya'yansa? Kuma ba a sha'ani a babban gidan ne da ba sa haduwa? Ko ba rashin
lafiya ba a rasuwa ne? Akwai dai abubuwan tambaya da dama.
Na taɓazama da 'yan ƙasar Ethiopia, ni ne ma wakilin
angon, ɗan Nigeria ne, ya musluntar da ita ya aure
ta. Soyayya ba kama hannun yaro.
Kullum tana jikinsa. Ba
ta yarda ta yi nesa da shi. Kai
ko titi za a tsallaka ba za ta yarda ya tsallaka ya bar ta ba, sai dai su tafi
tare. An kai yadda wurin aikinsa ma tare
suke tafiya, malami ne, duk ajin da zai shiga sai dai su shiga tare, irin alaƙar
malami da dalibannan sam ba ta yarda ba kuma ba ta daga masa ƙafa ko kadan, na
raba fada har na gaji, a ƙarshe na yi watsi da su, to kai a jinka ta ina zai
sami sarari bare har ya yi tunanin zai ƙara mata? Ita kadai din ma ya aka ƙare
bare ya auro wata? In dai zai ƙara auren to dole ya yi tunanin yadda za su rayu
tare a ƙasa daya ma ba gari daya ko gida daya ba.
Rauni kan bayyana ƙarara a wurin wasu mazan, wanda kai
da kanka ka san ba su shirya zama da mata biyu ba tsakani da Allah, wata matar
take fadi da kanta cewa "Mu wallahi in shedan ya buga mana tambari
dambacewa muke yi, ko maigidan yananan ba abinda yake iya yi, sai ma ya kulle
mana ƙofa ya yi zamansa, haka za mu kekketa kayanmu, mu tottana wa kawunanmu
asiri wallahi ko ƙala ba ya cewa bare mu sa rai zai shiga tsakanimmu, sai dai
in mun gaji mu bari don kammu" abin takaici suna da yara kuma yaran suna
ganin abinda yake faruwa, su ma babu cikakken hadin kai a tsakaninsu.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.